𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alekum waramatullahi wbrkth mlan tambayata auren wacce ta taba zina har ta samu ɗan?
HUKUNCIN AUREN MACEN
DA TA TAƁA YIN ZINA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
Hukuncin auren macen
da ta taɓa yin zina har ta
sami ɗa ya halatta a
Shari'ar Musulunci, matukar ta tuba, tuba na gaske da kuma tabbatar da rashin
juna biyu (Istibra'i).
Aure a Musulunci
ibada ne mai tsarki, kuma Shari'a ta tanadi hanyoyin da mutum zai iya gyara
rayuwarsa bayan ya aikata kuskure. Zina babban zunubi ne amma baya haramta aure.
Idan mace ta yi zina ta tuba, tuban tsakani da Allah, to aurenta ya halatta
kamar kowace mace.
Duk girman laifin
mutum in dai ta tuba da gaske, to Allah zai karbi tubanta ya gafarta mata kamar
yadda ya umurci Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya gaya mana:
قُلۡ یَـٰعِبَادِیَ ٱلَّذِینَ
أَسۡرَفُوا۟ عَلَىٰۤ أَنفُسِهِمۡ لَا تَقۡنَطُوا۟ مِن رَّحۡمَةِ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ
یَغۡفِرُ ٱلذُّنُوبَ جَمِیعًاۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِیمُ
"KACE YAKU
BAYINA WAƊANDA SUKA AIKATA ƁARNA BISA KANSU!! KAR
KU FIDDA TSAMMANI DAGA (SAMUN) RAHAMAR ALLAH. HAKIKA ALLAH YANA YAFE DUKKAN
ZUNUBAI BAKI ƊAYA, HAKIKA SHI NE MAI GAFARA MAI JIN ƘAI" (Surah
Az-Zumar: 53)
Malamai sun yi
bayanin cewa idan mace ta tuba, ba wajibi bane ta gaya wa wanda za ta aura cewa
ta taɓa yin zina a baya.
Dole ne macen da shi
kansa namijin idan wanda suka yi zinar ne zai aure ta su fuskanci Allah cikin
kaskantar da kai, su yi nadama, kuma su kuduri aniyar rashin komawa ga wannan
zunubi. Shari'a ba ta halatta auri mazinaciya mai ci gaba da zinar ba. Dole ne
mace ta nuna tsantsar nadama ta gaske kuma ta tuba zuwa ga Allah (S. W. T)
kafin a ɗaura auren. Ba za a ɗaura aure ba har sai
an tabbatar da cewa mahaifarta ba ta ɗauke da wani cikin na daban.
Mazhabar Malikiyya:
Sun tafi akan cewa haramun ne a ɗaura aure idan mace tana da juna biyu na zina,
sai bayan ta haihu. Idan kuma aka ɗaura auren tana da ciki, auren ya ɓaci kuma dole ne a
raba auren.
Mazhabar Hanafiyya da
Shafi'iyya: Suna ganin za a iya ɗaura aure ko da akwai cikin zina (musamman
idan wanda ya yi cikin ne zai aure ta). Sai dai sun yi gadi da cewa miji ba zai
sadu da ita ba har sai ta haihu domin kare tsarkakar shayarwa. Wannan ya dace
da fadin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa: "Kada mutum ya
shayar da ruwansa ga shukar waninsa". Idan wanda zai aure ta shi ne ya yi
zinar da ya haifar da cikin, Malamai sun fi karkata zuwa ga cewa zai fi kyau ta
haihu tukunna sannan a ɗaura auren don kiyaye
shari'ar ko kuma a ɗaura din amma a
kiyaye saduwa.
A karkashin Addinin
Musulunci bai halatta a Ɗaura ma mace aure da wani sabon Miji ba, har sai ta
tabbatar da cewar babu komai a cikin mahaifarta. a Bisa wannan dalilin shi ya
sa Mata suke yin iddah bayan sun fita daga hannun Mijin su kafin su sake aurar
wani Mijin daban. Hakanan duk Matar da ta yi Zina, ko budurwa ce ko bazawara, toh
bai halatta a Ɗaura Mata aure ba har sai ta yi Istibra'i. Wato ta yi Jini
uku, ko kuma a Ƙalla jini guda (a fa'dar wasu Maluman).
Duk Matar da ta
zamanto ita Mazinaciya ce, toh bai halatta a Ɗaura mata aure da
cikakken Mumini wanda ba ya Zina ba. Sai dai idan sun tuba Sahihin tuba irin
tubar da ba za'a sake koma Ruwa ba, Ita Mazinaciyar sai ta yi istibra'i. Sannan
zai halatta Mumini ya aure ta. Allah ne ya fada a cikin ayah ta Uku a cikin
Suratun Nuur.
الزَّانِي
لَا يَنكِحُ إِلَّا زَانِيَةً أَوْ مُشْرِكَةً وَالزَّانِيَةُ لَا يَنكِحُهَا
إِلَّا زَانٍ أَوْ مُشْرِكٌ وَحُرِّمَ ذَٰلِكَ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ
Mazinãci bã ya aure
fãce da mazinãciya kõ mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai aurenta fãce mazinãci
kõ mushiriki. Kuma an haramta wannan a kan mũminai. (Suratul Nur Ayata 3).
Al Imam Ahmad bn
Hanbal ya ruwaito hadisi daga Sayyiduna Abdullahi bn Amru bn Al-Aas (R. A) yace,
"Wani Mutum Mumini ya nemi izinin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa
Sallam) akan yana so zai auri wata Mata mai suna UMMU MAHZOUL wacce ta kasance
kowa ya san tana yin Zina. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya
karanto masa wannan ayar 3 ta cikin Suratun Nuur (A duba Hadisi na 11359 a
cikin Sunanul Kubrah ta Imamun Nisa'iy).
Hakanan akwai wani
Sahabi mai Suna MARTHAD IBNU ABI MARTHAD (ra) ya taɓa neman izini awajen
Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa yana so zai auri wata Mata mai suna
'UNAAƘ" ta kasance Mazinaciya ce agarin Makkah. Sai Manzon
Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi shuru bai bashi amsa ba, har sai da
wannan ayar ta 3 cikin Suratun Nuur ta sauka. Aduba Sunanu Abi Dawud hadisi na
2051. Da kuma Sunanun Nisa'iy juzu'i na 6 shafi na 66 acikin kitabun Nikahi.
Bisa waɗannan hujjojin ne
Malamai irin su Imamu Ahmad suka dogara. Sun ce bai halatta a auri duk Matar da
ta yi zina ba, har sai bayan ta tuba.
Duk wacce ta tuba
daga zunubi kuma ta yi nadama sannan ta nisanci wannan laifin, to Allah zai
gafarta mata wannan laifin koda kuwa ta yi shekaru masu yawa tana aikatawa. Allah
ya faɗa acikin Alƙur'ani cewa:
إِلَّا
ٱلَّذِینَ تَابُوا۟ مِنۢ بَعۡدِ ذَ ٰلِكَ وَأَصۡلَحُوا۟ فَإِنَّ ٱللَّهَ
غَفُورࣱ رَّحِیمࣱ
"SAI DAI WAƊANDA SUKA TUBA BAYAN
NAN (WATO BAYAN SUN AIKATA LAIFIN) KUMA SUKA KYAUTATA AIKI, TO HAKIKA ALLAH MAI
GAFARA NE MAI JIN ƘAI GARESU". (Surah An-Nuur: 5)
Ɗan da aka haifa ta
hanyar zina ba ya bin uban da ya yi zinar ta fannin nasaba na shari'a, sai dai yana
bin mahaifiyarsa. Wannan ɗa zai gaji
mahaifiyarsa da danginta, amma ba zai gaji uban da ya yi zinar ba, kuma shi ma
uban ba zai gaje shi ba.
Haifuwarsa ta hanyar
zina ba ta rage masa daraja ko haƙƙoƙi na ɗan Adam a gaban Allah
ba, muddin ya tashi da tsoron Allah da aikata nagarta.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.