Ticker

6/recent/ticker-posts

Addu'ar Magance Larurar Jinya

TAMBAYA TA 3232

Assalamu Alaikum don Girman Allah wanna zaure a taimaka man da addu,ar da zan yi wa yarana sun cika yin rashin lafiya,hankalina yana tashi Ina tsoron kar lalurar da ke gareni yazam suna da ita wato HIV don Allah a sakaya sunana.

AMSA

Wa alaikis salam wa rahmatulLah.

Daga cikin addu'o'in da Manzon Allah ya koyar domin magance yawan larurar jinya akwai:

أُعِيذُكُمَا بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّةِ مِنْ كُلِّ شَيْطَانٍ وَهَامَّةٍ وَمِنْ كُلِّ عَيْنٍ لَامَّةٍ

Zaki tofa musu ita kullum da safe kafa uku.

Idan yaran naki guda biyu ne sai ki fadi addu'ar kamar yadda take arubuce anan. Da kalmar 'U'eedhukuma' afarkonta. Amma idan sunfi biyun kuma sai kice "U'EEDHUKUM" Idan namiji ne guda daya "U'eedhuka" idan mace ce "U'EEDHUKI".

In shaAllahu za su samu kariyar Allah daga kowanne nau'in sharri ko jinya ko abin tsoro.

Daga cikin hadin magungunan da za ki rika sha ke kanki domin karfafa garkuwar jikinki akwai:

Garin Habba, Garin Kirfa, garin zogale, garin ganyen gwanda. Dukkaninsu ki samoshi daidai da daidai. Misali kamar cokali uku-uku ko biyar-biyar, ki hadesu waje guda ki zubasu a cikin zuma mai kyau sannan kullum da safe ki zuba cokali biyu na hadadden maganin a cikin ruwan dumi ko ruwan lipton sannan kisha.

Suma yaran naki ki rika basu ko da cokali 1-1 ne.

Ki dena sanya yawan damuwa a zuciyarki. Ki rika kokari kina yawaita zikirin Allah safiya da maraice tare da koya wa yaranki gakan suma suna yi. Kiyi kokari ki kulla kyakkyawar dangantaka tsakaninki da Allah. In shaAllahu za ki samu kulawa ta musamman daga gareshi.

Ki rika kuma ziyartar likitanki na asibiti domin samun karfin gwiwa da shawarwarin yadda za ki Ƙara kyautata lafiyar jikinki.

WALLAHU A'ALAM.

DAGA ZAUREN FIƘHU 07064213990 (02/11/2025).

ƘARIN BAYANI

ADDU’AR NEMAN KARIYAR ALLAH GA YARA DAGA YAWAN RASHIN LAFIYA

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh. Ina roƙon taimako da addu’a daga wannan zaure. Yarana suna yawan kamuwa da rashin lafiya, kuma hakan yana matuƙar tayar mini da hankali. Wani lokaci ma sai tsoro ya shige ni ko wata larura ce mai tsanani da za ta iya shafar su. Don Allah malam, wace addu’a ce Musulmi zai riƙa yi domin neman kariyar Allah ga ’ya’yansa daga cututtuka da sauran sharri? Ina roƙon a ɓoye sunana.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikis Salam wa Rahmatullahi wa Barakatuh.

’Yar uwa Musulma, abu na farko shi ne ki sani cewa lafiya da rashin lafiya dukkansu suna cikin ƙaddarar Allah, kuma Allah ne ke ba da lafiya kuma Shi ne Mai warkarwa. Don haka abin da ya kamata Musulmi ya yi shi ne ya haɗa tawakkali ga Allah, addu’a, da kuma neman magani na halal.

Daga cikin addu’o’in da Manzon Allah ya koyar domin neman kariya ga yara daga cututtuka, aljanu, da hassada, akwai addu’ar da yake yi wa jikokinsa Hasan da Husain (Allah Ya yarda da su). An rawaito daga Ibn Abbas (Radiyallahu anhuma) cewa Annabi ya kasance yana neman kariya ga jikokinsa da wannan addu’a:

« أُعِيذُكُمَا بِكَلِمَاتِ اللَّهِ التَّامَّةِ مِنْ كُلِّ شَيْطَانٍ وَهَامَّةٍ وَمِنْ كُلِّ عَيْنٍ لَامَّةٍ »

Ma’ana:

“Ina neman muku kariya da kalmomin Allah cikakku daga dukkan shaidan, daga kowace halitta mai cutarwa, da kuma daga dukkan idon hassada mai cutarwa.”

(Sahih Al-Bukhari)

Ana iya karanta wannan addu’a a kan yara sannan a tofa musu a hankali, musamman da safe ko da yamma. Idan yara biyu ne, a yi amfani da kalmar “أُعِيذُكُمَا” (U’eedhukuma) kamar yadda hadisin ya zo. Idan yara sun fi biyu, a ce “أُعِيذُكُمْ” (U’eedhukum). Idan yaro guda ne namiji, a ce “أُعِيذُكَ” (U’eedhuka), idan kuma mace guda ce a ce “أُعِيذُكِ” (U’eedhuki).

Haka kuma yana da kyau Musulmi ya riƙa yawaita karanta wasu ayoyin kariya daga Alƙur’ani kamar Ayatul Kursiyyu da kuma surorin kariya. Allah Ya ce:

اللَّهُ لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ الْحَيُّ الْقَيُّومُ

Ma’ana:

“Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai Shi, Rayayye Mai tsayuwa da komai.”

(Suratul Baqarah: 255)

Annabi ya bayyana cewa karanta Ayatul Kursiyyu yana kawo kariya daga shaidan har zuwa safiya ko dare.

Haka kuma yana da kyau a riƙa karanta Suratul Ikhlas, Suratul Falaq, da Suratun Nas domin neman kariya daga sharri. Allah Ya ce:

قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ • مِنْ شَرِّ مَا خَلَقَ

Ma’ana:

“Ka ce: Ina neman tsari ga Ubangijin safiya daga sharrin abin da Ya halitta.”

(Suratul Falaq: 1–2)

Wadannan surori suna daga cikin manyan addu’o’in kariya da Annabi yake karantawa ga kansa da iyalinsa.

Bayan addu’a da zikiri, yana da muhimmanci ki kula da lafiyar yaranki ta hanyar zuwa asibiti domin samun shawarar likita da magani idan akwai buƙata. Musulunci ya ƙarfafa neman magani, kamar yadda Annabi ya ce:

« تَدَاوَوْا عِبَادَ اللَّهِ فَإِنَّ اللَّهَ لَمْ يَضَعْ دَاءً إِلَّا وَضَعَ لَهُ دَوَاءً »

Ma’ana:

“Ku nemi magani, ya ku bayin Allah! Domin Allah bai saukar da wata cuta ba face Ya sanya mata magani.”

(Sunan Abu Dawud da Tirmizi)

Saboda haka ki haɗa addu’a, zikiri, tawakkali ga Allah, da kuma kula da lafiya ta hanyar likitoci. Ki guji yawan damuwa, domin damuwa mai yawa na iya ƙara wahalar da zuciya. Ki riƙa yawaita kusanci da Allah ta hanyar salla, zikiri, da karatun Alƙur’ani.

Allah Ya ba ki kwanciyar hankali, Ya kare yaranki daga dukkan sharri da cututtuka, kuma Ya ba su cikakkiyar lafiya.

Wallahu A’lam.

Daga Zauren Fiqhu.


ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments