𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malam khamis. Gaskiya muna jin dadin wannan group naka mai tarin albarka. malam khamis Allah ya biya ka da gidan Aljanna Allah ya tsareka a duk inda kake Allah yasaka maka da mafificin alkhairi. Tambaya ta a nan shi ne; wanne Annabawa ne waɗanda Allah Ya ambaci sunayensu da kuma zuwansu duniya tun kafin a haife su? Na gode
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuhu
A cikin Alƙur'ani Mai girma
akwai Annabawa waɗanda Allah Ya ambaci
sunayensu da kuma zuwansu duniya tun kafin a haife su. Sune:
1. Annabi Yahaya (A
S).
2. Annabi Isma'il (A
S).
3. Annabi Ishaƙ (A S).
4. Annabi Yakub (A S).
5. Annabi Isah (A S).
6. Annabi Muhammad
(Sallallahu Alaihi Wasallam)
1. Allah Ya ambaci
sunan ANNABI YAHAYA tun kafin a haife shi acikin Alƙur'ani:
يَا
زَكَرِيَّا إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَامٍ اسْمُهُ يَحْيَىٰ لَمْ نَجْعَلْ لَهُ
مِنْ قَبْلُ سَمِيًّا
"Yã zakariyya!
Lalle ne Mũ, Munã yi maka bushãra da wani yãro, sunansa Yahaya. Ba Mu sanya
masa wani takwara ba a gabãni. " (Suratu Maryam aya ta 7).
2. Allah Ya ambaci
sunan ANNABI ISMA'IL tun kafin a haife shi. Bayan tsawon lokaci da Annabi
Ibrahim (A. S) bai samu haihuwa ba kuma ya tsufa, sai ya roƙi Allah Ya ba shi ɗa na gari. Addu'ar ta
zo a cikin Suratul Saffat (aya ta 100):
رَبِّ
هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ
"Ya Ubangijĩna!
Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne. "
Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi addu'arsa, Ya kuma
yi masa albishir da haihuwar ɗa mai haƙuri (ANNABI ISMA'IL A. S) tun kafin
haihuwarsa, kamar yadda aya ta 101 a cikin Suratul Saffat ta tabbatar:
فَبَشَّرْنَاهُ
بِغُلَامٍ حَلِيمٍ
Sai Muka yi masa
bushãra da wani yãro mai haƙuri.
Wannan ɗa da aka haifa (wato
ANNABI ISMA'IL) daga matarsa Hajara. Allah Ya siffanta shi da kasancewa mai haƙuri tun kafin a haife
shi. shi ne kuma Allah Ya jarrabi Annabi Ibrahim da umurnin yanka shi, suka yi
biyayya tare, wanda hakan ya zama babban jarrabawa da kuma tushen babban
tarihin gina Ɗakin Ka'aba tare.
3. Allah Ya ambaci
sunan ANNABI ISHAƘ tun kafin a haife shi acikin Alkur'ani. Bayan haihuwar
Annabi Isma'il (A. S) ne kuma daga bisani Allah Ya sake yi wa Annabi Ibrahim (A.
S) bushara da haihuwar ANNABI ISHAƘ (A. S) a lokacin da
ya tsufa. An yi masa albishir tare da bayyana sunansa ga mahaifiyarsa (Sayyida
Sarah) da mahaifinsa (Annabi Ibrahim) ta bakin Mala'iku. inda Allah Ya ce:
وَامْرَأَتُهُ
قَائِمَةٌ فَضَحِكَتْ فَبَشَّرْنَاهَا بِإِسْحَاقَ وَمِنْ وَرَاءِ إِسْحَاقَ
يَعْقُوبَ
"Kuma matar tasa
tana tsaye, sai ta yi dariya, sai Muka yi mata bushara (albishir) da haihuwar
ISHAƘ, kuma a bayan ISHAƘ (Muka yi mata
albishir) da haihuwar YAƘŪB. " (suratu Hud,
aya ta 71).
Wannan bushara ce da
Allah Ya yi a lokacin tana zaune, kafin a haifi Annabi ISHAƘA, wanda shi ne
mahaifin Annabi YAƘUB.
وَبَشَّرْنَاهُ
بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِنَ الصَّالِحِينَ
Kuma Muka yi masa
bushãra Da IS'HÃƘA ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
(Surah: As-Saaffaat, Ayat: 112)
Bayan wannan lokacin
da aka ambaci sunansa a matsayin wanda za a haifa, Allah Ya sake jaddada
matsayinsa da albarkar da ke tattare da shi a wasu ayoyin:
الْحَمْدُ
لِلَّهِ الَّذِي وَهَبَ لِي عَلَى الْكِبَرِ إِسْمَاعِيلَ وَإِسْحَاقَ ۚ إِنَّ
رَبِّي لَسَمِيعُ الدُّعَاءِ
"Gõdiyã ta
tabbata ga Allah wanda Yake Ya bãni inã a cikin tsufa ISMÃ'ILA da IS'HÃƘA. Lalle ne
Ubangijina, haƙĩƙa, Mai jin addu'a ne.
" (Suratu Ibrahim Aya ta 39:')
4. Haka kuma Allah Ya
ambaci ANNABI ISA (Almasihu) kafin a haife shi a cikin alkur'ani ta bakin
Mala'iku inda aka ce:
إِذْ
قَالَتِ الْمَلَائِكَةُ يَا مَرْيَمُ إِنَّ اللَّهَ يُبَشِّرُكِ بِكَلِمَةٍ مِنْهُ
اسْمُهُ الْمَسِيحُ عِيسَى ابْنُ مَرْيَمَ وَجِيهًا فِي الدُّنْيَا وَالْآخِرَةِ
وَمِنَ الْمُقَرَّبِينَ
A lõkacin da malã'iku
suka ce "Yã Maryamu! Lalle ne Allah Yana bã ki bushãra da wata kalma daga
gare Shi; sũnansa Masĩhu ĩsa ɗan Maryama, yana mai daraja a dũniya da Lãhira kuma daga
Makusanta. (Suratu Ali 'Imran Aya ta 45).
5. Allah Ya ambaci
sunan ANNABI MUHAMMAD (Sallallahu Alaihi Wasallam) tun kafin a haife shi acikin
Alkur'ani. Allah Maɗaukakin Sarki ya
bayyana cewa Annabi Isa (A. S) ya yi wa jinsin Bani Isra'ila bishara da zuwan
Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) kafin ma a haife shi, inda ya
ambace shi da sunansa na sananniya wato "AHMAD" inda Allah Ya ce wa:
وَإِذْ
قَالَ عِيسَى ابْنُ مَرْيَمَ يَا بَنِي إِسْرَائِيلَ إِنِّي رَسُولُ اللَّهِ
إِلَيْكُمْ مُصَدِّقًا لِمَا بَيْنَ يَدَيَّ مِنَ التَّوْرَاةِ وَمُبَشِّرًا
بِرَسُولٍ يَأْتِي مِنْ بَعْدِي اسْمُهُ أَحْمَدُ ۖ فَلَمَّا جَاءَهُمْ
بِالْبَيِّنَاتِ قَالُوا هَٰذَا سِحْرٌ مُبِينٌ
Kuma a lõkacin da Ĩsã
ɗan Maryayama ya ce:
"Yã BanĩIsrã'ĩla! Lalle nĩ Manzon Allah ne zuwa gare ku, mai gaskata abin
da ke gaba gare ni na Attaura, kuma mai bãyar da bushãra da wani Manzo da ke
zuwa a bãyãna, Sunansa Ahmad (Mashãyabo). " To, a lõkacin da ya jẽ musu da hujjõji, suka
ce: "Wannan sihiri ne, bayyananne. " (Suratus-Saff Aya ta 6).
A cikin wannan ayar, sunansa
ya zo da suna "AHMAD", wanda yana daya daga cikin manyan sunayen
Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) da ke nufin "wanda ya fi kowa
cancantar yabo".
Sunan nan AHMAD da
MUHAMMAD duka sun fito ne daga tushe guda a yaren Larabci wanda ke nufin
"Wanda ake yabo" ko "Mai yawan godiya". Manzon Allah
(Sallallahu Alaihi Wasallam) da kansa ya tabbatar a cikin Hadisi cewa yana da
sunaye da dama, ciki har da MUHAMMAD da AHMAD.
Alƙur'ani ya bayyana
cewa wannan bishara ba a baki kawai Annabi Isa ya faɗeta ba; an kuma
rubuta ta a cikin littattafan dā (Attaura da Linjila) kamar yadda aka ambata a
Suratun Al-A'raf.
الَّذِينَ
يَتَّبِعُونَ الرَّسُولَ النَّبِيَّ الْأُمِّيَّ الَّذِي يَجِدُونَهُ مَكْتُوبًا
عِنْدَهُمْ فِي التَّوْرَاةِ وَالْإِنْجِيلِ
"Waɗanda suke sunã bin
Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da
Linjĩla. (Surah: Al-A'raaf, Aya ta157)
Wannan aya shaida ce
mai ƙarfi da ke nuna cewa zuwan Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) shiri ne na Allah tun can fil azal, kuma dukkan manyan
annabawa sun san da zuwansa.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa. . .
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.