𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam mene ne hukuncin macen da tayi wa kishiyarta asiri tana bunnewa, kuma ta shiga tsakanin ‘ya’yanta da mahaifinsu, duk ta hanyar asiri”?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Yi wa wani asiri ta
hanyar raba shi da wani da yake kauna da juyar da shi daga halin kauna da
soyayya zuwa halin gaba da kiyayya, mummunan aiki ne, kuma nau’i ne na sihiri
da ake kira ‘SIHRUT TAFRIK’, ko ‘AS-SARF’, wato sihirin rabawa tsakanin
ma’aura, ko masoya, ko juya hankalin wani da susuta shi da zautar masa da
hankalinsa daga wani abu da zai amfane shi zuwa mai cutar da shi, ko kuma daga
kaunar abin kaunarsa ko iyayensa zuwa kyamarsu da bijire musu. Akwai hanyoyi da
dama da masu irin wannan mugun aiki su kan bi wurin cimma burinsu.
Hukuncinsa a
musulunci ya zo kurukuru a cikin al-Qur’ani mai girma inda Allah Maɗaukaki ya ambaci cewa
kafirci ne, kuma malamai sun bayyana cewa duk wanda aka kama shi da irin wannan
aiki to hukuncinsa shi ne alkali ya sa a kashe shi kisan kafirci da ridda ta
barin addinin musulunci.
Don haka ya wajaba
wannan mata da duk wani mai mummunan aiki irin nata mai irin wannan bamagujiyar
mugunta da bakar aniya, ya ji tsoron Allah ya tuba.
Lalata kishiya ta
hanyar sihiri da raba ta da mijinta da shiga tsakaninta da ‘ya’yanta ba shi ne
zai jawowa mai neman a yi mata sihirin alherin duniyar da take fada da kishiyar
a kansa ya dawo gare ta ba. Arzikin duniya da na lahira duk a gun Allah yake,
kuma babu wata hanya da za’a same shi sai da yardarsa. Yaya za a yi kuwa a ce
mutum mumini ya jefa ɗan'uwansa cikin
damuwa, ya hana masa kwanciyar hankali; saboda kawai yana ganin cewa shi ne ya
hana shi samun wani abin duniya ko kadaituwa da kaunar miji da soyayyarsa, kuma
musamman ma a ce ta hanyar kafircewa da Allah da bautawa aljanu. Gaskiya wannan
ba karamar tabewa ba ce, da kekasar zuciya, da rashin tsoron Allah, da
fito-na-fito da kaddararsa, da rashin yarda da lamarinsa da dogaro da shi.
Manzon Allah
(sallallahu alaihi wa sallam) Ya gaya mana cewa duk wanda ya je wurin boka ko ɗan duba, kuma ya
tambaye shi kan wani abu har ya gaskata shi, to ya kafirta da abin da aka
saukarwa (Annabi) Muhammad (sallalllahu alaihi wa sallam).
A wata riwayar kuma
ba za’a karbi sallarsa ta kwana arba’in ba. Wannan wanda ya gaskata kenan, ba
tare da ya aikata sihirin ba. Kuma mafi rinjayen maganar malamai ita ce wannan
tambayar da gaskatawar kafirci ne amma karami, ba mai fidda mutum daga
musulunci ba. Amma mai aikata sihirin da mai ba da kuɗi da umurni a yi wa
wani, kuma wanda ake ba wa umurnin ya cika sharuddan da aljanun ke nema a yi
musu, to duk wannan aikinsu ɗaya ne da shi bokan, kafircinsu na fita daga addini ne.
Babban abin da ke
cikin wannan ma shi ne bautawa shaidanu da aljanu da yi musu da’a cikin abin da
suke so, na yanke-yanke ko neman cika wasu sharudda masu dan karen wahala, da
bada umurnin a je wani wuri a yi tono a binne. Wannan duk bautawa aljanu ne,
bayan dumbin dukiyar da mutum zai halakar ta wannan mummunar hanya. Allah ya
tsaremu.
Nasihata ga duk wanda
Allah ya jarraba da wannan mummunar ta’ada ita ce ya gaggauta tuba zuwa ga
Allah, kuma ya yi watsi da wannan shirka, kuma ya dogara da Allah bisa duk abin
da yake nema, sannan ya ji tsoron cewa shi ramin mugunta in an tona shi ba a fa
san wanda zai fara fadawa ba.
Daga cikin manyan
hadurran da wannan mummunan aiki ya kunsa akwai: Shirka da Allah da bauta wa
aljanu. Kila wata ta ce ai ita wurin ‘malami’ kawai ta je ba gun aljanu ba, to
ya kamata ki gane cewa shi wannan da kike kira malami ba ya iya komai da kashin
kansa sai ya yi da’a ga aljanu su kuma su ba shi umurni ya cika musu. Wannan
da’ar da kuma cika sharuddan yadda aljanin ya nema shi ne bakar shirka, domin
bautawa wanin Allah ne da neman yardarsa, wato sanya masa kishiya ta hanyar
mika wani hakkin ibada zuwa ga waninSa, kamar yanka dabba domin waninSa ko da
da sunan Allah ne, ko kuma cika wasu sharuddan da ba Allah ne Ya ce a cika su
ba, musamman kuma wurin bautawa wanda za a yi wannan abu dominsa. Allah kuwa ya
yi kashedi ga dukkan al’umma cewa “Duk wanda ya yi tarayya da Allah to lallai
Allah ya haramta masa shiga Aljanna, kuma makomarsa ita ce Wuta, kuma azzalumai
ba su da mataimaka. Allah ta'ala yasa muda ce.🤲
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.