Rabiatu Sani Katibu Mashi (2023). Alhaki Kwkuyo.... Ɗaukar Jinka (Labaran Da Suka Samu Nasara A Gasar Gajerun Labarai Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2022). Kangiwa Multimedia and Communication Company LTD
ALHAKI
KWIKUYO...
Na
Rabiatu
Sani Katibu Mashi
“Ƙi!!!!” Ya tsayar da motar da sauri,
matar da take baya ta buɗe ƙofar ta fito tun kafin motar ta ƙarasa tsayawa.
“Malam
Adamu fito ka taya ni korar yarannan.”
Ta
fara kutsawa cikin dandazon yaran da suke tafe sun zagaye matashin mahaukacin
cikin nishaɗi suna tafa hannu suke faɗin,
“Baban
bola!Baban Bola!!”
Wasu
daga cikinsu har suna ja masa riga. Malam Adamu ne ya kore su da icen da yake hannunsa duk suka watse,
dattijuwar ta ja hannun matashin zuwa wani dakali da ya ke kusa da wurin.
Duk da kasancewar lokacin zafi ne, sai da matashin ya
takure a wuri ɗaya jikinsa ya na ta kyarma kamar mai jin sanyi, sai
zazzaro ido yake.Ta ɗago fuskarta da ta gama cika da ƙwalla cikin tausayi ta ce.
“Allah Ya saka maka Auwal, matarnan ta cucemu, sai da
tayi nasarar korar ka daga gidanmu bayan ta haɗa ka da mahaifinku,
inshaa Allah duk ƙullin da ta yi kan ‘ya’yanta zai koma, sai
na shiga, na fita, koda abinda na mallaka zai ƙare, sai na tabbatar ta wulaƙanta kamar yadda ta yi maka.”
Dai dai lokacin Malam Adamu ya iso wurin riƙe da kwandon da aka jera kayan abinci a cikin, girgiza
kai kawai yayi saboda ya ɗan tsinci wani abu daga maganganunta.
Ya rasa dalilin da yasa har yanzu Hajiya ta ƙi yarda da ba wani ne ya yi wa ɗanta asiri ba, ta
gane laifinsu na gudummuwar da suka bayar wurin lalata rayuwar yaronsu.
“Ka
yi mini tsaye a wurin, ko abincin shi ne zai ajiye kansa?”
Da
sauri ya durƙusa
ya ajiye bayan ya dawo daga tunanin da ya
tafi.
Haɗa
lafiyayyen abincin ta shiga yi, da kanta take ba wa Auwal a baki, sai da ta
tabbatar ya ƙoshi, sannan ta kira
Malam Adamu ya tattara kayan ta miƙe
zata tafi.
“Umma!”
Karo na farko kenan da ya yi magana tun zuwansu wurinsa,
dakatawa tayi ba tare da ta juya ba, jakarta ta buɗe sai da ta
tabbatar ya kwashe kuɗin da ke ciki gabaɗaya sannan ta rufe jakar, ta yi haka
ne saboda ikirarin da mahaifinsa ya yi na idan har ta sake bashi kuɗi, a bakin aurenta.
‘Oho
dai! Wannan ai ba Ni na ba shi ba, ɗauka
ya yi.’Ta faɗa a zuciyarta sannan ta yi gaba.
Sai
da ta shiga mota har Malam Adamu ya tayar, sannan ta juya kallon in da yake,
har ya tashi ya ci gaba da ‘yan tsince-tsincen shi.
Bayan
sun ɗauki
hanya, Malam Adamu ya nisa cikin nutsuwa ya fara magana.
“Hajiya
ina tausayin yaronnan, ya na
matuƙar buƙatar
taimako”
“Kana
tunanin ka fini sani ne? Kana gani ai an hana mahaifinsa ya taimaka masa, nima
yana nema ya hanani taimaka masa, sai a ɓoye
nake zuwa wurin malamai nema masa taimako.”
“Hajiya
amma sai nake ganin kamar matsalar yaronnan bata Malamai ba ce, wurin da aka tanada don masu matsala irin
tasa ya kamata a kaishi, a hankali za ki
ga yana samun sauƙi
har ya warke ya koma kamar da.”
“Matsala
irin ta shaye-shaye kake nufi wai? To ka sani ni babu inda zan kai ɗana
a takura rayuwarsa, bayan nasan abin da
ke damunsa. Malamai sun fi
bakwai suka faɗa min wannan
baƙar matar ce tayi asiri yarona ya fara
shaye-shaye, ana gama masa magani na san
komai zai bari ya dawo kamar kowa.”
Malam
Adamu ya buɗe baki zai yi magana, ta dakatar da shi
ta hanyar ɗaga masa hannu.
“Wannan
matsalar da ta shafi iyalina ce, bana
son shisshigi. Ka tsaya a matsayinka, ka ci gaba da aikinka tun kafin kayi
silar rasa shi.”
Tuƙin ya ci gaba da yi cikin alhini. Yana ƙara hasko yadda iyayen yaron suka ba da
gudummuwa sosai wurin lalata tarbiyyar ɗansu,
sannan suka gaza neman hanyar taimaka masa.
* *
*
“Alhaji
ka tabbata fitar da kayannan babu matsala? Kana ganin yadda jami’an tsaro ke ƙara saka ido ta ko ina a fadin jihar
nan.
Ɗayan
ɓangaren ne na waya aka furta hakan, wanda aka
kira da Alhaji ya ƙyalƙyala dariya sannan yace.
“Shigo
da kaya bai zama matsala ba sai fitar da su
ne zai zama matsala? Yanzu
haka nasa an fara rarrabawa abokan kasuwancin namu, ba wani abin damuwa.”
Turo
ƙofar da Hajiya tayi ne ya sanyashi
saurin katse wayar.
“Wai
Hajiya sau nawa zan faɗa miki ki riƙa ƙwanƙwasa
ƙofa kafin ki shigomini ɗaki?”
“Na
yanzu dai ya wuce tunda na shigo, magana na shigo muyi akan yaronnan, don na
gaji da yadda ka zuba masa ido yake yawo a gari kamar wanda bashi da gata, duk
an rufe maka baki ka kasa taɓuka komai.”
Shiru yai mata saboda shi yanzu ba ta yaron yake ba, tuni
ya gama haƙura da shi ya sallama, saboda ya san
lallai alhakin wasu yaran ne ya sauka akan ɗan nasa har
shaye-shayen irin kayan da suke fatauci ya yi sanadiyyar aikata abin da yayi
har ya kore shi daga gidan.
“Alhaji da kai
fa nake magana.”
Wayar
shi ce tayi ƙara, ganin sabuwar
number sai ya ɗaga kawai saboda ƙauracewa tuhumar da Hajiya ke masa.
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!” Ya furta yana miƙewa tsaye, Hajiya ta bi shi suka miƙe a tare.
Abin
da ya furta kawai kenan, har aka katse wayar bai sake cewa komi ba.
“
Alhaji lafiya? Me ya faru?.”
Bai
ba ta amsa ba, ya kwashi makullanshi ya yi hanyar ficewa, ta bi bayanshi tana ɗaga
murya.
“ Ni fa na gaji da wulaƙancin nan da ka ke mun Alhaji, ka ƙi ka tsaya mu yi magana a kan yaron nan, ko don yanzu
kana da wasu yaran ne shi ya sa wannan ka ƙyaleshi?.”
Wani abu ya tokare ma shi zuciya, idan akwai abin da ya
tsana bai wuce Hajiya Rabi ta yi tunanin saboda wasu yaran nashi yake ƙin kula nata ba. Shi ya sa ba ya yadda ya kula yaran
Hajiya Karima a gaban Hajiya Rabi, soyayyar duniya ya ɗora akan Auwal, ya
sakar ma shi dukiya yana abin da yake so, ko faɗa ba ya mashi duk
don gudun ɓacin ran uwargidanshi, kasancewar Auwal ne ɗansu ɗaya tal da suka
haifa mahaifarta ta samu matsala, shi ne ma dalilin da ya saka shi ƙara auren.
“ Ni
dai na gaji da shirun nan da kake mun Alhaji. Idan kaima an gama da kai ba za
ka iya komai a kanshi ba sai ka min bayani.”
Ba
shi da lokaci da nutsuwar tattauna maganar nan da ita, cikin yanayin sauri ya
shiga rarrashinta.
“Ki
yi haƙuri kin ji, idan na samu lokaci sai mu
tattauna.”
Tun
kafin ta ba shi amsa ya yi gaba kawai ba tare da ya saurare ta ba. Suna fita
suka yi karo da Hajiya Karima za ta shiga ɗakin.
Fasa bin Alhajin ta yi, ta tsaya tana ta aika ma Hajia Karima da maganganu.
“ An
zo a yi murna saboda halin da aka saka ni da ɗana
a ciki ko? Ki cigaba da murna, mune da dariya a gaba. Yadda kika shigo gidan
nan kika rabani da mijina da ɗana, sai na tabbatar da na
tarwatsa miki taki rayuwar.”
Ba sabon abu ba ne a wurin Hajiya Karima, ta daɗe tana tunanin
hanyar da zata bi ta fita daga zargin Hajiya Rabi ta kasa, ita kanta ƙoƙarin ganin an ceci Auwal take amma
abun ya ci tura. Ita ma bar mata wurin ta yi, har tayi nisa
tana jiyo maganganun da take mata cikin ɗaga
murya.
Ɗakin Alhajin ta koma, bayan ta rufe ta ci gaba da duba
lungu da sako tana neman kuɗin da zata kai wa Malami, iyakar nema ta yi amma ba ta
samu ba, hakanan ta haƙura ta fito jiki a salube ta yi ma ƙawarta waya.
“
Lami kuɗin
nan fa ba su samu ba. Na yi, na yi Alhaji ya bayar ya hana, na duba a ɗakinshi
babu, ban san inda zan samo kuɗin nan a kai ma Malam ba.”
“
Haba Hajiya, dole fa sai kin siyar da filin nan.”
“
Filin ne da ba nawa ba Lami, na Auwal ne, ba ƙaramin
tashin hankali zan shiga da Alhaji ba idan ya gane na siyar da filin nan.”
“ Sadda zai gane ai fili ya gama mashi amfani, ba faɗan da zai maki sai
sam-barka, kina ji fa Malamin nan aikin shi ba ɓata lokaci, cikin ‘yan
kwanaki za ki ga ya warke sarai.”
“
Haka ne Lami, bari dai mu gani to.”
“ Ba
wani abin da za mu
gani, ban sanki da gardama akan neman lafiyar yaronnan ba, an jima ko gobe zan zo miki da mai sayen filin.”
“ To
shi kenan.”
Kwana
biyu ta gama tattara kuɗin fili a hannunta. Ƙarya ta yi wa Alhajin, da yake baya
cikin natsuwa bai tsaya bincike ba ya bar ta suka tafi kawai.
Sai
da ta biya wurin Auwal don ganin halin da yake ciki. Cikin sa’a yau bai riga ya
sha ƙwayoyin sun ƙarasa ɗauke
mishi sauran hankalin da ya rage mashi ba. Tana ganin lokacin da mai kawo mishi
ƙwayar ya bar wurin.
Bayan
ta gama bashi abinci, ya kalle ta yana harhaɗa
magana da ƙyar,
“
Umma wai ni yaushe zan dawo gidan nan?.”
“ Ka kusa insha Allah, ka ƙara haƙuri ka ji, yanzu ma
nema maka magani zan tafi, shi ya sa daga yau ma Bala ne zai rinƙa zuwa wurinka ba ni ba.”
Wani
abu ke son hanata tafiya ta bar shi, gani take kamar akwai abin da zai faru da
shi.
Zumbur
ya miƙe kaman wanda aka mintsina, a nan inda
suke ya juya baya kawai ya fara fitsari. Haka ta tashi suka bar wurin tana
mishi kuka sosai kamar kar ta tafi.
Ƙasar Nijer suka nufa, kwanan su biyar
ana yi ma Auwal magani a cewar Malamin, sannan suka ɗauki
hanyar dawowa.
Tun
a hanya da suka kunna labarai ta ji Sanarwar an kama mijinta akan laifin
safarar miyagun ƙwayoyi.
Bata samu fara biyawa ta wurin Auwal ba, gida kawai ta wuce don ganar wa
idonta.
Dandazon mutanen da ke zaryar zuwa jaje ma kaɗai ya isa ya
tabbatar mata, wata Ƙanwar Alhajin ce da suka shiga tare
ta taho inda suke, ko gaisuwar ta bata amsa ba take tambayarta,
“
Fatima wai me ke faruwa a gidannan?.”
“
Komai ma ya faru Hajiya kina ina? Jiyan nan jami’an hukumar NDLEA suka zo gidan
nan suka kama Alhaji, suna hanya wasu da ake zargin abokan harkarsu ne suka
saka su, su yi ƙoƙarin kashe Alhaji don gudun kar ya tona
musu asiri, ai jiya mun ga tashin hankali Hajiya.”
“ Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un, Alhaji da fataucin
miyagun ƙwayoyi Fatima.”
“ Mu
ma dai mun kasa daina mamaki Hajiya.”
“
To, Allah ya fitar da shi
idan ba shi da laifi.”
“ Ameen Ya Allah.”
Ɗakinta ta koma, batun kama Alhaji na ta damunta, ga
magungunan Auwal bata san yadda zata fita ta fara mishi amfani da su ba saboda
mutanen da ke ta sintirin zuwa gidan.
Bala
Driver ta kira sashenta, sun gama gaisawa, ta jawo ledar da magungunan suke a
ciki. “ Magungunan Auwal ne Bala, ban san yadda zan fita daga gidannan ba, zan
maka bayani idan ka je sai ka ba shi.”
Sadda
kanshi ya yi ƙasa, yana so ya yi mata bayani ya rasa
ta inda zai fara.
“
Lafiya dai? Ko ba zaka iya kaiwa bane?.”
“
A’a Hajiya, Auwal ɗin dai ne.
Ta
zabura ta miƙe a tsaye.
“Auwal
ɗin
dai ne kamar ya?, me ya faru da shi?.”
“
Wallahi tun ranar da kuka tafi ni ke
zuwa duba shi wurare daban-daban amma Allah bai yi na gan shi ba, yanzu haka
daga wurin da ya saba kwana ni ke ko
alamunshi babu.”
Zumbur
ta miƙe tsaye,
“kuma
ka ke nan gabana zaune? Bani makullan mota.”
“Hajiya
yanzu zan je in ƙara
dubawa.”
“ka
bani makullin mota na ce.”
Ba
ta tsaya jiranshi ba ta yi gaba, da ta tuna makullan motar da suka dawo na
wurinta. Da ƙyar
ta iya tsayawa yi wa
Fatima bayani, sannan ta tafi nemanshi.
Nema
sosai ta sha Babu Auwal babu alamunshi. Mutane da yawa sun tausaya mata, duk da
wasu na ganin kuskurenta ne, da kuma sakacinta tare da mugun bakin da take yiwa
yaran wasu.
*
* *
Waiwaye...
“Umma
ki ba ni kuɗin nan fa, idan ba ki ba ni ba waye zai
ba ni?.”
“To
Auwal ana bayar da babu ne? Wanda ni ke
da su duk ka kwashe. Ka na
sane da furucin mahaifinka na hana baka kuɗi
tun da ya ga ka fara shiriritar nan, kai kuma ka ƙi ka nutsu ka daina abubuwan da kake yi.”
“Umma
ni me nake yi? Don kawai na ce a bani kuɗi?.”
“Da
ma kai ba zaka san abin da kake yi ba Auwal, saboda duk abin da kake ba yin
kanka bane sanya ka ake.”
Kalaman ta da ke ƙara mishi ƙarfin gwiwa kenan yana aikata duk abin da yake yi, saboda
Ummanshi ba ta ganin laifinsa, kuma duk da yasan yana ɗaukar mata kuɗi bata taɓa yi mishi faɗa ba, sai shima
yake ganin kaman ba laifin nashi ba ne ya ke ci gaba da aikata shaye-shayensa.
Ganin ba zai samu komai a wurinta ba, sai ya wuce ɗakin Abban nasu,
cikin sa’a kuwa yau ma ya gane inda yayi ajiyar kuɗi. Masu
yawa ya kwasa, sannan ya fice wurin Abokanshi.
Yaran
masu kuɗi ne
kamanshi, da basu da aiki sai zuwa club da yawo da ‘yan mata.
Ranar burinshi kawai ya nuna musu shi ma fa zai iya shan ƙwaya da yawa kamansu koma ya fi su, saboda yadda kullum
su ke mishi gorin ƙaramar ƙwalwa gareshi, ba zai iya ɗauka da yawa ba.
Da
yawa ya sha yayi mankas, tun a wurin ya fara tayar da hayaniya, da ƙyar
Abokanshi suka bar wurin da shi, ranar bai kwana gida ba.
Abun
na shi yana ta ƙara
yawa, ba kullum yake kwana a gida ba. Idan bai samu kuɗi ba
kayan amfanin gida ya ke ɗauka ya siyar. Kullum cikin
kai shi Ofishin yan sanda, idan ba laifin sata ba to na faɗa,
ko kuma damfara. Tun yana abu cikin hankali, har ya fara fita hankalinshi.
Cikin zuwan da yake neman kuɗi ɗakin mahaifinshi
ne, da bai samu ba ya tsananta bincike, cikin sa’a ya ci karo da irin ƙwayar da yake siyarwa, dama irinta ne yake so ya ɗauki kuɗin ya saya, bai
tsaya ƙirgawa ba ya kwarara su kawai a baki. Tun
daga ranar ko babu kuɗi can yake zuwa ya duba, duk
wata ma’ajiyarshi ya santa.
Shawarar
yiwa Auwal aure Hajiya Rabi ta kai ma Alhajin, ya kalleta sheƙeƙe,
“Aure
fa kika ce Hajiya, a ɗauri kashi ko a ɓata
igiya? Ina abun yake wai maye ya ga jariri, duka shekarunshi nawa da zamu mishi
aure? Kuma wanne iyaye ne za su
yarda su bawa Auwal auren ‘yar
su? Sai dai ko wanda suka haƙura
da ita.”
“Haba
Alhaji, kai da kanka ka ke faɗin haka akan ɗan
cikinka? To idan bamu mishi auren ba ya zamu yi da shi? So kake mu zura ido
muna kallo ya lalace akan idonmu.”
“Lalacewa
ta nawa kuma Hajiya? Shawarar dai dana yanke zan ɗauke
shi ne na kaishi rehabilitation centre, su dan riƙe shi na wani lokaci a samu ya daina
abin da yake.” “_rehabilitation_ fa Alhaji,
ina! Nima ban yarda da wannan shawarar taka ba, akan me za’a kai shi can bayan ni da
kai mun sani sarai asiri aka mishi ya fara shaye-shayennan, ina ma laifin kace
za’a kai shi gidan Malamai a
nema mishi magani, ko ita kaje ka matsa mata ta sa a karya abin da
aka mi shi.”
“Kin ga Hajiya, don Allah ki daina maganganun nan,
ki ci gaba da kyautatawa abokiyar zamanki zato. Sannan ki bari a kai yaron nan
inda zai samu lafiya.”
“A’ah
wallahi, babu inda za’a kai mun ɗana
a takura rayuwarshi.”
“Shi
kenan.”
Ya ƙyaleta kawai a
haka, yana ƙara maida hankalinshi akan
harkokinshi na dillancin miyagun ƙwayoyi , cikin
sirri suna ƙara faɗaɗa wuraren siyarwa,
duk wani club da matasa ke zuwa, da wasu wuraren daban-daban.
‘Yan uwan Babansa duk sun gwada ɗaukar Auwal sukai
gidan mari saboda maganar da ya ke yawon dauko musu, anma fafur Hajiya ta ƙi yarda, ko fada bata son kowa ya mishi, haka duk suka
tattara suka barta da shi.
Neman
magani take sosai wurin Malamai, suna cin kuɗinta
kawai.
Ranan
tana zaune falo ya wuceta. Kuɗi ya duba babu, babu kuma
abun siyarwa, ƙwayoyinma da yake
samu a ɗakin
Abbansu ya daina ajiyewa. A fusace ya fito ya mata tsaye.
Yana
magana muryarshi na kyarma, tsayuwar ma da ƙyar yake yin ta.
“A
bani kudi.”
“Da
akwai ai da ka samu Auwal, bani da su.”
Wayarta
dake saman cinyarta ya fizga ya yi hanyar fita, da sauri ta tare shi.
“Ina
kuma za ka kai mun wayar?.”
“Siyarwa.”
“Siyarwa
kuma kamar yaya? To ni kuma in yi amfani da wacce?.”
Bangajeta
ya yi zai wuce, da sauri ta sake tararshi.
A yanayin da yake ciki baya jin zai iya haƙura, burinshi kawai ya samu kuɗi ko ta yaya ne ya
je ya amso ƙwaya, gaba ɗaya baya jin daɗi da bai sha ba.
Kokawa ya shiga yi da Umman tashi, ganin bata da niyyar
sakinshi ya cire charger ya fara dukan ta, duk da ta sakar mishi tana
ihu bai daina ba, gani yake ta ma raina shi, gani ya ke kamar wata daga cikin ‘yan
matanshi ce yake duka.
Daidai Abbanshi ya dawo gidan ya jiyo ihunta, da gudu ya
shiga ya tarar da Auwal ne yake dukan ta, yayi ƙoƙarin karɓarta sosai anma ya
kasa, wani irin harbi Auwal ya mishi sai da ya dangana da bango, tuni jini ya
fara zuba a kanshi, bai ƙara sanin meke
faruwa ba sai a asibiti.
Kafin a Sallameshi daga asibiti Auwal ya shiga wani
babban supermarket ya yi sata sun gudu shi da abokanshi, da ƙyar Alhajin ya iya rufe maganar, bayan ya biyasu kuɗi masu yawa. A
hankali ya rinƙa neman abubuwansa
masu muhimmanci babu, ga jinyar da Auwal ya bar shi da ita.
Sake
ma Hajiya maganar dauke Auwal yayi, ta ƙi
yadda, duk da itama halin da ya saka ta, saboda haka ya ce lallai sai Auwal ya
bar gidan ko kuma su tafi tare, saboda shi yanzu tsoran sa ma yake, haka ta haƙura ya kora Auwal daga gidan da tunanin
zata nema mishi magani ya dawo.
* *
*
Bayan
shekara ɗaya
da watanni.
Babu
Auwal babu labarinshi, tuni Hajiya ta rame ta fita daga hayyacinta. Ta kasa haƙura, kullum cikin fita neman Auwal take.
Alhaji an wuce da shi
gidan yari saboda tabbatar da laifin da ake zargin shi da shi
bayan doguwar shari’ar da aka gabatar, tun a kotun ya sawwaƙe musu aurenshi da ke kansu.
Gaba
ɗaya
Hajiya ta kasa hakura, har ɗaki ta tarar da Hajiya
Karima ta kama ɗanta Namiji ta shaƙe za ta kashe shi su duka su yi asara,
da ƙyar
aka ƙwace yaron, dole aka raba su zama gida ɗaya.
Tana
zaune ta zuba tagumi, ta jiyo sallamar Hajiya Karima,
Zumbur!
Ta mike a fusace ta fita, sai dai tana fita ta ci karo da Auwal tsaye yana
murmushi cikin shiga ta kamala, da yanayin da ta manta rabon da ta ganshi a
ciki.
Tsaye ta yi ta kasa ƙarasawa, tana tunanin ko gizo ne ya mata, sai da ya ƙaraso da kanshi ta ji ya yi magana,
“Umma.”
Da
sauri ta ruƙunƙumeshi ta kasa saki, kuka take sosai
tana godiya ga ubangiji.
Hango
Hajiya Karima ne ya sa ta sassauta riƙon
da ta mishi,
“Munafuka!
Dama nasan ke ce zaki ɓoye min ɗana,
kuma...”
“Haba
Umma, ko don yanayin da kika gan ni ai ya kamata ki haƙura a miki bayani, babu laifin Mama,
taimakona ne ma ta yi.”
“To
ina jinka.”
“Umma
mu zauna ko.”
Suka
shiga ɗaki
suka zazzauna, sannan Hajiya Karima ta fara bayani,
“
Tabbas Hajiya ni ce na ɗauke Auwal, amma kuma da
kyakkyawar manufa, da kuma sanin Alhaji da yan uwan Alhaji saboda ganin da muka
yi ke kin kasa yadda a taimake shi.
Ba wai mun ga gazawar ki bane wurin ganin kin gyara rayuwarshi, kawai dai
hanyar da kika bi ce muke ganin kamar kin rufe ido ne.” Ta nisa sannan ta ci gaba,
“Duk da zaman kishi ne ya haɗamu, tsakani na da
Allah nake zaune dake, ban taɓa tunanin cutar da ke ko ɗan Alhaji ba. Wannan
ya sanya mu ka ɗaukeshi
mu ka kai shi wurin da muka san lallai can za a
taimaka mi shi.”
Auwal
ne ya ci gaba da magana.
“_Rehabilitation_
mai tsada aka kai ni Umma, akwai wurin kwana mai kyau, abinci mai kyau, ana yi
mana duk abin da ya kamata. Babu mai dukanmu, akwai daɗin zama sosai wurin Umma kowa magana mai daɗi
yake mana.”
Ɗayan hannunshi ya ɗora
saman hannunta da ta
riƙe shi gam.
“Ko
kaɗan
banga laifinki ba Umma da ki ka
barni ina yawo cikin bola bana da wurin kwana ba, ni kaina a lokacin na ɗauka
shi ne gatan, bana so a kaini inda za’a hanani shaye-shaye, ina ganin kamar duk
sadda ban sha ba mutuwa zan yi.”
“Na
yi dana sani Umma, nayi dana sanin aikata shaye-shaye sosai. Da yanzu na zama
cikakken mutum kamar kowa, da yanzu nayi ilimi kamar kowa, watakila ina aikin
gwamnati ko kasuwanci da zai taimaka mana. Ban yi tunani ba ko kaɗan,
dana biyewa sharrin zuciya da zugar Abokai. Umma ban san ta inda zan fara rokon
yafiyarki ba akan dukkan abinda na aikata muku ba, kun nuna mun soyayya sosai
kun ɗora
yarda a kaina, na watsa muku ƙasa
a ido.”
Da ƙwalla ya karasa maganar, cikin tausayi
take kallon yaron nata.
“Kar
ka damu Auwal, abin da aka shuka shi yake tsira, icce tun yana ɗanye
ake tanƙwara shi, mu ma da namu laifin da muka
kasa tsayawa mu ba ka tarbiya yadda ya kamata, burinmu kawai muyi maka abin da
ka ke so komin muninsa. Hankali na ya kasa
kwanciya, kullum gani nake Hajiya za ta
kai ka wurin boka a raba ka da Alhaji, saboda yanda nake ji ana cewa kishiyoyi
na yi, har da su kuma Malaman da suke ƙara
tunzura ni, kullum cikin yi ma yaranta fatan lalacewa na ke yanda Alhaji zai
guje su ya soka kai kaɗai, sai gashi ni nawa yaron
ne ya lalace, ga kuma alhakin yaran wasu da rayuwarsu ta lalace saboda
mahaifinku, shi Alhaki kwikuyo ne, kuma sharri ɗan
aike, abin da muka yiwa wasu ne muka gani a kanka, kaima ka yafe mana saboda
kasa baka tarbiyar da muka yi.”
Ta
mai da dubanta ga Hajiya Karima.
“Ina
jin kunyarki sosai Hajiya, ban taba sanin ke masoyiyarmu ba ce, kullum a maƙiyiyata nake kallonki. Ba ki barni da yarona ba duk abubuwan da na
miki, ki ka dage ki ka
ceto rayuwarshi, na gode sosai, don Allah ki yafemun.”
“Kar
ki damu, komai ya wuce wallahi ban taɓa riƙonki da wani abu ba. Insha Allah wasu
yaran ma sun daina shiga halin da ya shiga, saboda yanda gwamnati ta saka tsaro
sosai a na ta
kama masu siyar musu da kayayyakin.”
“Masha
Allah, sauran namu muma iyayen mu ci gaba da saka masu ido, muna kula da irin
rayuwar da su ke, da kuma mutanen da suke tare.”
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.