𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam Khamis. Allah Ya saka maka da alkhairi. Gaskiya muna jin daɗin wannan channel, muna ƙaruwa sosai. Tambayata ita ce: Mene ne hukuncin Sallah da takalmi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu.
Sallah da takalmi ya halatta, idan takalmin yana da
tsarki (babu najasa a jikinsa), kuma ba zai cutar da masallaci ko sauran masu
ibada ba. Dalili kuwa shine a lokacin Annabi (SAW) da Sahabbansa suna sanya
huffi su yi sallah da su a ƙafafunsu.
HUJJAR DAGA SUNNAR MANZON ALLAH (SAW): Ya
halatta mutum yayi sallah da takalma domin Manzon Allah (SAW) yayi kuma yayi
umurni da ayi. Manzon Allah (SAW) ya ce: "Ku yi sallah da
takalmanku, (ku sãɓawa Yahudawa) domin lalle Yahudawa ba sa sallah da
takalmansu." . An rawaito daga Abi Maslama Sa'id bin
Yazid Al-Azdi, ya ce: Na tambayi Anas bin Malik ko Manzon Allah (SAW) ya yi
sallah da takalmi, sai ya ce "Kwarai kuwa." .
Har ila yau, Amru ɗan Huraith ya ce: "Na ga Manzon Allah (SAW)
yana yin sallah yana sanye da takalma da aka ɗinka." .
SHARUƊƊA DA KA'IDODI: Sallah
da takalmi Sunnah ce ta Annabi (SAW), idan takalmin suna da tsarki (babu najasa
a jikinsu). Amma a yau, idan kana cikin masallaci mai tsafta, ya fi dacewa ka
cire takalminka. Musulunci addini ne na sauƙi, yana koyar da tsafta da sassauci
a ibada. Saboda haka, kada kayi sallah da takalma a duk inda zaka
janyo tarzoma – idan ka sami jama'ar da ke kula da
masallaci basu aminta da ayi masu sallah da takalma ba, to kada kayi. Ko idan
takalminka zai kazamta masallaci, duk da haka kada kayi. Idan kayi ka cutar da
jama'a, zaka iya samun zunubi. Sallah da takalmi ta fi dacewa idan mutum yana
yin sallah a fili, a kan titi, a gona, ko a wuraren da babu shimfida.
A taƙaice, sallah da takalmi halal ne
kuma Sunnah ce idan takalmin suna da tsarki, amma a
masallatai masu tsafta, cire su ya fi dacewa don kiyaye tsafta da kuma guje wa
cutar da wasu. Allah ne Mafi sani.
Allah ne Mafi sani.
Amsa ta ƙare. Alhamdu lillah.
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.