"Ɗan Sarki fa Sarki ne,
Kai ko bai yi Sarki ba,
Ɗan Sarki fa Sarki ne
Magana tai ta Sarki ce,
Son jama'a kamab Bello,
Wasa da dariya kamab Bello,
Ga milki kamab Bello,
Ga kyauta kamab Bello,
Kuma ga ilimi kamab Bello ".
Haka☝️Makaɗa Alh. Garba Super Gwarzo,
Kano yake cewa a cikin waƙar da ya yi wa Marigayi Alhaji Abdullahi Bello Ka'oje mai
amshi "Toron Giwa mai ban tsoro, Abdullahi Ka'oje ".
Wane ne wannan bawan Allah?
Marigayi Alhaji Abdullahi Bello
Ka'oje ɗan Sarkin
Bargun Ka'oje na 9 ne wato Sarkin Bargu Bello, shi kuma Sarkin Bargu Bello ɗan Sarkin Bargu na 6 ne
wato Sarkin Bargu Aliyu, shi kuma Sarkin Bargu Aliyu ɗan Sarkin Bargu na 4 ne wato Sarkin Bargu
Buhari, shi kuma Sarkin Bargu Buhari ɗan
Sarkin Bargu na 2 ne wato Sarkin Bargu Muhammadu Zangi, shi kuma Sarkin Bargu
Muhammadu Zangi ɗan
Sarkin Bargu na farko ne wato Sarkin Bargu Yakuba wanda yayi mulki daga
shekarar 1823 zuwa wafatinsa a cikin shekarun 1850s, shi kuma Sarkin Bargu
Yakuba ɗan Malam
Sakita ne da ya kafa sarautar Fulani a masarautar Ka'oje dake Jihar Kebbin
Nijeriya ta yau a farko farkon ƙarni na 19.
An haifi Marigayi Alhaji
Abdullahi Bello Ka'oje a garin Ka'oje dake Ƙaramar Hukumar Mulkin Bagudo, Jihar
Kebbi, Nijeriya a cikin shekarar 1931.
Ya yi karatun addini ya kuma
shiga Makarantar boko ta garin Ka'oje a shekarar 1938. Ya halarci Makarantun
Sakandare na Lardi a Sakkwato da Kano(Provincial Secondary School) da Cibiyar
Koyar da Dabarun mulki ta Kongo, Zaria (Institute of Administration, ABU
Zaria).
Ya soma aiki a Majalisar Dokokin
Lardin Arewa a Kaduna inda bayan juyin mulkin soji da aka yi na farko a Nijeriya
ya koma da aiki a Ma'aikatar lamurran cikin gida ta Tarayyar Nijeriya.
Ya yi aiki a Lardin Zazzau da
kuma Lardin Jos. Alh. Abdullahi Ka'oje ya yi aiki a Cibiyar horas da Jami'an
Gwamnati(Staff Training Center) a Bida da Kano da Kamfanin buga Jaridar New
Nigeria da Gidan Rediyon Nijeriya na Kaduna inda ya taɓa gabatar da wani shiri mai suna "Kunun
Kanwa" ya kuma rubuta wani littafin ƙagaggen labari mai suna "Dare Ɗaya
Allah Kanyi Bature" ya kuma taɓa
aiki a Sashen Hausa na Gidan Rediyon BBC London. Haka zalika yayi aiki a
Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Ƙasa(Nigerian Ports Authority, NPA).
Ya shiga aikin Kwastan a matsayin
Sufiritandan inda ya zauna a Sapele da Idi-Iroko da kuma Sakkwato.
Allah SWT ya yi masa rasuwa a
shekarar 1979 a lokacin da yake jagorancin ofishin Kwastan na Sakkwato a
mashigin ruwan Kogin Neja na Tuga, Ka'oje sanadiyar hatsarin /haɗarin jirgin ruwan dake ɗauke dashi.
Ya bar matan aure guda biyu,
Hajiya Asma'u (Ladidi) da Hajiya Rabi da ya'ya guda 5, biyu maza da mata 3.
Daga cikin ya'yan akwai Buhari Abdullahi wanda Jami'in Yan Sanda ne a Kano da
kuma Hajiya Hadiza dake aiki da Hukumar Kwastan a Abuja.
Ƙasar Ka'oje wasu jinsin mutane ne da ake
kira Bargawa waɗanda a
halin yanzu ana samun su a wasu sassa na Jihar Neja ta Nijeriya kamar Bussa da
kuma wani sashe na Jamhuriyar Benin ne suka ƙirƙire ta shekaru da dama da suka wuce.
Wasu Fulani da suka fito daga
Futa Toro dake Kasar Senegal ta yau sun shigo yankin Kasar Hausa daga ɓangaren yamma. Suka jiɓinci lamarin Jihadin
jaddada Addinin Musulunci na Daular Usmaniyya da Mujaddadi Shehu Usman
Danfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi ya jagoranta a ƙarni na 19.
Bayan kammala jihadi aka damƙa su
ga jagoran yankin Daular na yamma mai hedikwata a Gwandu wato Malam Abdullahi Ɗanfodiyo,
suka zauna a wani gari kusa da Gwandu da ake kira Gulumbe.
Bayan wafatin Malam Abdullahi Ɗanfodiyo
sai masu jagoranci na Gwandu suka nemi waɗannan
Fulani a ƙarƙashin
shugabanci Malam Sakita da su kafa mazauni na Ribaɗi wajajen Kogin Neja domin kariya daga
hare-haren al'ummomin dake zaune a wannan wuri.
A lokacin da Malam Sakita da
Jama'arsa suka riski Ka'oje sun tarad da Bargawan nan da ba addinin Musulunci
suke biya ba a lokacin a ƙarƙashin mulki wasu mutane guda biyu, Doka da Galadima suka yaƙe su
har sai da suka samu galaba a kan su. Wannan ne dalilin samar da sarautar
Fulani a Ka'oje ya zuwa yau, inda Yakuba ɗan
Malam Sakita ya zama Sarki na farko daga zuriyar waɗannan Fulani da laƙabin "Sarkin
Bargu" a shekarar 1823.
Daga wancan lokaci ya zuwa yau an
yi sarakuna 13 kamar haka :-
1. Yakuba ɗan Malam Sakita.
2. Muhammadu Zangi ɗan Yakuba
3. Ibrahim Zangi ɗan Yakuba
4. Buhari ɗan Muhammadu Zangi
5. Muhammadu ɗan Buhari
6. Aliyu ɗan Buhari
7. Abdullahi ɗan Aliyu Buhari
8. Umaru Kigo ɗan Aliyu Buhari
9. Bello ɗan Aliyu Buhari
10. Amadu ɗan Aliyu Buhari
11. Shehu ɗan Aliyu Buhari
12. Usman Adamu
13. Mustapha Usman
Adamu.
A cikin wannan waƙa da
ta bijiro da wannan sharhi Makaɗa
Alh. Garba Super ya taskace wasu muhimman batutuwa kamar gadon sarauta na wanda
ya yiwa waƙar
inda yake cewa "Ɗan Sarki fa Sarki ne kai ko bai yi Sarki ba", da muka
bibiyi salsalar Marigayi Alhaji Abdullahi Bello Ka'oje mun gano cewa mahaifinsa
da kakansa duka sun yi sarauta.
Ya ambata masa ilimi, mun lura
har littafi ya rubuta, ya ambaci matarsa Ladidi (Asma'u) da ya'yansa
Hadiza(Hadizatul Kubura) da Buhari da sauran batutuwa masu yawa.
Haƙiƙa wannan waƙa tana ɗauke
da lamurran da ake iya nazarta a duniyar Adabin Hausa.
A wannan hoto Marigayi Alhaji
Abdullahi Bello Ka'oje ne.
Allah SWT ya jiƙan
Marigayi Alhaji Abdullahi Bello Ka'oje da dukan sauran magabatanmu ya sa mu
wanye lafiya mu cika da kyau da imani Alfarmar Sahibul Qiblataini Rasulallahi
Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya rabbal alamin.
Daga Taskar:
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
03/07/2026.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.