𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Godiya sosai Akaramakallahu Allah ya jikan magabata, ya sakanya da gidan aljanna🤲 Bayan haka ni ma ga tawa tambayar kamar haka:-- shin idan fitsari ko bayan gida na yaro/yarinya wacce bata fara cin abinciba ya shafi sutura yaya ingancin tsarkinta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Shi fitsarin Qananan
yara ya rabu ne zuwa kashi biyu. Idan fitsarin yarinya jaririya mace ne, to
daidai yake da na babban mutum. wajibi sai an wankeshi. Idan kuma fitsarin
Qaramin yaro ne jariri, to yayyafa ruwa kawai ya wadatar. Amma Malaman Fiqhu
sun ce wannan hukuncin ya keɓanci yaron da bai fara cin abinci bane. Idan ya riga ya
fara cin abinci, to hukuncin fitsarinsa kamar na babban mutum ne. Hujjah anan
ita ce hadisin da Bukhary da Muslim suka ruwaito daga Sayyidah Ummu Qays bintu
Mihsaan (ra) ta kawo wani yaronta wanda bai fara cin abinci ba, ta kawoshi
wajen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya karbeshi ya dorashi akan
cinyarsa mai albarka, Sai yaron yayi masa fitsari. Sai Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) yasa aka kawo masa ruwa ya yayyafa a tufafinsa, bai wankeshi
ba.
(aduba Sahihul
Bukhary hadisi na 223, Sahihu Muslim hadisi na 287).
Akwai wani hadisin ma
daga Sayyiduna Aliyu bn Abi Talib (ra) daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi
Wasallam) yana cewa : "KUYI YAYYAFI GA FITSARIN JARIRI QARAMI, KUMA KU
WANKE FITSARIN YARINYA QARAMA". (Aduba Sunanut Tirmiziy hadisi na 610,
Ibnu Maajah hadisi na 525).
Imam Qataadah yace
Wannan hukuncinsu kenan kafin su fara cin abinci. amma idan har sun fara cin
abinci to Wajibi ne awanke fitsarin kowannensu. Don Qarin bayani aduba Tuhfatul
Maurood shafi na 190).
Matsayin kashi ko
bayan gida na yaro/yarinya daban yake da na fitsari. Ko jaririn ya fara cin
abinci ko yana shan nono ne kawai, idan yayi kashi, suturar ko jikinsa ta zama
najasa, kuma dole ne a wanke wajen da ruwa mai tsarki har sai najasar da
warinta sun tafi.
Bayan gida (Kashi)
najasa ce mai tsanani (NAJASATUL MUGHALLAZAH), kuma babu wata alfarma a kanta.
Dole ne a wanke suturar da ruwa sosai har sai launinta da warinta da duk wata
alama ta najasar ta tafi.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.