𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam dan Allah a taimaka a yi min karin bayani yadda zan dinga sallah a zaune saboda ina fama da ciwo a kafana. Sannan kuma ina baran addu'a daga gareka da sauran 'yan uwa Musulmai Allah ya yayemin lalurar da nake fama da ita. Na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗
Wa'alaikumus salam
Warahmatallahi Wabarkatahu
Game da sallar mara
lafiya a zaune ya tabbata cikin hadisi Imrana dan Hussain (R.A) ya ce cutar
basir ta kasance agareni, sai na tambayi Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam sai ya ce kayi sallah a tsaye, kuma idan baka samu iko ba, to kayi a
zaune, kuma dai idan baka samu iko ba toh kayi a gefan jikinka (addini dan
sauki ke nan).
Haka dai shi Imrana
R.A ya kara cewa na tambayi Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam game da sallar
mutum Alhali yana zaune, sai yace: Wanda ya yi sallah a tsaye toh shi ya fi falala,
kuma wanda ya yi sallah a zaune toh yana da rabin ladan wanda ya yi ta a tsaye,
kuma dai wanda ya yi a kwance (awata ruwayar a kishingide) toh yana da rabin
ladan wanda ya yi ta a zaune (Abin nufi da shi wannan
hadisin) mara lafiya,
saboda hadisin Anas R.A: ya ce Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya fito
wata rana ya tarar da wasu mutane alhali su suna sallah a zaune saboda rashin
lafiya, sai yace: lalle sallar na zaune tana a bisa rabin sallar na tsaye.
Dole ne akan maras
lafiya ya yi sallah daidai iyawarsa, idan zai iya yin ta kamar yadda mai lafiya
zai iya to ya zama wajibi a kansa ya yi, in kuwa ba zai iya ba, to sai ya yi
yadda zai iya.
Wajibi ne akan maras
lafiya ya yi sallah a tsaye in zai iya tsayuwa, idan ba zai iya tsayawa ba, to
ya yi sallah a zaune, idan ba zai iya zama ba, to ya yi sallah a kwance akan
gefensa, fuskarsa tana fuskantar alƙibla, idan ba zai iya
kwance akan gefe ba, to ya yi a rigingine, ƙafafunsa suna
fuskantar alƙibla in zai iya, in kuwa ba zai iya ba, to ya yi a
gwargwadon halinsa.
Dalili kuwa shi ne
abin ya gabata na faɗin Allah:
فَاتَّقُوا
اللَّهَ مَا اسْتَطَعْتُمْ
“Ku ji tsoron Allah iya iyawarku” (Attagabun:
16).
WASU DAGA
HUKUNCE-HUKUNCEN SALLAR MARAS LAFIYA:
1. Idan maras lafiya
yana Sallah a zaune, amma zai iya yin sujjada, to sujjada ta wajaba a kansa.
2. Idan kuwa yana
sallah a zaune, amma ya kasa yin sujjada, to ya yi nuni da jikinsa a ruku’u da
sujjada, sujjadarsa tafi ruku’unsa ƙasa-ƙasa, idan nuni da
jikinsa zai masa wahala, to sai ya yi da kansa, haka ma zai yi idan ya yi
Sallah a rigingine, zai yi nuni da kansa.
3. Idan yin alwala a
kowace sallah zai yi wa maras lafiya wahala, ko kuma yin salloli a kan
lokacinsu zai masa wahala, to yana iya haɗa sallar azzahar da la’asar, magariba da
isha, a lokacin ɗaya daga cikinsu, ko
dai a lokacin ta farkon ko ta biyun, gwargwadon yadda ya fi masa sauƙi.
4. Sallah ba ta saraya
daga kan maras lafiya matuƙar yana cikin hankalinsa, saboda haka
bai dace ga maras lafiya ya yi sakaci da sallah ba, don da’awar bashi da
lafiya, don haka ya yi iyakar ƙoƙarinsa wajen yin
sallah.
5. Idan maras lafiya
yana suma tsawon wasu kwanaki sannan ya farfaɗo, to zai yi sallah ne a lokacin da ya
farfaɗo gwargwadon yadda
zai iya, kuma ba zai rama sallolin da suka wuce shi ba a lokacin sumansa, amma
idan suman kaɗan ne, na yini ɗaya ne ko kwana biyu,
to wajibi ne a kansa ya rama sallolin da suka wuce shi, a duk lokacin da hakan
ya sauwaƙa a gare shi.
Wallahi yan'uwa
mugodewa Allah swt kuma mu yi amfani da lafiyar da Allah yabamu mu bauta masa
yadda ya kamata..Allah kabamu ikon bauta maka yadda kakeso. kuma dan ALLAH
aringa share domin wasu su amfana.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.