MUƘADDIMA: AURE A ƘUNSHIYAR KARIN MAGANA
Na
Shafa'atu Salihu Labbo
Abu-Ubaida Sani
Da sunan Allah, mai rahama, mai jinƙai, wanda bai haifa ba kuma ba a haife shi ba. Salati da sallam su tabbata ga farin jakada, cikamakon Annabawa, Shugaban Manzanni, Shugabanmu Annabi Muhammadu (S.A.W) da iyalansa da sahabbansa da duk waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
Alal haƙiƙa, na yi matuƙar farin ciki da samun damar yi wa wannan littafi
mai suna Aure a Ƙunshiyar Karin Magana na Malama Shafa’atu Salihu Labbo da Dakta Abu-Ubaida
Sani muƙaddima, duk da cewa ba ni na fi cancanta in yi ba, amma ba ni wannan damar
babban abin jin daɗi ne a
gare ni.
Masu hikimar magana suna cewa, ba don aure ba da iri ya ƙare. Tabbas! Wannan
batu haka yake, domin aure muhimmin abu ne a cikin rayuwar Hausawa,
kasancewarsa hanya ɗaya
tilo da yake samar da tsarkakakkiyar zuri'a wanda kan sanya mutum ya yi
alfahari da dangantakarsa.
Wannan muhimmancin da aure yake da shi a cikin rayuwa ne ya sanya bayanansa
da kusan dukkan wasu al'amura da suka shafe shi suka riƙa bayyana a cikin ƙushiyar
adabin Hausa, musamman ma karin maganar Hausawa.
Karin magana wata falsafa ce ta Hausawa da take dunƙule zance mai faffaɗar magana, wadda ke buƙatar
zurafafa tunani, da faɗaɗa bayani kafin jama'a su fahimci ƙunshiyarta.
Alal haƙiƙa, marubuta wannnan littafi sun yi zuzzurfar nazari, duba da yadda suka
kawo bayanai daki-daki, kan abin da ya shafi aure da karin magana tun daga kan
ma’anar karin magana da
kuma yadda suke ƙunshe da falsafar zamantakewar aure a cikinsu.
Kasancewar na karanta littafin tun daga farkonsa har ƙarshe, wannan ya sa na
fahimci lungu da saƙonsa kuma na yi bitarsa ta hanyar bayyana
fahimtata dangane littafin kamar haka:
Littafin shi ne irinsa na farko da ya tattaro karin magana masu ɗimbin yawa da suke da dangantaka da aure,
ya kuma yi bayanin ƙunshiyarsu filla-filla tare da fito da falsafar da
ke cikinsu. Kamar yadda mai karatu zai gani, wannan litattafi na musamman ne
domin ya bambanta da sauran litattafai, domin kuwa ya tattauna muhimman abubuwa
da suka shafi aure a matsayin ginshiƙi na samar da tsaftatacciyar al’umma.
Marubutan wannan littafin sun yi hoɓɓasa wajen kawo rabe-raben aure tare da bayyana
yadda Hausawa suke aiwatar da su. Hakazalika, marubuta littafin sun yi amfani
sassauƙan salo wajen tattauna batutuwan da littafin ya ƙunsa, ta hanyar kawo
bayanan tirya-tiryan da kuma bayyana komai dalla-dalla don a fahimci yadda
karin maganar Hausa suke ƙunshe da al’amuran da suka shafi aure da zamantakewar iyali a Bahaushiyar al’ada. Bugu da ƙari, littafin ya kawo
karin maganganu da Hausawa suke da su waɗanda suka shafi tun daga neman aure da wadda ya
kamata a nema a aura da bukin aure da zamantakewar ango da amarya da dai sauran
abubuwa muhimmai waɗanda
ake samun su a dalilin zamantakewar aure.
Gaskiya ban san wani littafi da aka rubuta
da Hausa wanda ya kawo bayani filla-fillah a kan auren Hausawa a cikin ƙunshiyar
karin magana ba kamar wannan. An dubi falsafar da ke cikin karin maganganun da aka kawo a cikin littafin
aka warware tare da tsettsefe bayanansu domin a fahimce su da kyau.
Wannan littafin zai taimaka wa ɗalibai har ma da malamai da masu nazari a matakai
daban-daban na ilimi, wajen bunƙasa adabi da al'adun Hausawa, ta hanyar bayyana
muhimman abubuwan da suka shafi aure. Tun daga neman auren da zamantakewar
auren da ma abubuwan da auren kan haifar.
Bugu da ƙari, littafin zai taimaka matuƙa gaya wajen samar wa ɗalibai musamman masu nazarin adabi da
al’adun Hausawa abin karatu, musamman a jami’o’in Nijeriya da ma na ƙasashen
waje. Domin marubutan wannan littafi sun cika sharuɗɗan rubutu na ilimi wajen kawo duk wani
tushen bayani da madogara da suka yi amfani da ita wajen kalato bayanan da suka
haɗu suka tayar da
littafin.
Don haka, ina sanar da al’umma cewa wannan littafi ya cancanci yabo da
jinjina kuma ya tsere wa tsara. Kuma ina shelanta fitowarsa, domin amfanin ɗalibai da malamai da manazarta da sauran
al’umma. Ina kira ga malamai da ɗalibai
da duk masu ruwa da tsaki a kan nazarin Hausa da su tabbatar sun mallaki wannan
littafi, domin za su amfana ƙwarai daga ɗimbin ilimin da ke ƙunshe a cikinsa.
A ƙarshe, ina addu’ar Allah ya saka wa marubutan wannan littafi da mafificin sakamako, ya kuma ƙara masu dubun sani da faɗin ƙirji.
Dr. Jibril Yusuf
Sashen Harsunan Nijeriya
da Kimiyyar Harshe
Jami’ar Jihar Kaduna.
26 ga watan Oktoba, 2025
Manazarta
Labbo, S.S. & Sani, A-U. (2025). Aure a ƙunshiyar karin magana. Amsoshi Academic Publishers. ISBN: 978-1-257-07209-5. DOI: https://doi.org/10.5281/zenodo.19513449
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.