𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Idan aka saki Mace tana Shayarwa yaya hukuncin Iddarta zai kasance idan Jinin-Al'ada ya dena zuwa mata saboda Shayarwar da take yi??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wannan tambayar dama nataɓa bada
amsa akanta kimanin Shekaru biyu da suka wuce, wato kamar yadda yake sanennen
abu awajen Mutane cewa akwai Nau'ikan-Mata da yawa waɗanda
Jinin-Al'ada yake tsaya musu alokacin da suke Shayar da Jariransu, wasu bazasu
sake ganin Jiniba har sai sun yaye ''Ɗan''
da suke Shayarwa,
Saidai wasu Matan
jinin yakan dawō musune bayan Shekara ɗaya,
wasu Matan kuma bayan watanni Shidda(6) ko wani abu makamancin haka sai suga
Jinin-Al'adarsu yazo, yayin da wasu Matan kuma dama kwata kwata su Jinin-Al'ada
baya tsaya musu sakamakon Shayarwar da sukeyi, kawai da Jinin-Bīƙi yaɗauke
musu sai kuma Jinin-Haila yabiyo bayansa idan lokacin zuwansa yayi.
Idan ya kasance Mace batayin
Jinin-Al'adane sakamakon Shayar da Jariri da take yi, Malamai sukace irin
wannan Matar idan aka Saketa to zatayi ta jirane har sai tayi Jini-3 koda kuwa
hakan zai kaita zuwaga lokacin da zata yaye Jaririn da take Shayarwar wato
Shekaru biyu kenan, to dōlene har sai tagama waɗannan
Jinane-Guda-3 sannan iddarta zata ƙare, danhaka kenan idan
Sakine irin na "Kōmē" to Mijin yana da damar yace yadawō da Matarsa koda kuwa bayan Shekara biyune da yin
Sakin matuƙar dai batayi Jini-3
atsakaniba, wannan maganar kuma
dukkan Malamai-Fuƙaha'u
sunyi Ijma'i
akan haka, Hujjarsu kuwa ita ce faɗin Aʟʟaн( ﷻ
) dake cikin wannan aya:
وَالْمُطَلَّقَاتُ يَتَرَبَّصْنَ بِأَنْفُسِهِنَّ ثَلَاثَةَ
قُرُوءٍ ۚ
MA'ANA:
(Matan da) aka Sakesu zasu
zaunane harsuyi Jini-3 (tsarki-3) (Suratul Baƙara
Aya ta 228)
Danhaka kenan idan Mace tana
so Jinin yazo mata da wuri to saita bayar da Jarīrin nata wata Matar ta Shayar
dashi, kokuma tayi amfani da wani magani wanda zai janyo mata al'adarta
alokacin datake Shayarwar amma da Sharaɗin
ya kasance ba Saki bane irin na "Kōmē" domin idan Sakine irin na
"Kōmē" to bai halatta tayi amfani da magani dan ta janyo al'adarta
ba, domin kuwa Mijinta yana da haƙƙi
akanta na ya mayar da ita kokuma yarabu da'ita, amma idan Sakine irin wanda ba
Sakin-Kōmēba to ya halatta tasha
maganin da zai janyo mata jinin da wuri, amma shima da Sharaɗin
ya kasance anada tabbas kokuma zato mafi rinjane akan cewa maganin yadace da
Jikinta bazai cūtar da'itaba.
To amma idan ya kasance Al'adar-Mace
taɗaukene
sakamakon wani Sababi kamar irin na Shayarwa kokuma rashin lafiya, daga baya
kuma sai wannan Sababin yagushe, Misali ace tawarke daga rashin lafiyar, ko ta
yaye ''Ɗan'' da take Shayarwa, amma duk dahaka jinin
bai zomata ba, to anan sai mafi yawa daga cikin Malamai sukace Iddar irin wannan Matar zata zaunane har tsawon
Shekara guda cur, wato
watanni-9 amatsayin mafi galibin
tsawon lokacin da mai ciki take yi kafin ta haihu, Saikuma watanni-3 amatsayin
Idda, idan anhaɗa yazama watanni-12 kenan.
Danhaka idan yakasance Mace
zatayi Iddane na tsawon Shekara ɗaya,
Misali ace tayi watanni-11, kwatsam kawai sai taga Jinin-Al'ada yazo mata, to
yanzufa lissafincan da tayi na watanni-11 yariga yarūshe, danhaka yanzu dolene
sai ta sake jiran zuwan Jini na-2 da na-3 idan bai zoba har ta sakeyin wata
Shekarar guda cur, to shikenan tagama idda, amma idan taga Jini na-2 yazo koda
kuwa ta sake yin wasu watanni-11 da zuwan na farko, to anan ma lissafinta yasake
rūshewa, danhaka dole sai ta sake jiran wani Jini na-3 yazo sannan tagama idda,
idan kuma jini na-3 bai zoba har ta sake yin wata Shekarar shikenan tagama
Iddarta.
шαʟʟαнυ-тα'αʟα
α'α'αʟαм
AMSAWA
Mυѕтαρнα Uѕмαn
08032531505
Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαɗαппαп
ʟıтαттαғαı καмαя нακα:
''
ﻣﻮﺍﻫﺐ ﺍﻟﺠﻠﻴﻞ " ( 3/404 (
"
ﺍﻟﺘﺎﺝ ﻭﺍﻹﻛﻠﻴﻞ " ( 4/143 (
"
ﺍﻟﻤﻐﻨﻲ ﻹﺑﻦ ﻗﺪﺍﻣﺔ " ( 8/87 (
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.