Halima K. Mashi (2020). A Rashin Sani. Muhalli, Sutura (Labaran Da Suka Samu Nasara a Gasar Gajerun Labarai a Kan Muhalli Ta Arc. Ahmed Musa Dangiwa, 2020). Darma Digital Prints.
A RASHIN SANI
Na
Halima K Mashi
Malam Aminu ya kurɓi kunun tsamiyar cikin hikima don gudun kar ya ƙone, sauri ya ke zai je lambu in da suke sarin karas da yalo, ga yunwa yana ji, ga kunu da zafi, bugu da ƙari ga shi in mutum bai je a kan kari ya kama kayan ba babu lallai ya samu.
Ya sake girgiza kofin kunun tare da faɗin “Wai kuwa Hauwa me ya hana ki barin kunun nan ya huce ne?”
Ta ce “Baban Maryam ka ajiye ya huce mana,
ka san ban jima da dama shi ba”. Ya ce ”Au ki ce zamanki kika yi ba ki dama da
wuri yanda zai huce ba, kin san fa ina sauri in je lambu duk kuma wahalar nan
burina bai wuce in ga mun tsere ma batun hayar nan ba”. Ta ce “Baban Maryam kullum
addu’ata kenan mu ma dai mu mallaki muhallinmu domin mu ji yadda
masu gidan kansu suke ji, Kai! Gaskiya mun wahala a yawon haya har dai wannan
gidan da muka sha jinya sakamakon gina shi da a ka yi a kan
magudanan ruwa, kuma rijiyar gidan ta haɗe da masai”.
Ya yi ‘yar dariya “Bari tuna min Hauwa lokacin nan mun ji jiki, shi ya sa
ba ni da burin da ya wuce in kammala ɗan ginin nan ko ma fita daga wannan
takaicin na ƙuncin rayuwar haya”. Hauwa cikin salo na kwantarda hankali ta
tausasa murya ta ce “Ranar kuwa za mu yi bacci har da saleɓa Allah kar ka kashe
ni sai na ga wannan rana”. Ya ce “Amin Hauwa’una, in sha Allahu burin namu zai
cika muna raye ni da ke mai kambu biyu ga ki uwargida ga ki amarya, yaushe
rayuwa za ta yi daɗi babu ke, mun sha wahala tare ban kuma taɓa ganin canji ba,
da yardar Allah muna tare afuwa za ta samu ”. Ta ce ” Allah ya huwace mana, sai dai matsalar ɗaya ce na san da ka mallaki
muhallin nan sai ka buƙaci ka ƙara aure”. Ya dire kofin tare da miƙewa, ya tafi yana sosa ƙeya kana ya ce “Wananan kuma na Allah
ne Hauwa, fatanmu dai yanzu mu samu matsugunnin”. Ta ce”Allah ya ba da sa’a,
kar ka manta ka taho min da gurji”.Ya ce “ In sha Allahu ba zan manta ba Hauwa kar ki haifo min ɗana da
rowa”. Cikin jin daɗi ta ce” Allah ya dawo da kai lafiya”.
Malam Jamilu ya
shiga ofishin shugaban makaratar hankalinsa a tashe, malam Adamu
shugaban makaranta [ principal ] ya ɗago kai ya kalli malam Jamilu,
sannan ya mai da kansa ga takardun da ya ke dubawa tare da faɗin “Lafiya kuwa malam Jamilu na
ganka kamar a fusace?".
Malam Jamilu ya ce
”Yallaɓai na zo ne a kan batun nan na muhalli, ga shi kuɗin hayar gidan da nake
zaune da iyalina ya ƙare kuma mai gidan ba ya ɗaga ƙafa, saboda haka ni yanzu a
karɓo min kuɗina ma da na tara waɗanda ake ta tsakurar min duk wata sai in biya
hayar in samu sa’ida, can gaba in da rabo na mallaki muhallin”.
Malam Adamu ya ce “Ka
kwantar da hankalinka, duk zancen ba haka yake ba, ka zauna mu yi magana ta
fahimta”. Malam Jamilu ya ce “
Ba zan iya zama ba Malam, don gaskiya ina zaton ba a bi tsarin da ya kamata ba
ne, ga shi mutane suna ta amfana, mu tun yaushe muka cike bayanan ajiya kuma an
ce wata shida kawai ake yi a samu, to,wai a ina aka samun matsala ne, a can
bankin ne! ko a ma’aikatar ilmin? ko kuwa a nan ne?”. Malam Adamu ya buɗe baki
da nufin magana sai Malama Rahina ta ƙwanƙwasa ƙofa tare da sallama, ya yi
saurin amsawa tare da mai da hankalinsa gare ta, kamar ba ya son ta ji me su ke
tattaunawa da malam Jamilu.Ta kalli shugaba ta ce dama na zo ne kan
batunmu na bankin lamunin mallakar muhalli, yallaɓai ina muka
kwana?”. Gumi ya fara ratso jikin Shugaba, ya yi saurin tarar numfashinta ya ce
“Malama Rahina tsarinmu ya sha bamban da na mutum ɗaya, mu fa ma’aikata ce ta
yi mana rijista kuma daga albashinmu ake tsakurar kaso biyu da ɗigo biyar kuma
sai an yi wata shida a na cirewa kafin a fara neman rance na siyan gida ko
gyaran gida ko a bayar da kuɗi a gina gida, wannan ne sharaɗin”.
Malam Jamilu ya ce
“To amma in an duba mun haura wata shida a na cire mana kuɗi amma shiru
maƙwatau kake ji, kamar dai ba a bi tsari ba yadda ya kamata. Malam Adamu ya so
ma fusata ya ce, “ban gane ba, zargi na ku ke a kan ci muku kuɗi ko kuwa? Kar
ku manta mu duka ne a tsarin nan kuma tare mu ka yi komai a kan idanunku, sannan
ba ni ne na kai sunanku ko na yi muku rijista ba, nima daga ma’aikatarmu ta
ilimi [ministry of education] na ke samun bayanai kuma su ne ke aiko da
lambobi, a ofishina sa hannu kawai ake yi.
Ba zai zama adalci ba in kuka zarge ni da wani abu na
rashin bin ƙa ida. In kuma kuna son kuɗinku, to ku tafi can ma’aikatarmu ku
bincika ko ku bi kadi. In ban da son rai ni ma fa ina cikin tsarin, ku tuma so
nawa aka yi mana bita a kan wannan tsarin, tabbas za a ba mu tunda na san waɗanda
su ka amfana. Ya kamata ku gane ba lokaci guda za a ce kaf makarantun Jihar
Kaduna za a ba su ba, yanda suka raba lambobi bi -da –bi, to haka zai kasance
kowace makaranta za a zo kanta, ko kun ga an ba ni ne ku ba a ba ku ba?
Ya yi musu tambayar cikin gwauran numfashi. Malama Rahina
ta ce”In haka ne za mu iya ƙara haƙuri kaɗan ko Malam Jamilu?” Ta faɗa ta na
duban shi. Malam Adamu ya tari numfashinta ya ce, “Ba na buƙatar
ku ƙara haƙuri, ku ci gaba da ta da balli, In har yanzu ba ku gane ba ina ma
abin yake wai mayya ta ci jinjiri, har nawa aka cira a kuɗin da kuke wannan
surutun”.
Cikin jin kunya
malam Jamilu ya ce “ranka ya daɗe Allah ya huci zuciyarka, ai kuma na fahimta,
ba wai muna zargin ka ba ne, kuma ba abin tashin hankali ba ne, Allah dai ya
kai damo ga harawa ko bai ci ba zai yi birgima”. Malam Adamu ya ce ”Ka faɗi
haka mana tunda tusa ta ƙare wa Bodari, ko in ce ruwa ya ƙare wa ɗan kada, babu
sauran abin da za ka faɗa, matsalarku ke nan mutananmu rashin haƙuri. Na rasa
dalili duk lokacin da sauƙi yazo wa ɗan Najeriya sai ya dinga neman sa ka zargi
a ciki”.
Ya dubi malama
Rahina ya ce “ke kuma da na ke ganinki mai fahimta kuma wai sai kika biye wa malam
Jamilu wanda da ma shi ko ruwa ka wuce da shi ta gabansa sai ya ce ka baɗa masa
ƙura”. Ta ce “Ba haka ba ne malam, naji ne a na ta samu, kuma ka san wanda ke
matse, ga shi ina gidan haya ga marayu, sannan gidan ba mu kaɗai ba ne kullum
sai fitina, wallahi kaji amma ayi mana afuwa.” malam Adamu ya koma ya zauna
tare da faɗin “ku tafi gurin aikin naku”. Malam Jamilu ya fara fita cikin kunya. Malama Rahina ta
na fitowa ya tare ta ya ce “Kai na ji kunyar malam Adamu
sosai, na daɗe ina zarginsa cikin rashin sani, kuma ba ni da wata hujja”.
Malama Rahina ta ce, “Ni ma ai ka sa na ji kunyar mutumin nan yana ganin
mutuncina yana tausaya min na biye wa famfon da kai min”. Ya bi ta da kallo, ta
nufi ajinta. Sannan shi ma ya kaɗa kai zuwa nasa.
Malam Aminu Ya yi
tsaye turus a gaban gininsa wanda ya kai linta, ba komai ya tsorata shi ba sai
ganin rubutu da jan fenti, ko da bai da boko ya san rubutu da ja wata alama ce
ta matsala, sannan ga alamar [x] da ke nuna sharewa. Ya ɗaga kai ya kalli sauran gine- ginen suma duk an yi
musu wannan alamar, sannan filayen gurin gaba ɗaya an saka wani allo da irin
wannan rubutun wanda ba zai iya karantawa ba.
Cikin tashin
hankali ya kalli mai motar da ya kawo masa bulo tare da furta “Innalilahi wa
inna ilaihirraji’un!”. Mai motar bulo wanda ya ƙaraso dan tambayarsa a ina za a
sauke bulullukan, ya bi shi da kallo cikin rashin fahimta, sannan ya ce, “lafiya
Malam Aminu?”. Ya amsa cikin ruɗani “To ina fa lafiya malam Bawa, dubi ka ga
wannan rubutun ko daga ina ne? Ko
su ne KASUPDA da nake ji ana faɗin suna rusa gini!”. Ya tari numfashin Malam
Bawa. Malam Bawa ya ce” Gaskiya wannan rubutun nasu ne, Allah ya fidda ku”.
Malam Aminu ya ce” To ai ni da takarduna kuma wanda na sai filin nan yana raye
bai mutu ba”. Malam Bawa ya ce “Shike nan, ta kwan gidan sauƙi ka
ga sai ka je ka same shi ya dawo maka da kuɗinka”.
Malam Aminu ya ɗauko
dattijuwar wayarsa wadda ta ji leda ya soma laluban lambar Malam Shehu wanda
shi ne ya yi masa hanyar siyan filin. Malam Shehu na ɗaga wayar Malam Aminu ya
ce”Akwai ƙatuwar matsala, na zo filin nan na samu KASUPDA sun rubuta alamar
filin da na siya akwai wata a ƙasa”.Malam Shehu ya ce “Ba na zaton yana da
matsala gaskiya, amma dai ka na ina ne yanzu ?”. “Ina gurin yanzu haka”.
Malam Aminu ya faɗa
yana kallon filin tamkar ya ɗauke shi ya tafi da shi. Malam Shehu ya ce “Kawai zai fi kyau ka fito ka tsallako
ina gida kawai mu ƙarasa gidan mai unguwar tunda a hannunsa aka siya in da wata
matsala na san dole yanzu ya sani sai mu ji ƙarin bayani ko?”. Malam Aminu ya
ce, “Shikenan ga ni nan yanzu”. Ya kalli malam
Bawa ya ce “Ina ganin ku juya da bulon nan mu ji abin da zai biyo baya
tukunna”. Malam Bawa ya ce “shike nan”.
Cikin ci da zuci
ya ke tafiya tamkar ya gan shi a ƙofar gidan malam Shehu, yanke hanyar ya yi dan
ba ya son ya wuce ta gaban gidansu bazawararsa Binta, musamman da ya ke daga
gurin sana’arsa ta yalo da karas ya ke, bai je gida ya ɗan watsa ruwa ba, bare
ya canza kaya.
Cikin rashin sa’a
sai suka yi kiciɓis da Binta ta fito ɗauke da ɗan bokitin markaɗe, duk su biyun
kunya ta kama su, musamman Binta wadda ba ta taɓa bari ya ganta babu janbaki da
gazar da ‘yar hoda ba. Ta sunkuyar da
kai, ji take tamkar ta nutse. Ya ce “ A a Binta daga ina haka?”. Ta ce “daga kai markaɗe
na ke, ka ganni yaran gidan duk sun fita daga barci ma na tashi”. Ta faɗa ciki
salon son ta nuna mi shi kar ya damu da ganin ta da ya yi a
haka.
Ya yi ɗan yaƙe ya ce, “Allah sarki, ni ma nan zani gidan malam Shehu”. Ta
ce “Allah Sarki”. Ta ɗan saci kallonsa, ta ce “za ka zo in an
jima ɗin?”. “In sha Allah zan ma kira ki.” Ya fada cikin zaƙuwa da son ta
bar shi ya wuce. Ta ce, “Shi ke nan sai na jika”. Ya ce “To ki gaida su Inna”.
Ya wuce cikin wani sabon takaici domin dai auren Binta na daga cikin abin da ya
saka yake son ya ga cewa ya mallaki muhalli amma ga shi lissafin na neman
canzawa.
A gidan mai’unguwa suna zaune kan benci suna jiran fitowar sa daga cikin gida. Wani mutum ya yi musu sallama, suka
amsa, ya ce “Don Allah Mai’unguwa yana nan?”. Suka ce “yana fitowa, mu ma shi muke jira”. Ya samu ge
fe ya tsaya, shi ma da ganin fukarsa ka san da
magana . Mai’unguwa yana fitowa su ka yi masa barka da fitowa, sannan suka matsa masa ya zauna. Suka gaisa
sannan ya waiwaya gurin baƙon da ke tsaye, ya ce, “malam Mudi kai ma ka ƙaraso?”. Ya ce “Na ƙaraso”, su ka gaisa. Mai’unguwa ya dubi su Malam Aminu ya ce “ai da farko na zaci shi ne ya yi sallama dan ya yi min waya cewar yana zuwa’.
Malam Shehu ya ce “Allah Sarki da ma
mu ma mun zo ne kan batun fili da malam Aminu ya siya, mun ga hukuma sun yi
rubutu a gurin kamar suna gargaɗin cewa a dakata”. Yana maganar ne kamar ya
gani da idonsa. Mutumin da mai’unguwa ya kira da malam Mudi ya cafke zancan da
cewa, “Ni ma dai abin da ya kawo ni ke nan, an yi mana rubutun gargaɗin dakatar
da gini a filinmu wanda gurin ka muka siya ni da ƙanina, ga takardu da sa
hannunka da na shedu.
‘Yar dariya Mai’unguwa ya yi tare da
faɗin “Na san wannan maganar, kowa ya je ya ci gaba da gininsa babu abin da zai
faru, gurin nan gonakinmu ne na gado muka sayar muku, kawai don gwamnati ta yi
wannan gadar shi ne za ta zo ta ce mun sayar da filayenta kuma wai hanyar da za
ta fitar da magudanan ruwa ne, kai ka ji fin karfi’. Malam Mudi ya ce “Yallaɓai
na ji fa a radiyo cewar gwamnati ta biya diyya ga masu mallakin wanɗannan
gonaki, kuma ta sanar da su komai tsawon lokaci za ta waiwayi gurinta. Sannan hukumar
tsara karkara da birane sun shelanta cewa wannan guri magudanan ruwa ne, duk
wanda ya sayi fili a gurin, to ya sai gaibu,in kuma ya gina lallai hukuma za ta
rushe.
Don haka kawai a can za mana guri ko kuma
a dawo mana da kuɗinmu”. Malam Aminu ya zaro ido, jikinsa ya ƙara sanyi domin
ya fi gamsuwa da batun wannan Malam Mudin saboda shi ma ya ji zancen yana yawo
sai dai bai kawo cewa har da gurin da filinsa yake ba.
Ya yi ƙarfin halin buɗa baki kamar
mai koyon magana, ya ce, “ni ma dai na fi buƙatar kuɗi na”. Mai unguwa ya nannaɗe
carbin hannunasa tare da ɓata rai ya ce “Maganar kuɗi ko canza guri babu ita,
domin dai an riga an sayar muku da fili a gaban shaidu kuma an ba ku takardu, ga
shi har kun je kun fara gini, kawai don gwamnati ta ce ku daina gini a filin da
ku ka siya da kuɗinku sai ku daina?
Ita gwamnatin ta mahaukata ce da za
ta zo ta ga gini ta rusa, ku yi kayanku, ku kammala a kan kari ku tare da
iyalinku. In an zo rusau kuna ciki ai dole a barku ko kuma gwamnatin ta biya ku
diyya kafin ta rusa .Amma ni dai ba ni da abin da zan yi muku, ai yau kun zo
‘ƴan kaɗan ne ma, domin jiya fadar nan cika ta yi kuma irin wannan jawabin na
yi musu suka gamsu”.
Malam Aminu ya ce “ A gaskiya ba zan
haɗa koko da giya ba, an ce da asara gara gidadanci, ba zan ƙara kai wani bulo
ba domin karo da aljani babu daɗi, rigima da gwamnati ba daɗi! Gara in koma in
jira mu gani nan da wani lokaci, in ba ta rusa ba sai mu ɗora ginin. Kash! Amma
ban so hakan ba ko kaɗan, gaskiya ba a yi mana adalci ba”.Ya faɗa ya na kallon mai’unguwa.
Mai’unguwa ya ce “To kuna iya ɗaukar matakin da ya dace,
ni dai iya maganata kenan”. Ya nufi gida, daf da zai shige ciki ne sai Malam
Mudi wanda ya ƙufula har ya kasa magana sai lokacin ya samu damar faɗin “mataki ka ce a ɗauka ko to ni zan ɗauka ”. mai unguwa ya waiwayo ya yi masa kallon hadarin kaji tare
da faɗin “To ina jira”. Ya shige abin sa.
Malam Aminu ya ce, “Inna lillahi wa inna ilaihirraji’un! Allahumma ajirni fi musibati! Shikenan
an gama cutarmu, talaka ba ya iya mallakar muhalli a ƙasar nan, duk wani
lissafi na ya ruguje”. Malam Mudi ya ce “kai ka haƙura ke nan?Ai ni daga nan sai caji-ofis kai tsaye ba Mai’unguwa ba
ko Sarki ne shi sai mun je gaban kuliya na bi kadin haƙƙina, domin ya riga ya
sani gurin haramtacce ne amma ya sayar mana tunda tun tuni gwamnati ta riga ta
biya su diyya kuma sun karɓa, amma saboda zalunci ya zo ya siyar mana ya shiga bishasharsa domin har
‘yammata biyu ya wanke ya yi ta yin ƙara ‘i, ashe duk da kuɗinmu ne.
Don haka, ko kowa ya ƙyale shi ni
dai ba zan taɓa ƙyale haƙkina ba.Ya juya cikin sauri ya ɗau hanya tamkar zai
tashi sama. Malam Aminu ya bi shi da kallo tare da nanata jawaban da
ya gama ji a cikin zuciyarsa musamman ma na Mai’unguwa ya wanki ‘ƴammata biyu
bayan shi ga shi zai masa buƙulun auren bazawararsa Binta, saboda samun
muhallin nan da ya ke neman suɓuce masa shi ne zai sa ya auri Binta ba matsala.
Malam Shehu ya dafa kafaɗar malam
Aminu sannan ya ce, “Ka yi haƙuri yanzu mu je gurin mu yi shawara, in ya so sai
a yi mai yiwuwa”. Malam Aminu ya ce, “wace mai yiwuwa, in dai ba gammo zan naɗa
in ɗauki filin ba, ya ka ga za a yi, dama na sani ne sai in haɗa kai da wancan
mutumin da ya tafi mu je caji -ofis ɗin, sai dai kuma ni ba ɗan asalin jihar ba
ne”. “Kaima fa ɗan ƙasa ne ba baƙon haure ba, ko a ina ne za
ka iya neman haƙƙinka”. In
ji malam Shehu. Haka suka tafi babu takamaimiyar magana ko shawara.
Malam Aminu yana shiga gida ko sallama bai yi
ba ya nufi ɗaki, ya shiga zabga tagumi, Hauwa ta fito daga banɗaki ta same shi zaune
a kan sallayar da ta idar da la ‘asar. Cikin sauri ta
ce, “Lafiya kuwa Baban
Maryam, ya na ganka a irin wannan yanayi”?. Ya dube ta sannan ya sauke ajiyar
zuciya, ya ce, “Ina fa lafiya Hauwa, ai ta faru
ta ƙare wai an yi wa mai dami ɗaya sata”. Ta dafa ƙaton cikinta sannan ta isa
bakin gado ta zauna, cikin yanayin zaƙuwa ta ce, “sata aka yi maka ko damfara?”.
Ya ce, “Hauwa gara a sace ni ko in
yi hatsari in karairaye tun da jinya zan sha kawai a kan abin da ya faru domin
ban san da me zan haɗa baƙin cikin da na samu kaina a ciki ba. Cikin firgici ta
ce, “ba dai Baba ce ta mutu ba?”. Ya zaro ido ya ce
“Haba Hauwa! Wannan kuma ai fatan tsiya ki ke min, sai dai in ko Babar
gidanku!”.
Ya faɗa a fusace, dariya ta kusan
ƙwace mata, amma sai ta shanye, ta ce “To ka kasa magana baban Maryam don Allah
ka sanar da ni ko na samu salama daga wannan fargabar da ka sani”. Ya ce “na je
yau na cika kuɗin bulon nan ƙwaya ɗari da na faɗa miki, sai muka je kai wa
gurin ginin filin da nake yi, to a can ne na tarar da tashin hankali wanda
Hausawa suke faɗin ba a sa maka rana.
Sanarwa na gani ɓaro-ɓaro an rubuta
mana a jikin katangar da na fara tayarwa a filin wai kar mu ci gaba da gini
domin filin na gwamnati ne. Hauwa ta sulalo daga
bakin gadon ta yi dirshan a ƙasa tare da ɗora hannuwanta a ƙasan mararta ta
dafe cikinta wanda ya shiga juyawa tamkar zai fito waje.
“Innalillahi wa inna
ilaihirraji’un”. take ta maimaitawa kafin ta ɗan samu damar faɗin “Yanzu ka je
ka samu wanda ya sayar maka da filin Baban Maryam zama fa ba naka bane”. Ya ce “Zuwa kuma na nawa, ai sai dai kar a kuma wai an haifi kumama”.
Nan ya kwashe yanda suka yi ya faɗa
mata, kuka wiwi Hauwa ta shiga yi, ta na faɗin Allah ka kawo mana ɗauki, sai
yaushe talaka zai zama mutum a ƙasar nan, dubi ɗakin da muke ciki ƙwaya ɗaya
rak ga yara biyu ga na uku na zuwa, sannan wannan gidan na haya mu shida ne a
cikinsa kullum cikin masifar faɗa muke daga rigima a kan yara sai faɗan jan
ruwa a rijiya.
Wallahi ko ɗazu da a ce na kula
Maman Tasi’u sai mun yi faɗa a kan banɗaki, ina ciki ban gama uzurina ba, sai
ta zo za ta zubar da bayan gidan ɗanta, ina ciki ina ji sai surutu ta ke yi wai
ni dama haka na ke yi idan na shiga banɗaki kamar na samu fadar Sarkin
Istanbul.
Da na fito a cikin gadara na faɗa
mata cewa ta dai sha kuruminta mun kusa ban kwana da haya, har na jefa mata
baƙar magana cewar su ma dai su yi zuciya su mallaki muhalli”.
Malam Aminu ya sauke ajiyar zuciya
tare da taɓe baki ya ce “In ba wani iko na Allah ba, ai mu da su duk ɗaya ne,
wai makafi sun yi dare. Amma dai zan nemi
wannan mutumin wanda ya ce zai yi ƙarar Mai’unguwa mu ji yanda za a yi, ko ban
samu kuɗina duka ba wataƙila in rage, in ko ba mu samu ba, to ina tabbatar miki
mu da mallakar muhalli a Kaduna sai gani sai hange wai kuturu ya ga ƙwaurin
Baturiya”. Ranar
dai gidan malam
Aminu tamkar gidan makoki haka suka kwana.
******
Dukannin malaman sun hallara a ofishin
Shugaban makarantar domin tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi maganar
mallakar muhalli wanda ma’aikatar ilmi ta yi wa malaman makaranta da sauran ma’aikatan
hukumar rijista da babban
bankin bayar da lamuni domin mallakar muhalli. [FEDERAL MORGAGE
BANK OF NIGERIA] Dalilin
Malam Adamu (Shugaban Makaranta) na shirya wannan zaman shi ne domin ya wanke
kansa da ga zargin da malaman da suke aiki a makarantarsa su ke yi masa,
musamman Malam Jamilu da Malama Rahina, kuma domin ma ya yi wa tufkar hanci shi
ya sa ya gayyato ɗaya daga cikin ma’aikatan babban bankin na bayar da lamunin mallakar gidajen domin ya sake
fahimtar da malaman game da irin romon da gwamnati ta ke son su ɗanɗana.
Bayan buɗe taron
da addu’a, sai malam Adamu ya miƙe ya yi shimfiɗa tare da sanar da su dalilin zaman
sannan ya buƙaci ma’aikacin bankin da ya tashi ya yi musu ƙarin haske game da
kuɗinsu da ake tsakura a albashinsu domin yi musu gatan ganin sun mallaki
muhalli.Ya miƙe ya gabatar da sunansa tare da fara koro musu bayani kamar haka:
“Ma’aikatar
ilmi ta ƙasa ta yi wa dukkanin ma’aikatun ta dake ƙarƙashinta rijista, kuma an
bi kowace makaranta an ba ta lamba. Kaso biyu da ɗigo biyar (2.5%) a ke cirewa
daga albashinku, in an yi wata shidda za ku iya fara neman rance domin mallakar
muhalli ko gyaran gida ko kuma gina gida.
Wannan wani adashi
ne na gata a ka shirya muku kuma wani abin birgewa shi ne, in duk mutum bai yi
wannan ba ina nufin in ba ka amshi rance ba har ka kai shekaru sittin to banki
zai maido maka da dukkanin kuɗa -ɗenka, a nan kun lura da gatan da wannan banki
ya yi muku? Ya je ho tambayar ya na dubansu, suka amsa da cewa “a’a”.
Ya
ce “A shekaru sittin dai kowannenku ya san cewa ya bar aiki ko?” Suka amsa da
cewa “Haka ne”. Ya ci gaba da cewa,
“Ka bar aiki ga girma ya zo sai kawai a ka
ba ka kuɗinka da ka tara a tsawon shekarun da ka yi kana ajiya, a wannan
lokacin ya za ka ji?” Cikin murna suka cika ofishin da hargowar nuna fahimtar
cewa lallai za a amfana da wannan banki, nan suka soma jeho tambayoyi. Malam Jamilu ne ya soma tambaya, a in da
ya ce “Ni tambayata a nan in mutum ya fara neman rancen mallakar muhalli a
tsawon wane lokaci zai samu?
Malama Rahina ta ɗaga
hannu, aka ba ta dama sai ta ce “Ni tambayata ita ce “Gidan za a saya wa mutum
ko zunzurutun kuɗin za a bai wa mutum ya je ya yi gininsa?
Ma’aikacin bankin
ya ce, “to bari in fara ba su amsa sannan in saurari wasu tambayoyin, sai ya ce
“amsar mai tambayar farko shi ne za ka samu muhallinka da zarar ka cika
dukkanin ƙa’idojin da a ke so a cika na neman rancen. Kuma za ka biya ne kafin
shekarunka na barin aiki ko kuma kafin shekarunka na haihuwa su kai sittin”.
Sai amsa ta biyu ki
na tambaya ne a kan kuɗin za a ba ka ko gidan za a sai maka? Wannan ya danganta
da abin da ki ka nema wato gida ki ka nema ko kuɗin, in gidan ne shi ma ya
danganta da wanda ki ka nema domin akwai gidaje masu bene akwai kuma ƙanana
marasa bene tun daga mai ɗaki biyu zuwa mai daɗi uku, kuma ba sa haura miliyan
sha biyar.
Akwai na ƙasa da
haka ya danganta da unguwar da gidajan suke. In kuɗin ne kuma to sai ya kasance
kina da fili mai ɗauke da sunanki da takarda ta gwamnati sannan sai banki ta yi
bincike ta tabbatar cewa tabbas filinki ne, sannan sai an je filin an ga cewa
tabbas kin ɗan fara wata alama ta ginin, sannan sai banki ya ba ki kashi
talatin daga abin da kika nema domin ki ci gaba da ginin. Haka kuma za a tura
ma’aikatanmu su duba su tabbatar kin yi abin da kika ce za ki yi sannan a ƙara
ba ki kashi talatin (30%), in shi ma kika gama a ka tabbatar kin yi ginin da
shi, to sai a cika miki ka so arba’in (40%) ɗin domin ki kammala ginin gidanki
ki shiga ki zauna ke da iyalinki, kuma za ki biya ne kafin ki cika shekaru
sittin da haihuwa ko kafin ki yi ritaya.
Domin duk wanda ya
cika shekaru sittin ya fita daga tsarin.” Haka suka shiga jero tambayoyi yana
gamsar da su da amsoshi, har kowa ya fahimci cewa lallai gata ne wannan banki
yake yi wa al’ummar wannan ƙasa, saboda ƙudurinsa na ganin kowa ya mallaki
muhalli.
*****
Malam Aminu ya
kalli Binta wadda ke cika ta na batsewa a kan ɗauke ƙafa da ya yi, sai dai ya
ce, ta yi haƙuri a duk lokacin da ta kira shi a waya. Ya ɗan tausasa murya ya
ce, “Haba Binta ya za ki juyo min ƙeya wani hali na shiga wanda in ba wani ikon
Allah ba batun auranmu ya sha ruwa kenan.” Binta ta waiwayo cikin sauri, tare
da faɗin “kana dai son ka yaudare ni ne kawai, ce min ka yi da ka kammala
muhallinka za mu yi aure”. Ya ce “Wannan labari ya canza Binta domin zancen da
nake miki yanzu wannan guri ya zama ba nawa ba, ashe gurin mallakin gwamnati
ne, tuni ta biya masu gurin kuma in da aka sayar mana nan ne maguda nan ruwan
birnin da za a gina zata biyo, shi ne aka nemi da mu kwashe bulallikanmu mu je
mu samu waɗanda suka sayar mana filin su biya mu.
Tuni mun gurfana a
gaban Alƙali da waɗanda suka sayar mana har an kai su gidan yari suna can suna
zaman kuɗinmu. Haƙuri na zo in ba ki Allah ya haɗaki da
wani wanda ya fini, tunda muhalli ya kufce. Muryar Binta na rawa ta ce “Kana nufin muhalli zai hana
mu aure? Ya ce, “ya ma hana, tun da kin san a haya nake zaune da iyalina
kuma sana’ata ƙarama ce.Binta cikin shassheƙar kuka ta ce ”Yanzu shi ke nan
ƙurunkus soyayyarmu?”. Ya ce “ In ba sa a ba an rufe babin ruf, ki yi haƙuri Binta
sannan ki ba ‘yan gidanku haƙuri, ni zan tafi.” Ba ta iya amsa masa ba,
sai ma bango da ta samu ta jingina domin ƙafafunta ba za su iya ɗaukar ta ba.
Ta na kallon shi ya wu ce har zai tsallaka kwatar da zai fita daga lungun ya
waiwayo ya ce “ Amma kar ki goge lambata, in wata damar ta samu za ki ji ni”.
******
Alhaji Musa Wada maƙoci
ne ga malam Aminu shi ne ya kawo masa labarin babban bankin bayar da lamuni na
ƙasa [FEDERAL MORGAGE BANK OF NIGERIA] bayan ya ji labarin abin da ya faru, ya
yi masa cikakken bayanin yadda zai yi adashan gata kuma ya samu mallakar
muhalli ko da mai ɗaki guda da falo ne. Cikin farin ciki ya sanar da Hauwa
komai, nan da nan suka soma tsara yadda za su fara tara kuɗin da zai rinƙa kai
wa duk wata ya sa a sabon asusun nasa da za a buɗe masa.
Hauwa tana ban ɗaki
ya kira Binta cikin nishaɗi ya ce, Masoyiyata wata damar ce ta sake samuwa,
ashe dai inda rai da rabo, domin wani maƙocin arziƙi shi ne ya yi min hanyar
adashin gata na mallakar muhalli daga wani banki masu taimakon talakawa”. Da ga
ɓangaren Binta ta amsa da Alhamdulillahi! Ni fa na ji a jikina za mu yi aure da
kai”.Ya ce “Binta in har kika ga ban aure ki ba, sai dai in ban mallaki muhalli
ba a duniya”. “In ko ka ga ka mallaki muhalli sai dai ko in mutuwa na yi!”
Hauwa ta katse shi tare da kai wa wayar hannun shi cafka. Ya kufce cikin tausassar
murya ya ce “ Gimbiyata ai in na mallaki muhalli ɓangarenki daban sai dai ki
sakata ki wala”. Ta yi murmushi ta ce
“To Allah ya ba mu cikin sauri domin haya bala’i ce, kishiya kuma abokiyar zama
ce”. Ya sa hannuwansa ya rufe fuskarsa cikin alamar kunya, ya ɗago kai ya ce “
Uwargida sarautar mata, gimbiya Hauwa’u Kulu Maijidda jagorar matan gidana ko
su nawa ne komai ta ce a yi shi za a yi.
Ƙarshe
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.