Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Namiji Ya Yi Wa Mace Sallama

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum Ina da tambaya, tambayata gata kamar haka Allah gafarta malam ina cikin tafiya a matsayina na namiji sai na tarar da mata a hanya toh ko zan iya yimasu sallama?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam warahmatullahi Wabarkatuh

Da farko dai Allah ya umarcemu da yaɗa sallama a tsakaninmu ya kuma wajabta mana mayarda sallama ga daukacin musulmai. Ya sanya sallama ta zama wani abu dake yaɗa soyayya a tsakanin muminai. Allah yace:

وَإِذَا حُيِّيتُمْ بِتَحِيَّةٍ فَحَيُّوا بِأَحْسَنَ مِنْهَا أَوْ رُدُّوهَا ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ عَلَىٰ كُلِّ شَيْءٍ حَسِيبًا

Kuma idan an gaisheku da wata gaisuwa, to, kuyi gaisuwa da abinda yake mafi kyau daga gareta, ko kuma Ku mayar da ita, kuma Allah ya kasance akan dukkan komai mai lissafi. [Suratul Nisa'i aya ta 86]

An ruwaito Abu Hurairah Yace; Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Yace: baza ku shiga aljannah ba har sai kunyi imani, baza kuyi imani ba har sai kunso junanku. Shin bazan gaya muku wani abu ba wanda idan kunyi shi za kuso junanku?, Ku yaɗa sallama a tsakaninku, za ku so junanku" (Muslim ne ya ruwaito shi a hadisi mai lamba 54).

Umarnin yaɗa sallama umarni ne ga kowa (maza da mata) kuma ya shafi dukkan musulmai. Ya haɗa da maza suyiwa maza sallama, mata suyiwa mata sallama, da sallama tsakanin muharraman juna. Anan an shar'anta sallama a tsakanin wannan sashe yayi sallama ga ɗayan sashen da ya aka wajabta ma mayar da sallama.

Amma akwai hukuncin da ya hana namiji yin sallama ga macen da ba muharramarsa ba idan yaji tsoron aukuwar fitina a dalilin wannan sallama.

Babu laifi ga namiji yayiwa mace sallama batareda yin musabaha da ita ba, idan ita tsohuwa ce. Amma bazai yiwa wacce ba tsohuwa ba sallama idan baida tabbacin rashin aukuwar fitina. Wannan shine sharhin malamai Allah yayi musu rahama.

An tambayi Imam Malik shin za a iya yiwa mace sallama? sai yace: "Idan tsohuwa ce banga karhanci a sallamar ba, amma idan ba tsohuwa bace bana son haka"

Al-Zarƙaani yayi bayanin dalilin da yasa imam malik yace baya son haka, a ```sharhinsa na Al-Muwatta```: Saboda yana tsoron fitina idan yaji muryarta idan zata mayar da sallama.

Acikin _*(Al-Adaab al-Shar'iyyah 1/370)*_ ance:

Ibn Muflih ya kawo cewa Ibn Mansoor ya tambayi Imam Ahmad akan yiwa mata sallama sai yace: Idan matar tsohuwa ce babu laifi.

Saalih (Dan Imam Ahmad) Yace na tambayi babana akan yiwa mata sallama sai yace: sallamar da ta shafi tsofaffin mata babu laifi, amma waɗanda ba tsofaffi ba baza a sa suyi magana ba wajen mayar da sallama.

Al-Nawawi yace acikin littafinsa mai suna _*Al-Adhkaar a shafi na 407)*_ cewa: Sallamar mata ga mata yan uwansu kamar sallamar maza ne ga maza. Idan macen kuma matarsa ce ko baiwarsa ko muharramarsa, to kamar shi ne yake yin magana da wani namiji. Saboda haka zasu yiwa juna sallama haka mayarwa.

Amma idan wata mace ce daban kuma tanada kyau, kuma yana jin tsoron zata fitineshi, to shi bazai yi mata sallama ba, idan kuma yayi mata sallama, to bai halatta ta amsa masa ba. Hakanan itama bazata yimasa sallama ba, idan tayi masa bazai amsa mata ba, idan ya amsa to yayi makaruhi.

Idan akwai taron mata, namiji zai iya yi musu sallama. Haka idan taron maza ne zasu iya yiwa mace sallama matukar akwai yaƙinin cewa dasu da ita babu Wanda zai fitinu.

An ruwaito daga Asma bintu Yazeed (radiyallahu anhaa) tace; Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) ya wuce ta wajenmu (Mata) sai yayi mana sallama. (Abu Dawood, 5204). Albani ya ingantashi a Saheeh Abi Dawuda.

Al-Haafiz yace acikin Al-Fath: Akan halaccin sallama tsakanin mata da maza: Abinda ake nufi da ya halatta shine idan babu tsoron fitina.

Al-Haleemi yana cewa Saboda Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) Ma'asumi ne kuma an kiyaye shi daga fitina. Duk wanda keda yaƙinin ya tsira daga fitina, to zai iya yiwa mata sallama. Idan kuma akasin hakan ne, to ya tsare kansa yayi shiru.

An ruwaito Al-Muhallab yana cewa: Ya halatta maza suyiwa mata sallama haka mata suyiwa maza sallama idan babu fitina.

Domin Neman karin bayani duba: _*(Ahkaam Al-Awrah wa'l-Nazar na Musaa'id ibn Ƙaasim al-Faalih.*_

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

 ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments