Ticker

6/recent/ticker-posts

Addu’ar Da Za A Yi Domin Samun Natsuwar Zuciya Da Rashin Bacin Rai

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum warahmatullah bayan gaisuwa irinta addinin Musulunci ina yi wa malam fatan alkhaeri! Malam tambaya na ita ce idan ran mutam yana yawan ɓaci wace addu'a ce zai yi ya ji ransa yabar ɓaci.

ADDU’AR DA ZA A YI DOMIN SAMUN NATSUWAR ZUCIYA DA RASHIN ƁACIN RAI:

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumus salam warahmatullahi wabarakatuhu.

Idan mutum yana yawan jin ɓacin rai, fushi ko damuwa, yana da kyau ya yawaita zikiri da addu'o'in da Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya koyar damu.

Ibn Mas'ud Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Wata damuwa ko baƙin ciki ba sa taɓa samun mutumin da ya karanta wannan addu'ar, face Allah ya tafiyar masa da wannan damuwa da baƙin ciki, kuma ya canja masa da kwaranyewar damuwar:

"اللَّهُمَّ إِنِّي عَبْدُكَ وَابْنُ عَبْدِكَ وَابْنُ أَمَتِكَ ، نَاصِيَتِي بِيَدِكَ ، مَاضٍ فِيَّ حُكْمُكَ ، عَدْلٌ فِيَّ قَضَاؤُكَ ، أَسْأَلُكَ بِكُلِّ اسْمٍ هُوَ لَكَ ، سَمَّيْتَ بِهِ نَفْسَكَ ، أَوْ عَلَّمْتَهُ أَحَدًا مِنْ خَلْقِكَ ، أَوْ أَنْزَلْتَهُ فِي كِتَابِكَ ، أَوْ اسْتَأْثَرْتَ بِهِ فِي عِلْمِ الْغَيْبِ عِنْدَكَ : أَنْ تَجْعَلَ الْقُرْآنَ رَبِيعَ قَلْبِي ، وَنُورَ صَدْرِي ، وَجِلَاءَ حُزْنِي ، وَذَهَابَ هَمِّي ؛ إِلَّا أَذْهَبَ اللَّهُ هَمَّهُ وَحُزْنَهُ ، وَأَبْدَلَهُ مَكَانَهُ فَرَجًا".

"Ya Allah ni bawanka ne, ɗan bawanka, kuma ɗan baiwarka, makwarkwaɗata (maɗigata) a hannunka take, hukuncinka zartacce ne a kaina, kuma ƙaddararka a gare ni mai adalci ne, ina roƙonka da dukkan sunayenka, wanda ka ambaci kanka da shi, ko ka saukar da shi a cikin littafinka, ko ka sanar da shi ga wani daga cikin halittarka, ko ka keɓance kanka da saninsa a cikin ilimin fake (gaibu) da ke wurinka, ka sanya Alƙur'ani ya zama daɗi ga zuciyata, ya zama haske ga ƙirjina, ya zama kwaranyewa ga baƙin cikina, ya zama mai tafiyar da damuwata".

A ƙarshen hadisin an ruwaito cewa Sahabbai sun tambayi Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa; shin ba ma koyi wannan addu'ar ba? Sai ya ce: "Tabbas, ya kamata wanda ya ji addu'ar nan ya koye ta"". Musnadu Ahmad (3712), Sahihu Ibn Hibban (972).

An ruwaito daga Abu Bakrah cewa Manzon Allah (tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi) ya ce addu'ar wanda ya shiga mawuyacin hali ita ce:

ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﺭَﺣْﻤَﺘَﻚَ ﺃَﺭْﺟُﻮ ، ﻓَﻠَﺎ ﺗَﻜِﻠْﻨِﻲ ﺇِﻟَﻰ ﻧَﻔْﺴِﻲ ﻃَﺮْﻓَﺔَ ﻋَﻴْﻦٍ ، ﻭَﺃَﺻْﻠِﺢْ ﻟِﻲﺷَﺄْﻧِﻲ ﻛُﻠَّﻪُ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺃَﻧْﺖ

"Ya Allah! RahamarKa nake fata, kada Ka bar ni da kaina ko da da sakan guda (da idanuwa suka lumshe), kuma Ka gyara mini dukkan lamurana, babu abin bautawa da gaskiya sai Kai." [Abu Dawood (5090), Ahmad (27898)].

An ruwaito daga Ɗan Abbas cewa Manzon Allah (tsira da amincin Alllah su tabbata a garshi) ya kasance yana yin wannan addu'ar alokacinda ya ji kansa a yana yin damuwa:

 ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢُ ﺍﻟْﺤَﻠِﻴﻢُ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭَﺏُّ ﺍﻟْﻌَﺮْﺵِ ﺍﻟْﻌَﻈِﻴﻢِ ، ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻟَّﺎ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭَﺏُّ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﻭَﺍﺕِ ﻭَﺭَﺏُّ ﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ ﻭَﺭَﺏُّ ﺍﻟْﻌَﺮْﺵِ ﺍﻟْﻜَﺮِﻳﻢ

"Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai Girma, Mai Hakuri. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Arshi Mai Girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai da Ubangijin kasa da Ubangijin Arshi mai daraja.

[ Muslim (2730) ].

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya cewa Asma'u bntu Umais R.A: Shin bazan koya maki ba wata addu'a da za ki karantata alokacin damuwa da bakin-ciki, ko lokacin kuncin rayuwa?? Kice:

 ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺭﺑِّﻲ ﻻَ ﺃﺷﺮِﻙُ ﺑِﻪِ ﺷﻴﺌًﺎ

"Allah, Allah shi ne Ubangijina, ban yin taraya yia da shi da kowane abu (ban saɓa masa ko haɗa shi da wani a bauta)."

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa: Adduar zinnun lokacin da ya roki Allah yana cikin kifi:

لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظَّالِمِينَ

"Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai, tsarki ya tabbata a Gare Ka, lalle ne ni na kasance daga cikin masu zaluntar kainu."

«اللَّهُمَّ إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحَزَنِ»

Ya Allah, ina neman tsarinka daga damuwa da baƙin ciki.

Haka kuma idan fushi ya taso, Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya koyar da damu cewa mutum ya ce:

«أَعُوذُ بِاللَّهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ»

"Ina neman tsarin Allah daga Shaiɗan abin jefarwa.”

Ya kuma dace mutum ya yi shiru, ya canza matsayinsa idan yana tsaye ya zauna, ko ya yi alwala. Allah Maɗaukaki Ya ce:

أَلَا بِذِكْرِ اللَّهِ تَطْمَئِنُّ الْقُلُوبُ

 “Ku saurara! Da ambaton Allah zukata suke samun natsuwa.” (Ar-Ra'ad: 28).

To ire-iren wadannan addu'o'in waɗanda suka tabbata daga Annabi (sallalahu alaihi wasallam) sune ake son Musulmi ya lazimci yinsu a duk lokacinda ya tsinci kanshi a cikin wani mawuyacin hali, bakin ciki, masifa ko damuwa.

Saboda haka shawaran dazan baka shi ne ka yawaita istigfari da salati ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam), karatun Alƙur'ani da wannan addu'a, tare da yin haƙuri in sha Allahu duk wani ɓacin rai Allah zai cire maka shi. Allah Ya sanya maka natsuwa a zuciya, Ya kawar maka da dukkan damuwa da baƙin ciki damu baƙi daya.🤲

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam  

Post a Comment

0 Comments