Aliyu Rabe Aliyu (2020). Sanin Hanya. Muhalli, Sutura (Labaran Da Suka Samu Nasara a Gasar Gajerun Labarai a Kan Muhalli Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2020). Darma Digital Prints.
SANIN HANYA
Na
Aliyu Rabe Aliyu
A zamuna da yawa da
suka wuce, da yawa ba a da masaniya a kan yadda al’amurra suke tafiya, wannan
bai rasa nasaba da yadda ake rufa-rufa a kan ayyukan gwamnati musamman a
ma’aikatu da sassansu, wannan ya sa da yawa daga cikin Mutane ko ma’aikata suke
yin fargar jaji a duk sanda suka zo gabar ajiye aiki musamman rashin samun
muhalli da zasu mike kafafuwansu a duk sanda suka kammala aiki..Sai dai sarki
goma zamani goma; juyi-juyin siya sa da kuma sanya ƙwararru akan hukumomi da
sassansu ya kawo wata sabuwar rayuwa in da ƙananan ma’aikata ma suke rabauta da
ayyukan gwamnati tun a matakin farko ta hanyar bayar da dama ga dukkan wanda
yake da buƙata ya amfana ba tare da banbancin siya sa ko aiki ba; wannan kuma
bai rasa nasaba da yadda ake tafiyar da abubuwa a buɗe da kuma gangamin wayar
da kan al’umma a kan shirye-shirye da ayyuka na gwamnati mai ci a yanzu abin da
masana da ƙwararru suke da yakini cewa wannan itace babbar hanyar da zata
magance cin hanci da rashawa da kuma gina al’umma ta hanyar da ya dace.
FARKO
A duk sanda aka ce safiyar litinin ce, zaka samu babban titin Ahmadu Bello
da ke Abuja motoci ne ke zirga zirga , wannan bai rasa nasaba da yadda yake ɗauke
da manyan ma’aikatu na gwamnati, ciki har da ma’aikatar ilimi wadda take da
gurbi a cibiyar ma’aikatun gwamnatin tarayya.
Zubairu Ɗanmalam ya fito daga cikin motarsa Toyoto Lexus wadda kuɗinta ya
kai naira miliyan sha-takwas, rike da yar jika ya hau sama zuwa ofishinsa da ke
hawa na biyar.
Matsayin Zubairu shi ne mataimakin darektan ilimi, a yanzu shekara ɗaya ta
rage masa ya yi ritaya, kuma wannan ce shekara ta biyu da dawowarsa Abuja bayan
yi masa sauyin wurin aiki daga kwalejin gwamnatin tarayya da ke Zaria. In da ya baro can
a matsayin shugaban makarantar watau principal.
Kusan rayuwar Malam Zubairu ya yi ta ne a ire iren waɗannan makarantu na
gwamnatin tarayya tun daga matsayin malamin makaranta har zuwa yau da yake a
cibiya inda yake ƙoƙarin yin ritaya a matsayin mataimakin darektan ilimi.
To sai dai wani hanzari ba gudu ba idan akwai abin da yake tada wa Zubairu
hankali a rayuwarsa ita ce yadda ya kwashe shekaru 34 yana aiki amma har yanzu
bashi da gida mallakar kansa, wannan bai rasa nasaba da dalilai guda biyu;
Na farko duk tsawon rayuwarsa a wuraren da ya yi aiki a kusan jihohi guda
takwas yana zama ne a cikin gidajen malaman makaranta da shi da iyalinsa;
Na biyu kuma bai taɓa yin wani tanadi na aje isassun kuɗaɗe domin mallakar
muhalli akalla koda fili ne a garinsu na asali watau Gashua ko kuma a garuruwan
da ya yi zaman aiki, wannan shi ma ba ya rasa nasaba da irin salon rayuwarsa ta
son kawa da burge mutane da sharholiya da kuma rashin sanin ya kamata.
Ko a yanzu zaman da yake yi a Abuja dankareren gida ne ya sa aka kama masa
ya biya naira miliyan shida domin yin wa’adin shekara biyu a ciki, kaga kenan
naira miliyan uku kenan duk shekara.
Ga mota mai tsada, ga gidan haya mai tsada, ga kuma lokacin ritaya ya
matso. Sai yanzu ne Zubairu ya fara tunanin yadda rayuwar shi za ta kasance
idan har ya yi ritaya, na farko ma bai san inda zai koma ba, saboda a garinsu
na asali baya da gida, sannan matan shi guda biyu da yara guda shida, rayuwar
birni suka saba da ita; kuma dukkansu a gida suke zaune in banda babban dansa
Mutari wanda yake ya yi digiri kuma har ya samu aiki a hukumar kamfanin
dillancin labarai na najeriya watu NAN.
Lokacin da yake a FGC Kano ya taɓa cin bashin banki da niyar ya sayi gida,
daga baya kuma sai ya fasa inda ya kara aure kuma ya sayi sabuwar mota marsandi
ya ci gaba da fantamawarsa.
A Zaria ne ya samu makudan kuɗaɗe sakamakon kasancewarsa shugaban
makarantar kuma a wancan lokacin aljihun gwamnati a bude yake duk wata
almundahana ba wanda ya damu da sa ido a kanta, wannan ya sa Zubairu ya yi
tsayin daka wajen azurta kanshi ba tare da ya yi la’akari da mallakar gida ko
muhalli a can ba, sai kawai ya yi kundunbala ya sayi mota Toyota Lexus abin da
ya janyo masa hayaniya da sa ido wanda shi ne sanadiyar dawo da shi Abuja
cibiyar ilimi ta ƙasa don kamala aikinsa anan.
A daidai wannan lokacin ne kuma ɗansa Mutari yake cika shekara uku da fara
aikin gwamnatin tarayya kuma ya rage wata uku kenan za a ɗaura masa aure da
wata yarinya a Minna ta jihar Niger inda a can ne yake aikin aiko da labarai ga
kamfanin dillancin labarai na najeriya watau NAN.
Bayan zaman sa a ofis Zubairu ya ɗauki waya ya tuntubi ɗansa Mutari akan ko
ina aka kwana akan maganar bukinsa, da kuma inda zai zauna da matarsa bayan ɗaurin
aure.
Sai dai sabanin Zubairu, ɗansa Mutari yana da taka tsantsan da kuma lura da
yadda rayuwa ta canja, sannan yana jin ciwo a duk sanda suka je Gashua sallah
da Babansa da yan gidansu sai suyi ta raɓe- raɓe na wurin da za su zauna, wani
lokaci a gidan kakanninsu suke kwana, wani lokaci a gidan kawunsu, wannan ya sa
a kodayaushe yake jan hankalin Babansa cewa ya kamata ya yi kokari ya mallaki
muhalli a kalla koda na fita kunya ne a garinsu don kaucewa shiga matsala a
rayuwa musamman ma idan aka ce yau ya yi ritaya.
Wannan ne ya sa daga lokacin da Mutari ya fara aiki da NAN a shekarar 2016,
ya fara tsimi da tanadi akan yadda zai mallaki muhalli nashi.
A wani lokaci ya je ɗaukar rahoto a kan wata yarjejeniya da aka kulla da
bankin bayar da lamunin gidaje na ƙasa da kuma kungiyar Ƙwadago ta Jihar Niger,
akan wani shirin samar da gidaje ga ma’aikatan jihar, wannan ya ba Mutari damar
yin bincike da kuma tuntuɓar jami’ai na bankin inda suka bashi isassun bayanai
da hanyoyin da zai bi wajen cin gajiyar shirin bankin akan samar da gidajen
ma’aikata.
Tun daga wancan lokacin yake kwanci tashi har sai da ya cika sharuɗɗa na
mallakar muhalli wanda yake cikin rukunin gidaje da bankin ya gina a shiyar da
zummar tallafama al’umma mallakar muhalli cikin sauki da kuma rangwame.
A daidai lokacin da Mutari yake yi wa mahaifinsa bayani cewa ya mallaki
gida ba ƙaramin kaduwa uban ya yi ba yana nazari ta yaya a wannan karon yaron
zamani ya fi dattijo kyakkyawan tunani irin haka? Ta yaya haka ta kasance?
Yanzu kuma mine ne makomarsa nan gaba idan ya yi ritaya da mata biyu da yara
guda shida? Ina
zai sa gaba? Wane irin barcin kwalwa ne ya yi a tsawon shekara 34 yana aiki bai
tsinana komai ba??? Tunaninsa ya katse a daidai lokacin yaji ɗansa
yace ”Baba kai ma
baka Makara ba zan bincika maka
yadda zaka mallaki gida a ko’ina ne a Najeriya”
TA WACE HANYA CE MUTARI ??? Uban Ya Tambaya
cikin ɗoki a lokaci ɗaya kuma yana tunanin kamar abin ba zai taba yiwa ba.
“Ka kwantar da hankalin Baba akwai gidaje da bankin bayar da lamunin gidaje
na kasa da ya gina ta hanyar haɗaka da wasu masu harkar gine gine a wasu
jihohin kasar nan kuma tabbas gidajen nan an kamala su har ma an fara amfani da
su a wasu jihohin ƙasar nan don haka zan bincika maka don ganin cewa kaima ka
mallaki gida a yan kwanakin ka na kamala aiki, kuma zan tabbatar da cewa gurin
ka ya cika na shiga sabuwar rayuwa da ƙafar dama” cewar Mutari.
* * *
Babban ɗakin taro ne mai ɗaukar mutane aƙalla ɗari biyu, kowanne mutum daga
cikin mahalarta taron ya yi ƙasake yana sauraron mukalar da Farfesa Yakmut
Bahago yake gabatarwa akan yadda rayuwa zata kasance ga waɗanda suke gab da yin
ritaya kuma ake musu bita akan yadda za su wanye lafiya a rayuwarsu bayan
kammala aikin gwamnati.
Duk da cewa abin da Farfesa Yakmut yake faɗa a muƙalarsa a matsayinsa na
masanin tattalin arziki da zamantakewa abu ne da yake zurfafa bincike kafin ya
gabatar da ita a duk wani taro da aka gayyace shi, yakan yi kokari ya fitar da
wasu mas’aloli waɗanda galibi ba kowanne masani yake da irin wannan gwaninitar
ba, a don haka a duk sanda yake gabatar da bita zaka samu kowa ya nutsu yana
sauararon ilimi mai cike da basira da kuma ratsa zukatan masu sauraro.
A wannan karon bitarsa ta ta’alaƙƙa ne akan tsallen baɗake da ma’aikata
suke yi a duk sanda suka fuskanci lokacin ritaya ta hanyar yaki haram-yaki-
halak.
“ bincike na baya-bayanan ya nuna cewa kashi sittin cikin ɗari na waɗanda
ke yin almundahana da babakere da ruf da ciki na kuɗaɗen ma’aikatu zaka samu
masu shirin yin ritaya ne waɗanda galibi suka yi baccin ƙwalwa tun farkon fara
aikin su ba su yi kokarin mallakar muhalli ba, sai a dadai lokacin da ritaya ta
riske su sannan za su yi abin da ake cewa fargar-jaji”
Zubairu wanda yake cikin waɗannan mutane yaji gaban shi ya faɗi ba shakka
wannan kamar wani shagube ne Farfesa yake yi a cikin wannan taro domin yana ɗaya
daga cikin wanda ya tsinci kansa a wannan rukunin mutane masu fafutakar muhalli
a ƙurarren lokaci.................... maganar Farfesa ce ta katse tunanin da
yake yi.
“ rashin mallakar muhalli ga mutumin da yake gaɓar ritaya yana da ƙalubale
mai yawa ga al’umma, kamar yadda na faɗa muku shi ne ummul aba’isin cin hanci
da rashawa a ma’aikatu, sannan yana kawo durƙushewar ayyukan gwamnati, sannan
kuma yana haddasa ruɗani ga iyalan mutum, baya ga haka kuma akwai rashin tabbas
ga rayuwar yaranka nan gaba saboda ba su da wata sahihiyar makoma”
Tabɗi! Zubairu ya faɗa tare da gyara zama
Farfesa Yakmut ya ci gaba da cewa “ abin takaici a nan shi ne zaka samu
mutum ya yi ritaya a matsayin darakta ko mataimakin darekta ko wani babban
jami’i na gwamnati amma wata ɗaya da yin ritaya sai ka samu ya fara lalacewa
yana ramewa sai yawan zuwa asibiti, hawan jini, cututtuka na zahiri da na ɓoye,
sai ƙorafe-ƙorafe shin kun san babban dalilin wannan ciwo? Rashin samun muhalli
ne da kuma yankewar kuɗaɗen cuwa-cuwa da ya saba samu, ga kuma batun kuɗaɗen
haya, dana ɗawainiyar iyali ga kuma rashin sanin makoma ta yaya mutum ba zai
kasance ba a cikin larurar da bata da magani har tsawon rayuwarshi? kai in
takaice muku wani lokaci idan kun ga mutum farat ɗaya ya yanke jiki ya faɗi
sumammme ko matacce duk bai rasa nasaba da abin da muke magana a kai na rashin
muhalli”
“Wannan ya sa a yanzu na yi nazari akan samar muku da mafita ta yadda waɗannan
ƙalubale za su zo muku da sauki amma kafin nan zamu je hutun ɗan takaitaccen
lokaci”
Raf-raf-raf-raf-raf............. sai tafi abin da yaba Farfesa Yakmut
dariya saboda sai a yanzu ne aka yi masa tafi don sun ji cewa zai kawo musu
mafita a rayuwar da suke taraddadin shigarta.
* * * *
Kusan kowa daga cikin mahalarta taron bitar masu ritaya a shekarar nan ya
yi kasake yana sauraron Farfesa yakmut akan yadda za su gama aiki lafiya, kowa
da abin rubutu ya yin da wasu kuma suka kunna wayoyinsu domin ɗaukar bayanan da
ake don adanawa, ga mamakinsu sai suka ji Farfesa ya furta wata magana ta
hanyar tambaya; Shin ko kun san cewa sabbin Ma’aikata da aka ɗauka daga
shekarar 2015 zuwa yanzu za su fi ku jin daɗin rayuwa a nan gaba? Shin ko kun
san cewa a yanzu an sami gagarumin ci gaba wajen baiwa al’umma damar amfana da
shirye shirye ko ayyuka na gwamnati? Shin kuna da labarin cewa ƙananan
ma’aikata yan shekara uku da fara aiki sun fara mallakar muhalli ya yin da
wasun ku a yanzu shekaru 35 da fara aiki amma basu da ko fili
mallakarsu?..........; saurara yallaɓai….. “gaskiya ba mu ce ba haka ne ba;
amma zai yi wuya ma’aikaci a mataki na takwas ko tara ya mallaki gida; mun san
yadda aikin gwamnati yake kwarai, kuma duk salon tsarin aiki da zasu bi mun bi
amma ga halin da zamu kare aiki” malam Bala Jogana kenan ya katse hanzarin Farfesa
wanda yake ta warwarar bayani akan yadda ma’aikata na wannan zamani suka fara
samun ribar aiki a kuruciyarsu.
“ Farfesa duk tsarin da ya kamata mubi na samun muhalli mun shiga, kuma tun
1983 aka fara cire mana kuɗaɗen mallakar gidaje (NHF), sannan tsawon lokaci
babu wata amsa dangane da kuɗaɗenmu da aka rika cirewa a baya tun lokacin ana
yi da hannu, aka zo sabon tsari a 2010 sannan ne ma muka fara sanin inda kuɗaɗenmu
suke shiga ta hanyar komawa manhajar zamani ta bankin gidaje, kuma daga nan
babu wata dama ko gina gidaje ko bashi ko tallafi, sai dai jefi-jefi, yanzu ne
muka fara ganin cewa al’amurra sun fara canjawa dangane da batun mallakar
muhalli a ƙasar nan …………” “dakata malam, duk na fahimce ka” Farfesa Yakmut ya
katse hanzarin Bala Jogana fitaccen malamin makaranta kuma ɗan gwagwarmaya mai
akida.
“ ai abin da na faɗa ne ɗazu cewa ma’aikatan yanzu za su fi ku rayuwa
ingattacciya saboda sun riski zamani da ake yin komai a buɗe, a cikin ƙa’ida da
kuma sanin yakamata, na gaya muku cewa daga 2015-2020 an samu ci gaba sosai a
wannan ɓangare na kyautatatawa ma’aikata da ba su haƙƙoƙinsu ta hanyar ba
kowacce hukuma cin gashin kanta. Wannan ya sa ma’aikata a yanzu kai tsaye suke
amfana da ayyuka ko manufofin gwamnati, kuma hakan ya faru ne dalilin ba kowa
da kowa damar amfana da abubuwan da ake samarwa ga al’umma”.
Farfesa Yakmut ya ci gaba da cewa; “dalili na biyu kuma shi ne akwai
gangamin wayar da kan al’umma da ma’aikatan wannan lokaci suka samu ta fuskoki
da dama wannan ya hada da yawaitar kafofin yada labarai, da hanyoyin sadarwa na
zamani, kana kuma wadannan hukumomi kamar bankin bayar da lamunin gidaje, da
ma’aikatar ayyuka da gidaje da makamantansu kaitsaye suke ɗora ayyukansu da
shirye-shiryensu akan dandalin shafinsu na yanar gizo”
“ haka kuma akwai fahimtar juna a tsakaninsu da sauran hukumomi takwaransu
da ƙungiyoyin ƙwadago da kuma ɗai-ɗaikun mutane da yan kasuwa masu zaman kansu,
uwa uba kuma batun yaƙi da cin hanci da gwamnati mai ci yanzu take yi na ba
sani ba sabo ga dukkan wanda yaci amanar kasa wannan ya sa ma’aikatu da
hukumominsu suke taka tsan-tsan wajen yin abin da ya dace”.
Idan kowa a cikin wannan ɗakin taro bai yarda da mukalar da Farfesa Yakmut
yake gabatarwa ba, to ban da Zubairu Ɗanmalam, mataimakin darektan ilimi mai
gab da yin ritaya wanda a zuciyarsa ya gasgata dukkan abin da Farfesa ya faɗa
domin shekara 34 ya yi yana aiki amma bai tanadi komai ba dangane da muhalli
kuma wannan ba matsalar kowa bace, laifinsa ne domin ya sami dama iri-iri a
rayuwarshi amma ya yi sakaci da ita ƙarshe kuma yanzu yake ta fafutukar yadda
zai kasance a cikin muhalli bayan ya yi ritaya. A nan ne kuma ya tuno da yadda ɗansa
Muntari ya mallaki gida shekaru uku da fara aikin sa a kamfanin dillancin
labarai na Nijeriya.
* * * *
Wata huɗu kenan da yin ritayar Zubairu Danmalam, kuma yana zaune ne a ɗaya
daga cikin sabbin gidajen da bankin bayar da lamunin gidaje ya gina a gundumar
Tamburawa dake birnin Kano,
Ya zabi birnin Kano ne domin yaci gaba da tafiyar da sabuwar rayuwa bayan
ajje aiki a watan maris da ya gabata.
Saboda a duk wuraren da ya yi aiki ya fi sabawa da Kano, sannan yana son ya
fara kasuwanci, kana kuma ba za ya ji daɗin zama a Gashuwa ba mahaifarsa,
saboda ba kasafai yake zuwa can ba tun ma a lokacin da yake aiki, don haka Kano
nan ne wurin da ya ga ya dace ya ci gaba da rayuwarshi domin kasuwanci da kuma
sanya yaransa a makarantun gaba da sikandire.
Zubairu bai taɓa tsammanin zai mallaki gida ba, amma sai ga shi yanzu ya
mallaki gida cikin ƙanƙanen lokaci, kuma nagartaccen gida, ginin zamani a cikin
rukunin unguwa sabuwar ya yi da ke Tamburawa.
Kasancewar Mutari ɗa ne mai hazaƙa, mai bibiyar ayyukan bankin bayar da
lamunin mallakar gidaje, wannan ya bashi damar sanin aikace-aikacen bankin
wanda hakan ne ya sa shima ya rabauta da mallakar gida a tsarin ayyukan bankin,
sai dai duk da haka ya yi ta faɗaɗawa wajen bincike da samun ƙarin bayanai a kan
yadda ya kamata ace wanda ba ma’aikacin gwamnati ba, da ɗan-kasuwa da masu
zaman kansu sun amfana da ayyukan bankin.
A ƙoƙarin wannan bincike da yake yi ne kuma bukatar mahaifinsa ta taso na
ganin ya mallaki gida a kan gabar ritaya. Duk binciken da Mutari ya gudanar bai
ga wata kafa da bankin ya yi tanadi ga masu ritaya ko yan fansho ba, amma a duk
sanda suka yi ritaya ana maida musu kuɗinsu ne na ajiya a yi sallama dasu. Don
haka, a nazari da tunanin Mutari ya san ko ba komai Babansa yana da kuɗi na
asusun gidaje (NHF) a bankin bayar da lamunin muhalli na ƙasa, sannan kuma
akwai kuɗaɗensa dake asusun ajiyar fansho, baya ga wannan kuma akwai yan kuɗaɗe
kusan miliyan huɗu a bankin da yake ajje kuɗi, kuma ga motar alfarma ta miliyan
sha takwas yana hawa, don haka duk yadda za’a yi a wannan da’irar ne ya kamata
a ce kuɗin muhalli sun fito don ganin cewa mahaifinsa ya shiga gida mallakar
kansa.
Da farko ya tuntuɓi mahaifinsa da shawarar sayar da motar alfarma ta Toyota
Lexus, sannan kuma ya bukace shi inda yake so ya zauna bayan ya yi ritaya, da
kuma salon rayuwar da za ya yi nan gaba, wannan tunani na Mutari ya yi mawafaƙa
da shawarwari da Farfesa Yakmut ya bayar a watan Junairun da ya gabata inda
yake shaida musu cewa a “ a duk sanda kiɗa ya canja rawa ma canjawa take” inda
ya basu shawarwari akan gudanar da rayuwa mafi sauki bayan ritaya, tare da
dakatar da duk wasu batutuwa da suke kawo kashe kudi da yawa, kamar amfani da
motocin alatu, tafiye tafiye da kuma yin rayuwa ta ƙarya ko kuma ta wuce gona
da iri, sannan kuma da kaucewa biyan kuɗin haya mai yawa tare da neman wuri ko
gari da suke da sauƙin rayuwa yana mai shaida musu cewa “kada ku manta a wannan
matakin babu albashi, babu alawus da yawa, babu damar handama da kuma samun
wani tallafi ko agaji daga ma’aikata ko wani abokin hulda, kuma kada ku manta a
wannan karon iyalinku ba su da tunanin cewa duk wannan damar ta kuɓuce muku;
tunaninsu shi ne kawai jiya ita ce yau”
A lokacin da Mutari ya zo wa da mahaifinsa da waɗannan shawarwari bai yi
wata ja-in-ja ba ya bashi dama ya yi duk abin da ya dace saboda ya san cewa
yaronsa yana da hankali sannan kuma ya goge a cikin ƙoƙarin samar da mafita a
dukkan wani sha’ani na rayuwa ta yau da kullum.
Da farko motar Toyota lexus ya kai wani kamfanin sayar da motoci a
Gwarimpa, inda aka yi kakara ya amshi karamar mota Toyota camry 2010 a naira
miliyan biyu suka bashi cikon naira miliyan sha biyu a hannunasa ya je ya saka
su asusun ajiyar bankin mahaifinsu kuma kuɗin dake ciki a ajiye dama Naira
miliyan huɗu ne, gaba ɗaya suka kama naira miliyan sha shida da yankai.
Daga nan ya bincika a asusun kuɗaɗen da ake cirewa na fansho dake IBTC a
nan ma kuɗaɗen da ake dasu sun kai miliyan sha takwas, duk da cewa akwai sauran
hanyoyi da ya kamata abi kafin a sami damar fito dasu. Sannan yaje ya duba
asusun ajiyar kuɗin mallakar gida nan ma naira miliyan biyu ne da yan kai.
A lokacin ne Mutari ya tuntubi jami’in hulda da jama’a na bankin lamunin
gidaje na ƙasa akan ko suna da muhallai na saidawa a jihar Kano? Domin nan ce jihar da mahaifinsu
ya zaba domin ci gaba da gudanar da rayuwarsa. A nan take jami’in hulɗa da jama’a na bankin bayar da lamunin gidaje ya tabbatar
masa da cewa akwai kuma an tallata su a shafin yanar gizo na bankin domin ba
kowa da kowa damar sayen gidan.
Ba tare da ɓata lokaci ba ya shiga shafin yanar gizo na bankin bayar da
lamunin gidaje inda ya ga gidaje da dama da aka tallata a shafin ciki kuwa har
da jihar kano, kuma kowanne fasalinsa da farashinsa.
Ba tare da ɓata lokaci ba ya yi nazarin bayanan da aka rubuta dangane da
gidajen da bankin ya gina a jihar kano a gundumar tamburawa tare da hadin gwiwa
da wani kamfanin gina gidaje na Almukab wanda suka gina da zummar samar da
nagartaccen muhalli da bunkasa walwalar birni bayan cunkoso da ƙwaryar kano
take fama da shi, sannan kuma su samar da wani tsari ta yadda zai karfafawa
masu son gina sabbin unguwanni ƙwarin gwiwa domin ganin cewa sun tashi daga
aƙidar awon igiya ya zuwa tsararrun unguwanni na faɗa a gani.
A lokacin da Mutari yake gudanar da bincike ya yi mamaki cewa guda hamsin
ne aka gina a kano sai dai mutane da dama musamman yan asalin birnin Kano ba su
mallaki gidajen ba kuma duk da farashi da rangwame da gidan yake da akwai da
kuma hawa hawa ne daga mai ɗaki hudu zuwa uku , zuwa ɗaki biyu, amma a binciken
Mutari ya gano cewa dama can ɗabi’ar wasu daga cikin mutanen yankin ba kasafai
suke son barin cikin birnin Kano ba har ma ya gano cewa, yawanci sabbin
unguwannin gefen Kano baƙi ne suka fara gina su kamar rijiyar zaki , janbulo,
kwandila da ire-irensu.
Amma kasancewar akwai ma’aikatan gwamnatin tarayya da suka fara sayen waɗannan
gidaje daga ciki har da ma’aikatan jinya daga asibitin malam Aminu Kano, da
kuma wasu daidaiku daga sauran ma’aikatu na gwamnatin tarayya.
Mutari Wanda ya yi la’akari da yawan iyalin mahaifinsa, da kuma gidan da ya
dace da shi inda ya zabi gida mai ɗaki huɗu wanda kuɗinsa ya kama naira miliyan
sha biyar. Duk da cewa akwai masu ɗakuna uku na naira miliyan sha biyu da kuma masu ɗaki biyu na naira miliyan tara, amma kasancewar zubairu Danmalam yana da mata biyu da yara gida mai ɗaki huɗu ne ya yi daidai da tsarin
iyalinsa, kuma haka aka yi ya tare a gidansa da iyalinsa da kuma motarsa ƙirar Toyota camry.
A cikin sauran kuɗin da ya rage masa ne ya yi ƙoƙarin mallakar gona a
ƙaramar hukumar Kura kasancewar gundumar Tamburawa tana kusa da kura wurin da
ya shahara da noman shinkafa da kayan lambu, duk fa wannan ci gaba da Zubairu Ɗanmalam
ya samu a ƙanƙanen lokaci ya faru ne ta sanadiyar ɗansa Mutari wanda yake
bibiyar abubuwan da suke faruwa a kodayaushe kuma yakan yi tsayin daka ya ga
cewa ya amfana kuma wani nashi ma ya amfana.
A yanzu abin da ya sa a gaba shi ne yadda zai shiga ya fita wajen ganin ya
taimaka wa mahaifinsa ya samu kuɗinsa na ritaya tare da shigar da shi a kan
tsarin masu amsar fansho a kan kari.
A wani lokaci ne za su tafi Abuja tare da mahaifinsa domin zuwa wajen
tantance waɗanda suka yi ritaya a farkon shekara , mahaifinsa yace su biya ta
Zaria domin gaisawa da wani tsohon abokinsa wanda ya yi ritaya a shekarar 2018
a matsayin baban jami’in mulki da walwalar ma’aikata a hukumar ƙidiya ta ƙasa.
Da farko dai Mutari ya yi zaton zai ga abokin mahaifinsa a wani katafaren
gida na alfarma, sai dai ga mamakinsa sai gashi a wata unguwa wadda an ɗauki
minti talatin ana ta waya a tsakanin juna kafin akai ga gano unguwar wadda take
cikin wani lungu mai sassarƙiya. Kusan tazarar mita 800 suka aje motarsu sannan
suka ƙarasa gidan a ƙasa.
Zubairu Danmalam tare da ɗansa Mutari sun yi mammaki yadda abokin
mahaifinsu ya kasance a cikin wannan wuri dama irin muhallin da yake ciki na
tsohon ginin tubali kuma duk an yi masa yar kwaskwarima da siminti sannan kuma
ga ƙunci a wurin daɗin daɗawa kuma a haka har kiwon dabbobi ake a wurin abin da
ya hadu ya zama wata kwamacala a wurin.
Bayan sun zauna ne an gama gaisawa Zubairu yake shaidawa abokin nasa Magaji
Maiburki cewa shi ma ya yi ritaya a yanzu haka ma akan hanyar zuwa tantancewa
suke a birnin tarayya Abuja.
Ba tare da ɓata lokaci ba Magaji maiburki ya yi maraba da zuwansu ”da farko
ina taya ka murnar kammala aiki lami lafiya, sai dai wani hanzari ba gudu ba,
ina jin tausayinka akan halin da zaka shiga a yanzu na rayuwa bayan ritaya,
bata da daɗi ko kaɗan, yanzu ne nike nadamar yadda aka yi na shiga aikin
gwamnati ba tare da na tsinkayi yadda rayuwa zata kasance a gaba ba, na farko
nan inda ka ganni gidan gado ne na amshi bangarena na gyara, na biyu ina da
fili a wajen gari amma har yau na kasa kewaye shi, sannan na uku larurori da
hayaniyar iyali da yan unguwa ta hana ni sakat, kusan kullum cikin masifa muke
ta ambaliyar ruwa, cakwali, kwalara da zazzazabin cizon sauro da makamantansu,
kuma babbar matsalar da nike fuskanta a yanzu ita ce yadda jama’a suke yin
yadda suka ga dama wajen zubar da shara a kan magudanar ruwa da kofar gida in
nayi magana sai a ce sanda nike da dama wace tsiya na yi wa al’ummar unguwar
don haka sai na kame baki na na yi shiru”
Malam Zubairu Ɗanmalam ya tausaya abokinnsa kan labarinsa da ya ji, a don
haka shi ma cikin ɗan ƙanƙanen lokaci ya sanar da abokin nasa yadda ɗansa
Mutari ya ceci rayuwarsa a daidai gaɓar da yake ritaya, kuma duk abubuwan da ya
mallaka ya mallake su ne a ƙanƙanin lokaci.
Magaji Maiburki ya yi wata ajiyar zuciya kana ya ce wa abokinsa Zubairu “ka
yi sa’a da ka sami yaro mai hankali mai tunani, kuma wannan bai rasa nasaba da yadda
suka zo a wani zamani da ake yin abubuwa a buɗe, sannan kuma bahaushe ya yi
gaskiya da yake cewa “sanin hanya ya fi sabko” domin ka ga su son zo a zamanin
da ake wayar da kan mutane a kan muhimmancin tsimi da tanadi, sannan dukkan
wani romon rayuwar duniya yana farawa ne daga Muhalli, mun yi sakaci da ba mu
maida hankali ba a farkon rayuwarmu wajen tanadi da kuma mayar da hankali a kan
abubuwan da ya kamata, kaga yanzu sai tunane tunane da yin da na sani, amma kai
kayi sa’a da ka farga a daidai lokacin da mu kuma muka yi fargar jaji”
* * * * *
Karshe
Mutanen biyu suka
taho zuwa wurin da su Mutari suka aje motarsu suna hira irin ta tsaffin abokai
duk da cewa kowannensu yana da yanayi na rayuwa da ya sa a gaba, amma idan ka
kalli nutsuwa da kuma salon tafiyar mutnen guda biyu zaka samu akwai banbanci
domin Zubairu Ɗanmalam fuskar shi tana annuri yana ta murmushi ya yin da Magaji
Maiburki zaka fahimci cewa a cikin taraddadi yake da tunzuri da kuma halin
neman taimako a kodayaushe.
A daidai lokacin da suke ƙoƙarin fitowa daga
lungun ne wani yaro ya taho da taya yana garawa kwatsam ta subuce masa sai
cikin kwata, a daidai lokacin da Magaji da Zubairu suna ƙoƙarin ƙetarawa kawai
sai ganin cabin kwata suka yi a rigunansu musamman ma Zubairu Danmalam wanda ya
sha farar babbar riga. Magaji Maiburki abin bai yi masa daɗi ba, yana ƙoƙarin
ya yi wa yaron tsawa sai Zubairu ya ce masa ai ba komai akwai ruwa a mota zamu
wanke kuma kada ka cewa yaron komai, domin a cikinsu kake da zama don ka da shi
da iyayensa su riƙa zautar da kai a irin wannan lokaci da kake buƙatar samun
nutsuwa.
Za su yi sallama ne a
bakin mota zubairu Ɗanmalam ya ɗauko naira dubu goma yaba Magaji Maiburki tare
da cewa” ga wannan ka sayi omo ka wanke wurin da Yaron nan ya ɓata ka da kwata”
Magaji ya yi tsaye Turus kamar wanda ruwa yaji, ya shiga wani dogon tunani na
daban....
Alhamdulillah
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.