Ticker

6/recent/ticker-posts

Tushen Farin Ciki

Ɗanladi Haruna (2020). Tushen Farin Ciki. Muhalli, Sutura (Labaran Da Suka Samu Nasara a Gasar Gajerun Labarai a Kan Muhalli Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2020). Darma Digital Prints.

TUSHEN FARIN CIKI

Na

Ɗanladi Haruna

Yanayin garin ba yabo ba fallasa, to amma duk da kasancewar akwai lullumin gajimare, zufa na bajekolinta. Cikin ma’aikatar ilmi kuwa, a ofishin su Sammani, sanyin Iyakwandisha ne ke karakaina gwanin daɗi.

Ibrahim Shehu na ta waɗari cikin kwamfuta. Sammani kuma na zaƙulo takardu a fayiloli yana miƙa masa. Ni'imar ofishin bata sa fuskar Sammani ta sauya daga ta shanu ba, lokaci zuwa lokaci sai ya girgiza kansa ya yi ajiyar zuciya. Ibrahim ya lura da yanayin da Sammani ke ciki. Bai ce masa komai ba, har sai da suka kammala aikin tukunna.

“Yau da alamun baka cikin walwala. Allah ya sa dai ba Madam ce ta jawo ba.” Ibrahim ya ce da Sammani cikin zolaya. Sammani ya yi ajiyar zuciya ya ce, “kai dai ayi sha'ani yallaɓai. Yau da nahisa na tashi. Gidana da kwanaki katangar ta rushe sakamakon ruwan sama, yau kuma ɓarawo ya shiga ya sace min ragon sunan da na yi tanadi. Ga haihuwa ko yau ko gobe.”

Cikin tausaya wa Ibrahim ya ce, “assha! Abu bai yi daɗi ba, Allah ya maida alheri.”

“Amin yallaɓai. Na gode.” Sammani ya faɗa. Daidai lokacin wayarsa ta yi ƙara. Ya duba ya ga matarsa ce ke kira. Ya ɗauka. Ya ji muryarta a raunane tana magana kamar mai raɗa cikin alamun ciwo.

“Ba ni da lafiya. Ka ceci raina!”

A ɗarare ya ce, “gani nan zuwa mu je asibiti.” Ya dubi Ibrahim watau maigidansa na ofis ya ce, “yallaɓai, zan koma gida. Wataƙila haihuwar ce ta zo. Tana kwance ba lafiya.”

Ibrahim ya ce, “Allah ya raba lafiya. Ka hanzarta kai ta asibiti. Kar a zauna gida tsammanin wa rabbuka.”

Tuni Sammani ya yi fita bai ji ƙarshen maganar maigidansa ba. Ya buga babur ɗinsa da hanzari ya fita daga ma'aikatar tasu ya nufi gida. Lokacin kuwa gari ya soma canja kamanni, yanayin samaniya ya zama murtuk. Curarrun gajimare sun dunƙule sun lulluɓe hasken rana, cikin hanzari kuma suka rikiɗe zuwa baƙiƙƙirin. Babu jimawa iska ta soma kaɗawa tana awon gaba da tarkace da sauran abubuwa marasa nauyi.

Ƙura na bubbule fuskar Sammani ya yin da yake shara gudu, amma bai kula ba. Burinsa ya isa gida ya taimakawa matarsa. Ya san wannan watan ne zata haihu, don haka ya shiga tanadin kayan haihuwa amma ga ɓarawo ya yi masa ƙafar ungulu.

Bai yi nisa sosai ba ruwa ya tsuge kamar da bakin ƙwarya. Shi kuwa kamar kaza yake, idan ruwan sama ya taɓa shi sai ya kwanta zazzaɓi. Don haka ya zaɓi hanyar lafiya a bi ta da shekara. Ya samu waje ya fake.

Yana fakewa sai wayarsa ta shiga ƙara, alamar kira ya shigo. Ya duba mai kiran. Matarsa ce. Nan take ya ji hankalinsa ya tashi. Ga bikin zuwa amma babu zanin ɗaurawa. Sammani na tsananin ƙaunar matarsa. 'Yarsu ɗaya, yanzu ne haihuwa ta biyu. A baya a gidansu ta haihu.

Unguwar Zurmawa inda gidan Sammani yake, galibi 'yan 'Rabbana-Ka-wadata mu’ ne ke zama irin na 'yan marina. Kowa da inda ya sa gaba. Duk da sababbin gine-gine ne amma kowanne gini da inda ya karkata. Gwamutsin gine-ginen ya jawo cunkoson lunguna da kwataman da ruwan da ba ya gudana. Kana dosar unguwar za ka wani iri ɗoyi gami da samami na tashi. Ga wani irin zafi mai ratsa jiki na bugun fuska. Mata da yaran unguwar sau tari su kan kamu da wasu irin ƙuraje da tari mara kan gado.

Gidan Sammani wanda a baya yake a sarari, yanzu ya koma cikin lungu sakamakon ginin da aka yi wanda ya toshe babbar hanyar shiga unguwar.

Duk wani ƙoƙarin hanya da mutanen unguwar suka yi domin daƙile ginin ya tashi a tutar babu. Wannan ginin ya toshe babban layin unguwar, har ya zamana babu inda mota za ta shiga, sannan magudanan ruwa duk sun toshe. Shi kuwa ruwa ba a yi masa shamaki, da aka toshe masa hanya, sai ya koma gidajen da ke kusa ya mamaye, masu rarraunan gini suka yi ta zubewa ciki har da katangar gidan Sammani. Da buhu ya kange gidansa yadda ba za a hangi ciki ba.

Ya kara wayar a kunnensa yana mai cewa, “ina tafe. Ruwa ne ya hana ni isowa.”

Cikin rarraunar murya ta ce, “ga maƙota sun zo za mu tafi asibiti.”

Ya ce, “to a samu abin hawa kafin na zo.”

Daga ɗaya ɓarin sai ya ji maganar wata mata na faɗin, “bani wayar na yi masa magana.” Ya ji muryar maƙociyarsu na cewa, “ba za ta iya tafiya ba fa. Dole sai ka zo an tallafa mata. Mu nan duk mata ne, muna buƙatar taimakon namiji. Ka yi wa Allah ka zo yanzu.”

Ya kashe wayar cikin tashin hankali da tunani iri-iri. Ya haƙiƙance dai babu abin hawar da zai iya shiga lungun da gidansa yake. Shekararsa biyu a ciki amma har yanzu bai san yadda za ya yi wa maziyarta kwatancen gidansa ba, domin duk alamar da yake bayarwa, kafin wani lokaci sai ta ɓace.

Wata zuciyar na yi masa gargaɗi cewar, 'ka yi gaggawa ga ceton matarka. Idan ka kuskura ta rasa ranta, to alhakin na wuyanka, kuma 'ya'yanta ba za su taɓa yafe maka ba!' Ya yi firgigit kamar wanda ya farka daga barci. A lokacin ya lura a tare da shi akwai wasu jama'ar da ke fake ruwa har da ma su haya da babur mai rumfa.

Ba tare da jinkiri ba ya yi wa ɗaya daga cikinsu bayanin halin da yake ciki. Ya ƙara da cewa, “ka taimaka min mu je a ɗauke ta zuwa asibiti.” Mai babur ya amince suka tafi.

Lokacin da suka isa ruwa ya tsagaita sai yayyafi. Aka yi dabara aka taitayo Sadiya aka saka cikin babur zuwa asibiti.

Suna hanyar zuwa asibiti Sammani na ta karatun wasiƙun jaki cike da takaicin yadda unguwar Zurmawa ta zarme, kullum sai ƙara matsewa take da gine-ginen rashin kan gado ba tare da la'akari da abin da ka je ya zo ba. Wata zuciyar kuma ta ƙara ingiza shi bisa tsanar Alhaji Gambo wanda ya jawo musu tarin matsaloli birjik a unguwa. Sun sha tattauna wannan maganar da maƙwabtansa amma babu yadda suka iya. Mai ƙumba shi ke susa, shi kuwa kuturu sai dai shafa. Suna ji suna gani ginin Alhaji Gambo ya zame musu ƙurjin gwiwa mai wuyar fasawa.

****

Malam Mamman wanda aka fi sani da Dogo, shi ne maƙocin Sammani na kusa. Ƙaramin ma'aikaci ne a wani kamfanin gina hanyoyi. Gidansa kamar na sauran ya-ku-bayi, bai wuce a kira shi kango ba. Da ƙyar ya ƙuƙuta ya yi rufi ya shiga ba tare da ko ƙasar ciko ba.

Rannan ya nemi alfarma a wajen aiki aka ba shi ƙasar ciko mota guda. Sai dai ba hawan ba saukar inji madugun kutare. Motar da ake wa laƙabi da gingimari ba za ta iya kutsawa lungun nan ba. Dogo kuma ba shi da kuɗin da za ya iya biya a kwaso daga titi zuwa gidansa.

Sai ya yi wata dubara, ya shaidawa direban ya bi ta wata siriryar hanya da motar za ta kurɗa ta shiga. Mota ta shiga lungu tana bi ta tsakanin kwatoci da ramukan ‘soakway’. Cikin rashin sa'a ta taka wani ramin 'soakaway' da aka gina a ƙofar wani gida. Nan fa ƙafa ɗaya ta rufta ciki. Nauyin kaya da nauyin motar suka tararwa katangar gidan ita ma ta rubza.

Juyin duniya motar ta kasa fita. Mutane suka taru, aka ga cewar ba za a iya cire motar ba sai an juye ƙasar da ta ɗebo a wajen. To amma daga juyewa, sai ƙasar ta toshe ƙofar shiga gidan. Nan fa aka yi haihuwar guzuma, layin ya zamana ba shiga ba fita, ƙofar gidan ta toshe, ga mata da yara a ciki suna koke-koke. Jama'a suka samo tsani aka fitar da su.

Jidali tun safe har gefin magariba ana fama, aikin hula ya kai ga dare. Sammani na cikin waɗanda suka tafi kamfanin su Dogo suka sanar da su abin da ke wakana. Bayan hawa da sauka tsakanin mutanen Zurmawa da kamfanin, aka da aiko da katafila domin cire motar.

Assha, ashe dai gyaran gangar auzinawa aka yi. Katafila ta shiga lungun a kaikaice. Ta miƙa hannunta mai ruguje gini ta tura motar daga inda ta maƙale. Garin direban ya dawo da hannun daidai ya daki falwaya. Nan take kuwa ta faɗi, wayoyin jiki duka suka tsinke. Ita kuma motar da aka yi nasarar cirewa daga ramin bayan gida ta daki wani garu, nan take shi ma ya zube.

Dogo ya gigice, ya ransa inda zai sa kansa. Ya tabbatar asarar da ya janyowa kamfaninsu da masu gidajen unguwarsu, ko an sayar da gidansa ba zai biya ba. Ya ji kamar ya zura a guje ya bar garin. To amma ya saduda, domin gudun da babu tsira kwanciya ta fi shi.

Gwano baya jin warin jikinsa. Mutanen unguwar gaba ɗaya ba su dubi cewar rashin tsarinsu ne ya jawo wannan matsala ba, sai suka ɗauki laifin gaba ɗaya suka ɗorawa Alhaji Gambo wanda ya gine babban layin da motoci suke iya shiga unguwar salum alum.

Labarin tsautsayin nan ya watsu cikin unguwa, hankalin kowa ya karkata kan tilas a samo mafita. Cikin daren nan jama'a suka taru ana tattauna yadda za a ɓullowa lamarin. Dogo ya zama kamar wani taɓaɓɓe ba shi da kataɓus.

A wajen taron wani dattijo ya ce, “tun farko dai wannan unguwar ba a gina ta bisa tsari ba. Masu gonaki ne suka cuce mu. Kowa ya yanka feginsa yadda yake so mu kuwa muka saya saboda tsira da mutuncinmu.” Wani mutum ya yi farat ya ce, “son zuciyarmu ne ya jawo. Kowa aka nuna masa fili, ba zai yi wani tunani ba sai kurum ya hau gini. Ni ban taɓa ganin unguwa mara kan gadon wannan ba. Ga ƙazanta, ga shi ta zama mafakar ɓarayi ga ba wani abu da gwamnati ke iya yi mana. Babu ruwa, babu makaranta, babu komai sai azaba.”

Wani kuma ya ce, “duk mu bar wannan zance, da a ce ba mu zuba ido har aka gine mana babban layin da ababen hawa ke bi ba. Da bamu tsinci kanmu a wannan hali ba. Ku tuna fa jama'a, kyakkyawan muhalli, shi ne tushen farin cikin kowacce al'umma.

Sammani wanda ke cikin taron jama'ar ya ji an taɓo masa inda ke masa ƙaiƙayi. Don haka ya miƙe ya ce, “wallahi duk sakacinmu ne, mun mayar da muhallinmu kamar garken awaki, kowa ya zo da kuɗinsa sai ya yi gini yadda yake so ba tare da la'akari da haƙƙin waɗanda ke kewaye da shi ba.”

Mutane suka maida hankali ga saurarensa ya yin da yake zayyana musu irin ta'asar da ginin Alhaji Gambo ya jawowa mutanen da ke kusa da shi.

“Ya zubar min da katanga, Dogo ɗin nan saura kaɗan tasa ta zube. Rashin katanga ya sa aka shiga gidana aka sace min ragon da na jima ina kiwo. Malam Iliya kuwa, ɗakunansa biyu duk sun zube. Ko jiya matata da ƙyar muka kai ta asibiti za ta haihu. Saboda ba hanyar shigowar abin hawa. Bayan haka, ga sace - sace da ayyukan masha'a da ake tafkawa cikin wannan gini. Jama'a indai muna son kanmu da arziki ya zama wajibi mu kawo ƙarshen wannan ginin da aka yi mana ƙarfa-ƙarfa.”

Mutane suka ji an yi musu ƙaimi, kowa ya yi ta faɗin albarkacin bakinsa. Tsohuwar gabar da ke tsakanin mai akwai da babu ta motsa. Cikin daren nan zuciyar mai tsumma kamar ta yage.

****

Tashin hankali wanda ba a sa maka rana. Wannan azancin ya tabbata ga mutanen unguwar Zurmawa waɗanda suka gamu da gamonsu sabili da ɗaukar doka a hannunsu.

Sun yi haka ne kuwa domin ganin duk koken da suka sha kai wa ga mahukunta a baya bai samu nasara ba. Alhaji Gambo ya tsaya kai da fata cewar gininsa na kan daidai kamar yadda aka tsaga gona aka sayar masa. Don haka ya cigaba da gininsa da taimakon ƙarti madaka kare. Yanzu dai tura ta kai bango, mutanen Zurmawa sun zurma kansu rami mai zurfi.

Sammani na sahun gaba riƙe da dundurusu. Biye da shi matasa ne kowanne riƙe da marushi irin su dagi da masaba da kuma gatari. Suna ihu suna cewa, “sai an rushe, sai an rushe! Hanya muke so. Bama son gini!!”

Sammani ne ya soma dukan katangar iyakacin ƙarfinsa sannan ya waiwaya ga matasan ya ce, “ku rushe ginin nan ku samarwa kanku hanya!”

Akuyar ɗaure ta samu saki! Matasa masu jiran kaɗan suka yi kukan kura suka yanyame katangar nan kamar ƙuda akan nama. Baka jin komai sai ƙarar gatura da masabai suna kirɓar katanga tare da ihun samari. Kafin a yi haka, tuni sun yi gagarumar ɓarna.

Ana tsaka da wannan ta'annati sai aka ji wata irin ƙara mai kama da rugugin aradu. Sai ga wani curarren hayaƙi ya yi sama sannan ya baje ya sulmiyo ƙasa. Duk wanda ya shaƙi iskar sai ya kama tari ba ƙaƙƙautawa. Kafin ƙiftawar ido jami'an tsaro sun bayyana. Nan take suka shiga aikin nasu.

Jama'a suka ce 'ƙafa mai na ci ban baki ba?' Tabbas in ka ga ƙi-gudu lallai sa-gudu ne bai zo ba. Cikin ƙanƙanin lokaci waje ya zama ba kowa sai masu tsautsayin da ruɗewa ta sa suka kasa gudu. Wasu kuma, garin aka tunkuɗe su ƙasa, suka kasa tafiya.

Al’amarin ya zama 'in ba ka yi ba ni wuri'. Unguwar gaba ɗaya ta turnuƙe, babu abin da kake ji sai tari da iface-ifacen neman agaji da ƙarar fashewar barkonon tsohuwa. Jami'an ba su saurara ba, sai bugu da kulki suke suna kama mutane suna cusawa cikin shiga-ba-biya.

Duk da kasancewar rana tsaka ne, amma unguwar Zurmawa ta yi baƙiƙirin sakamakon ƙura da ke tashi saboda titirniyar da ake sha tsakanin jami'an tsaro da gungun matasan da suka sha alwashin rushe ginin nan ko ana ha maza ha mata. Ƙwanjin da hukuma ta nuna ya tilasta su watsar da aniyarsu, kowa ya shiga gudun neman tsira.

 Sammani na cikin waɗanda yaji ya gigita. Ya zura gidansa a guje. Ya shiga wawaken neman ruwa. Babu ruwa inda ya yi tsammani in ban da na shansu wanda ke cikin randa. Cikin gigicewa da ɗimautar yaji da ke shiga ta ido da hanci da kunne, Sammani ya cusa kansa cikin randar. Nan take randar ta fashe.

Bayan kwana bakwai

Faffaɗan falo ne mai ɗauke da kayan alatu daidai gwargwado. Akwai babbar talabijin maƙale a bango ana gudanar da labaran duniya. Hankalin Ibrahim Shehu baya kan labaran da ake nunawa, ya maida hankalinsa ga Sammani wanda ke durƙushe gabansa kamar mai neman gafara yana zayyana masa irin balahirar da ya shiga kwanaki bakwai da suka wuce.

Tun bayan kwana guda da kama su ‘yansanda suka miƙa su kotu da laifin haɗa baki da ɓarnata dukiya da kuma ɗaukar doka a hannu. Alhaji Gambo yana da'awar a biya shi asarar da aka jaza masa sannan kuma yana neman maƙudan kuɗaɗe na ladan gaɓe.

A zama na biyu alƙali ya ba da belin mutanen da aka kama sannan aka ɗaga shari'ar zuwa lokaci na gaba. Dangin Sammani da matarsa mai ɗanyen jego suka yi ta zarya har ya samu kansa.

“Har gida suka bi ni suka kama. Yaji ne ya gigita ni ban san lokacin da na cusa kaina cikin randa ba.” In ji Sammani yana ba wa Ibrahim labarin.

“Yaya ka yi da iyalinka sabon jego?”

Da aka sallame su daga asibiti gidansu ta wuce. Yanzu haka tana can.”

 Ibrahim ya ce, “Allah dai ya kiyaye gaba, amma ka riƙa lura sosai. Ba kowacce rigima ake shiga a fita lafiya ba. Ka auna arziki ma da bata shafi aikinka ba.”

Sammani ya ce, “wannan ma tsautsayi ne wallahi. Irin rashin mutuncin da ake mana a unguwar tamu ya wuce ƙima. Ga shi muna jin raɗe-raɗin wai gwamnati za ta yi mana rusau saboda gine-ginen da ake yi a unguwar ba bisa ƙa'ida ba. Wai za a rushe unguwar gaba ɗaya a sake tsaga filaye awon gwamnati.”

“Ta yiwu su yi hakan. Ko makamancin haka.”

Sammani ya yi ajiyar zuciya ya ce, “Ni dai fatana Allah ya ba ni iko na sake muhalli zuwa wuri mai yalwa. Me za a yi da gini a irin wannan unguwar tamu? Kana gidanka amma baka da walwala? Kullum cikin fargaba. Ga ba tsaro, ga cututtuka, ga ..... Yallaɓai ku dai kun haye tudun mun tsira. Ba ruwanku da wannan ja'iba.”

Ibrahim ya ce, “Kai ma ɗin da ka so da tuni ka mallaki gida mai yalwa, sai ka nuna wayon rashin wayo.”

“Yallaɓai kamar yaya?” Sammani ya ce cikin rashin fahimta. Cikin nutsuwa Ibrahim ya ce, “in ka tuna, shekaru biyu da suka wuce na baka wani fom ka cike. Na shaida maka na bankin lamunin ginin gidaje ne watau Federal Mortagage Bank of Nigeria (FMBN). Na ce da kai duk ɗan ƙasa yana iya nema a ba shi amma a matsayinka na ma'aikaci ka fi kowa damar cin moriyar shirin. Tun ranar da na baka fom ɗin baka ƙara yi min maganarsa ba, sai kwatsam ka sanar da ni tarewarka a unguwar Zurmawa.”

Sammani ya ji wani irin sanyi a jikinsa kamar an kwara masa ruwan ƙanƙara, ya ji jikinsa na ƙyarma kamar ana kaɗa masa kurya gangar yaƙi. Sai dai ba irin tsimar jarumai yake yi ba, tsima ce ta jin tsoro da firgici.

Nan take ya tuna da fom ɗin da Ibrahim ya taɓa ba shi domin samun tagomashin daga bankin lamunin muhalli. Ya yi ajiyar zuciya mai cike da nadama. Babu shakka a lokacin da ya ba shi fom ɗin ya cike bai ɗauki batun da wani muhimmanci ba.

Ya dubi maigidansa ya ce,”lallai kam na tafka kuskure ga shi wankin hula ya kai ni dare. Ban gama ginin ba, ga ba kwanciyar hankali.” Ya sauke numfashi irin na ƙaƙa-ni-kayi.

Ibrahim ya ce, “baka makara ba har yanzu. Ka ci arzikin ana yankar maka 2.5% a albashinka duk wata. Wannan zai zamar maka kandagarki. Sannan kana da shekaru da yawa nan gaba kafin ka bar aiki. Sauran dabara ya ragewa mai shiga rijiya.”

Sammani ya ce, “yallaɓai wanne irin lamuni suke bayarwa ga jama'a?” Ibrahim ya ce, “da farko dai suna iya ba ka kuɗi ka gyara gidanka, ko kuwa idan kana da fili ka gina kayanka. Idan baka da waɗannan duka, za su iya ba ka gida sukutum ka zauna ciki kana biya sannu a hankali. Abin da za a riƙa cirewa daga albashinka bai taka kara ya karya ba. Ana iya rarraba kuɗin har tsawon shekara 30 yadda ba za ka jigata ba.”

Sammani ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana cewa, “yallaɓai bari na je ofis na dubo fom ɗin nan na cike yanzun nan.” Ibrahim ya bi shi da kallo yana murmushi ya ce, “ɗokin mazallaƙo ka manta ne an tashi daga aiki? Sannan kuma ai fom ba wahala yake ba, kana iya sauko da shi ta intanet daga shafin yanar gizo na FMBN, ko kuma ka je ofishin su baka shawara da sauran bayanai.”

Sammani ya koma ya zauna yana mai cewar, “Allah ya kai mu.”

*****

Dare mahutar bawa, amma wannan dare ga Sammani ya zama maƙirƙirar tunani. Tun da ya kwanta bai iya runtsawa ba, sai ya ƙulla ya kwance. Gani yake kamar gari ba zai waye ba balle ya je bankin FMBN ya karɓi fom.

Duk tsananin son da yake wa matarsa, amma ta haihu rikicin da ya same shi ya hana masa zarafin gudanar da hidimar suna kamar yadda ya tsara. Yana ji yana gani ko rago bai samu ya yanka ba. Zuciyarsa ta shiga zarginsa bisa yadda ma aka yi ya yi gini a unguwar Zurmawa.

“Tsautsayi ba ya wuce ranarsa, in ban da tsautsayi da ƙaddara me zai sa mutum ya yi gini a inda rayuwarsa za ta ƙuntata. Ga cututtuka ga ɓacin rai ga gulmace-gulmace....” Zuciyarsa ta yi ta ƙissima masa abubuwa barkatai har zuwa lokacin da gamzaki ya bayyana.

****

Asubancin Sammani zuwa bankin FMBN ya yi rana, domin kuwa shi ne na farkon da wani jami'i ya saurara a bankin.

“Za mu iya baka kuɗi har naira miliyan ɗaya domin ka gyara gidanka.” In ji jami'in banki. “Wannan shi ake kira 'Renovation Loan.’ Sannan muna da wanda ake kira 'Construction Loan', shi kuma zai ba ka dama ka gina gida a filin da ka mallaka muddin ka cika sharuɗɗan da aka gindaya. Za a iya ba ka har naira miliyan 15 gwargwadon yadda albashinka zai iya ɗauka domin ba za a iya yankar abinda ya wuce sulusin albashinka ba kuma biyan kada ya zarce shekaru talatin.”

Sammani ya ce, “ka ƙaddara ban mallaki fili ko taki ɗaya ba ballantana kuma gida. Wanne irin lamuni za a bani? Wanne agaji za ayi min?”

Jami'i ya ce, “muna da tsarin ɗan haya ya mallaki gida watau 'Rent to Own'. Za mu iya baka gida ginanne kana biyan aunaka har ka ida biya. Kuma muna da tsarin da ake kira 'Mortgage Loan'. Shi ma za a mallaka maka gida kana biya sannu a hankali amma sai ka bi ta ƙarƙashin wasu yardaddun kamfanoni da ake kira 'Mortgage Loan Orginator (MLO).' Ta hannunsu za ka samu gidan mu kuma za mu zama tamkar alƙalai tsakaninku.”

“Ranka ya daɗe, wanda ruwa ya ci ko takobi ka miƙa masa riƙewa yake. Duba min wanda ya fi dacewa da ni cikin tsarin 'Rent to Own' ko 'Mortgage Loan' ɗin nan.”

Jami'i ya yi nazarin takardun aikin Sammani da sauran bayanai sannan ya ba shi fom ya yi masa bayanin yadda za ya cike tare da takardun da ake buƙata.

“Ka haɗo da takardunka na ɗaukar aiki da na tabbatarwa da katin shaida da kuma bayanin asusun ajiyarka na banki da kuma lambar BVN. Har ila yau za ka je ma'aikatarku a ba ka takardar garantin za su riƙa yankar kuɗin aunaka daga albashinka suna aiko mana. Haka kuma za ka samu wasu ma'aikatan da za su tsaya maka.”

Sammani ya ji kamar ya daka tsalle don murna. Ya tafi ofis ya nunawa Ibrahim tare da duk abubuwan da ake buƙata.

“Ina fata idan al'amarin nan ya tabbata don Allah Sammani ka kula da gidanka da kyau. Duk wani gyara da ya taso ka daure ka yi. Ka tuna fa, muhalli shi ne tushen farin ciki. Haƙiƙa ma dai, muhalli shi ne tushen rayuwa, domin daga nan ne ake samar da iyali lafiyayyu da za su haifar wanzuwar zuriya ta gaba. Shi ya sa ma a Hadisi aka ambaci muhalli a matsayin ɗaya daga tubalan arziki.” Ibrahim ne ke yi wa Sammani nasiha bayan ya kammala duba takardun.

Sammani ya rusuna ya ce, “yallaɓai da yardar Allah zan kula sosai da dukkan iyawa ta.” Ya gyara zama ya ce, “ya zama wajibi gare ni na kula da muhallina, domin kuwa na ga illar gini a waje mara fasali. Ina ji ina gani aka yi min haihuwa amma ban iya zama na yi bikin suna cikin iyalina da 'yan uwa da abokaina ba. Ba domin taimakonku ba ma yallaɓai da yanzu labari ya sha bamban. Ai ni kam an sha ni na warke, ni da gini awon mai gona haihata - haihata.”

Ibrahim ya sauke numfashi ya ce, “Allah dai ya rufa asiri. Sai ka je ka yi himma ka harhaɗa abubuwan da ake buƙata domin ka samu da wuri.”

****

Unguwar Zurmawa ta amsa sunanta, domin kuwa ƙarfi da yaji gidajen sun zurma cikin lunguna. Babu wani layi wanda jama'a ke iya walwala cikinsa ballantana ababen hawa su samu matsuguni.

Rikicin mutanen unguwar da Alhaji Gambo ya sa gwamnati ta farka daga barcin da take yi dangane da fasalin unguwar. Jami'ai suka tafi gudanar da bincike kan yadda za a inganta muhallin domin unguwar ta samu ababen more rayuwa. Jami'an suka bayar da shawarar a rushe wasu gidaje domin samar da hanyoyin da za su iya ratsa unguwar domin inganta lafiya da tsaro.

Mutanen Zurmawa suka yi ta gudanar da tarurruka domin neman mafita. Cikin kowa ya ɗuri ruwa domin tsoron kada rusau ɗin ya faɗa gidansa. Sammani bai taɓa halartar ko taro sau ɗaya ba duk da kasancewarsa ɗaya daga jagororin mazauna unguwar. Ya maida hankalinsa kacokam wajen neman tabbatuwar samun mallakin gida daga bankin FMBN. Duk inda ya tsuguna zancen yake yi, kullum ya kwanta mafarkin da yake yi kenan. Lallai ruwa ya daki babban zakara.

Wata ranar Alhamis yana ofis yana ta fama da aiki sai ga saƙo ya shigo wayarsa. Bai tsaya dubawa ba sai da ya kammala abinda yake yi. Saƙon yana ɗauke da sunan FMBN. Cikin fafarniya ya duba. Saƙon na cewa, “muna taya ka murna. Ka samu lamunin gida mai ɗaki biyu a unguwa awon gwamnati. Maza ziyarci ofishinmu domin ƙarin bayani. Danna *219# daga wayarka domin sanin matsayin lamunin da aka baka.”

Sammani ya yi ihu kamar wani taɓaɓɓe. Ya ji kamar an yi masa ƙaimi, ya kasa zaune ya kasa tsaye. Ya yi ta zagayawa tsakanin 'yanuwa da abokan arziki yana shaida musu abin da ya same shi na farin ciki. Wasu kuma ya buga musu waya ya sanar da su. Nan take ya ji duk wani ƙunci da ke tauye masa walwala ya kau.

Danginsa da sauran 'yanuwa da abokan arziki aka yi ta zuwa ana taya shi murna. Maƙwabtansa na Zurmawa suka taya shi murna tare da fatan su ma kurtun sa'a ya fashe akansu yadda za su samu ikon barin unguwar nan mai kama da ƙuncin kurkuku.

Bayan wata uku - Ranar Litinin

'Mande tushen aiki ko nasara na tsoronki.Wannan ne kirarin da ake yi wa ranar Litinin domin ita ce rana ta farkon zuwa wuraren aikin gwamnati bayan an shafe ranakun Asabar da Lahadi ana hutun ƙarshen mako. Ga Sammani kuwa wannan Litinin ɗin ta zama ta farkon komawa ofis tun bayan da ya tare a sabon gidansa.

Bayan an danƙa masa mukullan gida bai yi wata-wata ya haɗa nasa ya nasa daga Unguwar Zurmawa ya koma sabon gidansa. An yi dace kuma, lokacin ya zo daidai da zai soma gudanar da hutun shekara. Wannan ya ba shi dama ya sakata ya wala.

Gidan dai fasalin ginin da ake kira 'bungalow ne, ya ƙunshi ɗakunan kwana biyu da babban falo da kuma kicin da banɗakuna biyu. Akwai wadatacciyar haraba da aka kewaye da ƙaramar katanga inda aka dasa bishiyoyi gajejjeru masu bada iska yalwatacciya da ke bugawa cikin gidan. Duk wanda ya je ganin gidan sai ya yi marmarin mallakar irinsa.

Arziki kamar jiran Sammani yake a sabon gida. Cikin ƙanƙanin lokaci ya sake babur ɗinsa da ya tsufa, kuma ya sayo ƙaton rago biyan bashin sunan ɗansa wanda ya ci sunan mahaifinsa watau Bashir. Ana kiransa Abbaji.

Ya yin da yake kan hanyarsa ta zuwa ofis, sai ya ji shi kamar sabon ango. Tafiya yake cikin nishaɗi da annashuwa. Gani yake duk duniya babu wanda ya kai shi sakewa da jin daɗi.

Duk unguwar da ya wuce sai ya tsaya ya yi nazarin layukansu da irin fasalin da suka yi wajen gini. Cikin zuciyarsa yakan yanke hukuncin irin jin daɗin da mazaunan ke yi. Zuciyarsa na shaida masa cewar, duk wanda bai mallaki muhalli a wuri mai kyakkyawan fasali ba yana da sauran aiki gabansa.

Ya yin da ya isa ofis, tun daga nesa maigadi ya hango shi. Ya taso da hanzari yana yi masa gaisuwar yaushe gamo yana cewa, “ni na fara ganinka. Lallai Sammani ka samu duniya a daidai. Hutun nan ya yi maka kyau. Fes da kai. Ga sabon gida, ga sabon babur ga kuma sabuwar duniya. Allah ya ba mu i-taku.”

Sammani cikin jin daɗi ya sa hannu ya fito da kuɗi ya danƙa masa ya ce, “riƙi wannan ka sha ruwa.” Maigadi ya hau godiya yana cewa, “na gode ƙwarai yalllaɓai. Allah ya sa ka fi haka. Duk wanda ya raina arzikinka, ya Allah ka yi masa mutuwa irin ta shaddar talaka.” Sammani ya fashe da dariya ya wuce zuwa ofishinsa.

Da yamma, ya koma gida kenan, sai aka aiko ana sallama da shi. Ya yin da ya fita sai ya ga ashe mutanen unguwar Zurmawa ne, ciki har da Liman da Dogo wanda ya samu kansa da ƙyar daga kamfaninsu.

Bayan an yi raha da gaisuwa irin ta yaushe-gamo sai Liman ya soma cewa, “Malam Sammani, mu wakilai ne aka aiko musamman domin neman alfarmarka.”

Sammani ya gyara zama ya ce, “ina sauraro.” Liman ya cigaba da cewa, “kana sane da dukkan balahirar da ta auku a unguwarmu ta Zurmawa. To yanzu haka dai gwamnati ta aiwatar da shawarwarin rahoton kwamitin nan na kwanaki. An rushe gidaje da dama hatta shi kansa ginin nan na Alhaji Gambo bai tsira ba, an rushe fiye da rabinsa domin samar da hanya mai inganci da kuma tsaron unguwar.

“Don haka sai mu duka mazauna unguwar muka tattauna tsakaninmu sannan muka miƙa ƙoƙon bara ga gwamnati kan ta yi mana agajin ginin asibiti. Gwamnatin ta bamu damar mu lalubo duk wurin da muke so a yi mana wannan aiki. Da taimakon jami'an safiyo muka zaɓi rukunin gidaje shida da za a haɗe a samar da asibitin.

Kwamitin ya tuntuɓi mutane biyar ɗin har da Dogo maƙwabcinka ga shi a zaune. Kuma duk sun amince za su sayar da gidajen nasu. Kai ne kaɗai ka rage ba a tuntuɓa ba da yake yanzu baka unguwar. Shi ya sa aka wakilto mu domin neman alfarmar ka sayar wa mutanen unguwa gidanka da za a mayar asibiti.”

Sammani ya nutsu yana sauraren Liman har ya ƙare jawabinsa sannan ya ce, “kasancewa ta mutumin da ya zauna a Zurmawa kuma na yi gwagwarmaya domin cigaban ta, to duk abin da ya taso na bunƙasar unguwar zan yi maraba da shi. Don haka, ni Sammani Bashir, na mallakawa mutanen unguwar Zurmawa gidana da ke turba, domin samar da asibiti. “

Yana rufe baki wakilai suka hau sowa da kabbara suna gode masa bisa wannan namijin tagomashin da ya yi musu. Sammani na wangale baki cikin fara'a ya yin da suke sa masa albarka shi kuma yana cewa, “ba ni za ku godewa ba, ku godewa Allah da bankin FMBN da suka mutunta ni suka maida ni ɗan adam bayan na maida kaina tamkar muzuru.”

Liman ya ce, “haka fa, to su ma bankin Allah ya ƙarfafe su bisa aniyarsu ta alheri da taimakon da suke yiwa talakawa samun ingantaccen muhalli.”

Wakilai gaba ɗaya suka amsa da “amin, amin.”

Ƙarshe

Muhalli, Sutura

Post a Comment

0 Comments