Citation: Umma Ado ABBAS (2021). Warwarar Tubalan Ginin Turken Waƙar Al’almajiri’ Ta Haruna Aliyu Ningi. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 9, Issue 1. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
WARWARAR TUBALAN GININ TURKEN WAƘAR’ALMAJIRI’ TA HARUNA ALIYU NINGI
Na
Umma Ado ABBAS
Tsakure
Wannan takarda ta yi nufin yin nazarin tubalan ginin turke da
Haruna Aliyu Ningi ya yi amfani da su a waƙarsa ta Almajiri wajen
isar da manufarsa ga masu sauraro. Takardar ta samu jagoranci daga mazahabar waƙar baka Bahaushiya ta Gusau (2015). An yi amfani da hanyoyin
bincike waɗanda suka haɗa da samo matanin waƙar kai tsaye daga wurin
Haruna Aliyu Ningi. Takardar ta fito da muhimman tubala guda takwas (8) waɗanda Haruna Ningi ya yi amfani da su wajen gina manufar waƙar da kuma isar da saƙonsa ga masu sauraro.
Keɓaɓɓun Kalmomi: Warwara, Tubali, Turke, Waƙa, Almajiri, Haruna Ningi
1.0 Gabatarwa
Waƙa hanya ce da ake amfani da ita wajen isar da saƙo cikin sauƙi. Wannan ne ma ya sa a duk lokacin da ake son
bayyana wani muhimmin saƙo ga al’umma, sai an bi ta hanyar waƙa. Za a fahimci haka idan aka yi la’akari da yadda mawaƙa suke taka rawa wajen bayyana manufar gwamnati da tallata wata
haja da sanar da bikin ɗaurin aure da fito da abubuwa na wayar da kan
al’mma da sauran abubuwan da suka shafi rayuwar yau da kullum. Gusau (2003, sh.
ɗiii) ya bayyana waƙar baka da cewa, “Zance
ne na hikima da azanci da yake zuwa gaɓa-gaɓa bisa ƙa’idojin tsari da daidaituwa a rere cikin sautin
murya da amsa-amon kari da kiɗa da amshi”. Shi kuwa Satatima (1999, sh. 24) ya
bayyana cewa waƙar baka ita ce, “Wadda ake rerewa don jin daɗi a ajiye ta a ka kuma a yaɗa ta da baka”. A wurin
Mainasara (2016, sh. 9) yana ganin, “waƙar baka wani zance
mai ƙunshe da azanci da ake shiryawa bisa wasu ƙa’idoji na musamman don isar da wata manufa ko saƙo ga al’umma”.
A wannan takarda an yi
nazari ne a inda aka fito da tubalan ginin turke da Haruna Aliyu Ningi ya yi
amfani da su a waƙarsa ta’Almajiri’ wajen isar da saƙonsa ga masu sauraro.
1.1 Taƙaitaccen Tarihin Haruna Aliyu Ningi
An haifi Haruna Aliyu Ningi ranar Talata 22/11/1972 a ƙauyen Rumbu da ke cikin ƙaramar hukumar Ningi ta
jahar Bauchi. Haruna ya yi karatun allo a wurin mahaifinsa wanda a wurinsa ne
ya sauke Alkur’ani, tare da karantar sauran littattafai waɗanda suka haɗa dai littattafan Fiƙihu da Hadisai da
sauran littattafai na addini. An saka Haruna a makarantar firamare ta garin
Rumbu daga shekarar 1977-1981. Ya samu nasarar shiga makarantar sakandire da
take garin Bura daga 1981 zuwa 1986. Haruna ya ci gaba da karatu mai zurfi a
makarantar Kimiyya da Fasaha da ke Ƙauran Namoda, a inda ya
samu shaidar Dufuloma a ɓangaren harkokin kuɗi (Financial Studies) a shekarar 1996. Bayan gama karatun ne kuma
sai ya faɗa harkar siyasa.
Haruna ya fara waƙa ne a shekarar 1996 a
lokacin siyasar UNCP da DPN. Shahararrun waƙoƙin Haruna su ne waƙar “PDP jam’iyata” da “Ku faɗa wa Obasanjo; Mu kan ba mu yarda ta zarce ba” da kuma “Shegiyar
uwa mai kashe’ya’yanta PDP” da sauransu. Haruna bai gaji waƙa ba domin mahaifinsa malami ne, to amma da yake Allah ya ƙaddara zai zama mawaƙi sai ya tsinci kansa a
cikin harkar. Haka kuma ba wanda ya koya masa waƙa, kawai dai Allah ne ya
haska tauraronsa, shi ya sa ma ba shi da wani wanda zai ce shi ne maigidansa a
harkar waƙa, sai dai abokan hulɗa kawai. Amma kuma akwai mutumin da yake ganin da Allah ya haɗa su, to da ya zama uban gidansa ko da kuwa bai koya masa komai
ba. Wannan mutumi shi ne Auwalu Isa Bunguɗu. Haruna makaɗi ne da yake aiwatar da waƙoƙinsa da kayan kiɗan zamani tare da’yan amshi a sitidiyonsa mai
suna Baushe Media da ke garin Bauchi (Muhammad, 2019, sh. 4).
2.0 Turke a Waƙar Baka
Masana da manazarta da dama sun yi rubuce-rubuce a kan ma’anar
turke. Daga cikinsu akwai, Gusau (2008, sh. 370) ya bayyana cewa turke na nufin, “Saƙon da waƙa take ɗauke da shi. Idan an ce saƙo kuma ana magana ne kan
manufar da ta ratsa waƙa tun daga farkonta har zuwa ƙarshenta: Wannan saƙon kuma yakan zo cikinta,
ba tare da karkacewa daga ainihin abin da ake zance a kansa ba. Ashe ke nan, saƙon da makaɗi yakan zaɓa ya gina waƙarsa, ya tauye kansa da
kansa ya zuba ɗiyanta bisa wasu zaɓaɓɓun kalmomi da za su doshi wata babbar
manufa ɗaya, shi ake kira turke”.
Abba da Zulyadaini, (2000, sh. 45) sun
bayyana jigo (turke a waƙar baka) da cewa: “Jigo[1] na nufin saƙon da mawaƙi yake so ya isar cikin waƙarsa ga jama’a”.
A nasa ra’ayin (Muhammad, 2012, sh. 65).
ya bayyana turke da cewa shi ne: “Saƙon da makaɗi yakan zaɓa ya gina waƙarsa, cikin tsari bisa wasu
zaɓaɓɓun kalmomi inda za a doshi
wata babbar manufa ɗaya, shi ake kira turke.”
Daga waɗannan ra’ayoyi na mabambantan masana, a iya cewa
turke na nufin manufar waƙa, wato saƙon da mawaƙi yake son ya isar ga masu sauraro.
2.1 Tubalan Ginin Turke
Tubalan ginin turke na nufin, wasu maganganu
da aka bi aka ƙuƙƙulla waƙa da su don ta ƙara tsawo, amma ba su ne
babbar manufar waƙar ba (Gusau, 2003, sh.
30).
Har ila yau, Gusau (2008, sh. 374) dangane da ma’anar
tubali ya ci gaba da cewa:
A waƙoƙin baka na Hausa akan jajjefa wasu ƙananan maganganu na daban ƙari a kan wasu manyan manufofin
da aka gina su a kansu. Makaɗan baka sukan yi amfani da waɗannan ƙananan zantuka ne su ƙuƙƙulla waƙa don ta ƙara tsawo, sai dai lalle ne
su dace da babbar manufar waƙa. Sannan kowanne babban turke, akwai
nau’o’in ƙananan turakun da suka dace
da shi
Satatima (2009, sh, 82) da ya zo bayyana ma’anar tubali cewa ya yi:
Cikin hikima ne mawaƙan baka sukan zaɓi turken waƙarsu su kuma ƙayatar da shi ta amfani
da ƙananan turaku wato tubalan
ginin turke, ko kuma raɓa dannin turke kamar yadda wasu sukan kirasu. Alal misali
idan waƙa turkenta yabo ne, to sai
ka ga mawaƙi ya taɓo nasaba da riƙo da addini da kyauta ya
lanyace wannan yabo nasa da shi.
Dangane da ma’anonin da masana suka kawo, a
iya cewa tubali na nufin ƙananan saƙonni da mawaƙan baka kan yi amfani da su
a cikin waƙoƙinsu domin taimakawa wajen
fito da babban turke. Kaɗan daga cikin tubalan akwai yabo, zambo, habaici, zuga, kirari da
makamantansu.
2.2 Bayani a Kan Almajiri
Asalin kalmar’Almajiri’ ta samo asali ne daga harshe Larabci
wato ‘‘Al-muhajiri’ da take nufin wanda ya yi hijira daga wani
wuri zuwa wani wurin. Wannan shi ne sunan da ake kiran Sahaban Manzo (S.A.W) da
suka yi ƙaura daga Makka zuwa Madina. A ma’ana ta zahiri
kuwa almajiri shi ne mutumin da ya ƙaura daga garinsu zuwa
wani wuri da nufin ya yi karatu, tare da sauke Kur’ani mai tsarki. Wannan tsari
na almajiranci ya fara tun lokaci mai tsawo da ya wuce a inda Hausawa da Fulani
suke tura’ya’yansu makarantar allo don su haddace Alkur’ani da sauran littattafan
ilimi (Mashema da Idris da kuma Musa, 2018, sh. 1).
Mashema da Idris da kuma Musa (2018, sh. 1) suka ci baba da cewa,
“Tasirin karatun Alkur’ani na almajiranci a ƙasar nan ya fara ne
a ƙarni na goma sha ɗaya, a wannan lokaci masarautun Borno da na Sakkwato suka samar da
makarantun allo a inda ake karantar da karatun Kur’ani. Masarautun nan (Borno
da Sakkwato) sun taka rawa wajen koyar da Kur’ani. Da yawa daga cikin
mashahuran malaman arewacin ƙasar nan da kuma
wasu ɓangarori na Afirka sai da suka yi karatu a irin
waɗannan makarantu na allo kafin su zama’Hafizai’
(waɗanda suka haddace Kur’ani).
3.0 Hanyoyi da Dabarun Gudanar da Bincike
Kowane irin bincike na ilimi da za a gudanar akan zabi hanyoyi da
dabaru da ake yin amfani da su domin ganin wannan bincike ya kai ga samun
nasara. Hanyoyi da dabaru da aka yi amfani da su wajen gudanar da wannan
bincike sun haɗa da samo matanin waƙar, kuma daga bisani aka juye ta a rubuce domin samun sauƙin nazari. An tattauna da makaɗi Haruna Aliyu Ningi a
inda aka yi masa tambayoyi a kan abin da ya shafi waƙar.
Ningi ya bayyana cewa ya yi wannan waƙa ne saboda ya jawo hankulan Gwamnoni su gane cewa hana
almajiranci ba shi ne mafuta ba. Ya aiwatar da waƙar ne a situdiyonsa mai
Suna Baushe Media da ke garin Bauchi. Waƙar tana da ɗiya guda goma sha uku (13).
4.0 Tubalan Waƙar Almajiri ta Haruna
Aliyu Ningi
Haruna Aliyu Ningi ya yi amfani da tubala mabamabanta a waƙar almajiri domin samun sauƙin isar da saƙon da ta ƙunsa ga masu sauraro. Daga cikin tubalan da ya
yi amfani da su akwai:
4.1 Mai da Martani
Martani na nufin magana ko jawabi a kan wani abu da wani ya
yi. Dubi yadda Haruna Aliyu Ningi ya mayar wa da gwamnoni maratani a kan ƙudurinsu na hana almajiranci a jahohinsu. Ga abin da yake cewa:
Jagora: Ni almajiri ne,
: Kai ma almajiri ne,
: Kuma almajirai ne,
: Ai waƙar almajiri ce,
: Gwamnoni kun ji kunya,
: Kuna sukar almajiranci.
: Amma kuma ga jaharku,
: Ana buga harkar karuwanci.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 1).
A nan Haruna ya mayar wa da gwamnonin Arewacin Nijeriya
martani ne a kan ƙudirinsu na hana bara (almajiranci) a jahohinsu,
alhalin sun kyale abubuwan da suka fi almajirancin illa kamar su karuwanci ana
gudanar da su a jahohinsu. Haruna ya fito ƙarara ya nuna wa
gwamnonin cewa sun ji kunya, sun bar abubuwan da suka saɓawa al’adu da ɗabi’un Hausawa da ma
addinin Musulunci ana gudanar da su a jahohinsu, amma kuma suna ƙoƙarin hana almajiranci.
4.2 Asali
CNHN (2006, sh. 20) ya bayyana kalmar asali da cewa tana
nufin “mafari ko tushe ko salsala”. Haruna Ningi a ƙoƙarinsa na fito da manufa da saƙon waƙar ya bayyanaa abin da ake nufi da almajiranci,
da yadda aka sami sauye-sauyen zamani a kan tsarin na almajiranci, a inda yake
cewa:
Jagora: Farko ga tambaya mu
ji menene almajiranci?
: Daga kan almajiri aka san kalmar almajiranci,
‘Y/Amshi: Shi ko almajiri
mabiɗin ilimi ne in ka gan shi,
: Kuma ko da taimako ne sai in kai ra’ayi ka ba shi.
Jagora: Wasu ne suka ɓata harkar,
: Masu jidon yara ƙanana,
: Su saka su bara a titi,
: Wai haka ɗin sun ɗau amana,
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 3-4)
A nan makaɗi Haruna Ningi ya fito da asalin menene
almajiranci ta samu ne daga almajiri, sannan kuma almajiranci hark ace ta neman
ilimin addinin Musulunci. Haka kuma ya ci gaba da sanar da masu sauraro cewa
almajiri bai tilasa wa mutane su taimaka ma sa ba, har sai in suna da ra’ayi na
su taimaka masa. Amma sai wasu suka ɓata wannan harka ta
almajirancin a inda suke ɗauko yara ba tare da damuwa da ci da sha da
makwancinsu ba. Suka sake su kawai a gari kwararo-kwararo suna bara.
4.3 Shawara
CNHN, (2006, sh. 411) ya bayyana ma’nar shawara da nasiha ko
tattaunawa a kan wasu matsaloli tsakanin mutum biyu ko fiye. A ƙoƙarin Haruna na isar da saƙon waƙar ya ba da shawara a kan yadda za a gyara
harkar almajiranci kamar haka:
‘Y/Amshi: E! Lalle na
fahimta ta nan haka illar ta fara,
: Sai dai ko mai ya faru abin da ya dace sai a gyara,
: Kwarai!
Jagora: Ni ma na
yarda a gyara ya fi ya fi a ce a rusa,
: Gyaran abu in ya ɓaci a nan sai mai hange
na nesa,
: Domin in za a gyara za ai don an ba da amsa.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 5)
A nan Haruna yana ba wa gwamnoni shawarar cewa duk lallacewar da
harkar almajiranci ya yi, bai kamata a hana yin sa ba, maimakon a hana gwanda a
zauna a yi nazarin abubauwan da suka sa harkar ta lallace a gyara su. Haka kuma
yana nuna in za a yi gyaran sai an kalli harkar da idon basira kafin a kai
gyara ta.
4.4 Nuna Takaici
CNHN (2006, sh. 420) ya bayyana takaici da jin haushi wanda ɓacin rai yakan kawo. Haruna Ningi ya nuna takaicinsa na yadda
gwamnoni suka kau da kansu a kan abubuwan alfasha da ake aikatawaa a jahohinsu,
suka tsangwami harkar almajiranci. Ga abin da ya ce:
Jagora: Abin ne babu tsari,
: Babu kishi,
: Babu darajawa,
: Ba mutunci,
: Mun yarda bara a
daina,
: Tun da a tsari ta
haramta,
: Amma almajiranci kar a
hana don ya halarta.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 7)
A wannan misalin da aka kawo na ɗan waƙar da ya gabata, Haruna Aliyu Ningi ya nuna
takaicinsa a kan yadda gwamnoini suke son su kawo tasgaɗo a kan harkar almajiranci alhali ga abubuwan alfasha nan ana
aikatawa, amma ba ɗau mataki a kai ba. Haka kuma ya nuna yadda yake
ganin rashin tsari da kishi, sannan kuma ba daraja da mutunci a cikin hana
harkar almajiranci. Tsari a nan na nufin rashin dacewa. Kishi kuwa shi ne
rashin tsayawa da nuna ƙwazo a kan wani abu. Daraja kuwa tana nufin
rashin girmamawa. Ita kuwa kalmar mutunci a nan tana nufin halin girma. Haruna
ya yi amfani da waɗannan kalmomin ne duk don ya nuna takaicinsa a
kan yadda gwamnoni suka tsangwami harkar almajiranci.
4.5 Habaici
Habaici shi ne yin amfani da wasu kalmomi a fakaice don a
musgunawa wani, a ɓata masa rai, ya ji haushi. A wajen yin habaici
ba a fitowa fili a nuna da wanda ake yi, sai dai a yi amfani da kalmomin
sakayawa irin su’wane’ da’wani’ da’wasu’ da sauransu (Muhammad, 2019, sh 121).
Ga misali inda Haruna Aliyu Ningi ya yi habaici a waƙarsa ta Almajiri kamar haka:
Jagora: Gwamnonin nan da
sata sun ɗara ɓeraye aradu,
: Su dai su gani
su ɗauka ,
: Hakkin kowa su taka,
: Wani gwamna
har da duka,
: Wai ai shi ba yi
shakka,
: Sun girma a cin amana,
: Masu idanun dubarudu.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 8)
A ƙoƙarin Haruna Ningi na isar da saƙon waƙarsa, a nan ya yi wa wani daga cikin gwamnonin
Arewa habaici, a inda yake nuna masu sauraro cewa har dukan mutane yake
yi.
4.6 Yabon Ubangiji
Yabo shi ne ambaton kalmomin sambarka da
nufin nuna amincewa da hali ko wani abin da mutum ya yi nagari. Ko kuma a iya
cewa yabo wani lafazi ne da ake yi ga wani mutum domin a nuna halayensa da
siffofinsa kyawawa da cewa abin so ne kuma abin ƙauna ne. (Gusau, 2008, sh. 376). Ubangiji kuwa shi ne mahaliccin komai, wato Allah (CNHN, 2006,
sh. 14). Ke nan yabon ubangiji shi ne yin amfani da lafuza masu daɗi wajen nuna girmansa da buwayarsa da adalcinsa da sauransu.
Haruna Aliyu Ningi ya yi amfani tubulin yabaon ubangiji wajen gina turken waƙar kamar haka:
Jagora: Shi Allah adali ne,
: Kuma mai son mumini ne,
: Mai ƙyamar kafiri ne,
: Bai kunyar fasiƙi ne.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 11)
A wannan ɗan waƙa da aka kawo a sama
Haruna Aliyu Ningi ya yabi Allah (S.W.T) ha hanyar yi masa kirari, ya fito da
sifofinsa, ta amfani da kalmomin yabo waɗanda suka haɗa da adali da son muminai da ƙyamar kafir, sannan kuma
ba ya kunyar faskiƙi. Adali na nufin mai adalci. Shi kuwa mumini
yana nufin wanda ya ba da gaskiya da Allah, ya kuma ke bin dokokin Musulunci.
Kafiri kuwa shi ne wanda bai yarda da addinin musulunci ba. A inda kuma yake
nufin ashararin mutum ko mai yawan yin aikin assha. Haruna Aliyu Ningi ya yi
amfani da waɗannan kalmomin ne, ya yabi Allah ta hanyar fito
da wasu siffofinsa.
4.7 Addu’a
CNHN (2006, sh. 3) ya bayyana addu’a da roƙon Ubangiji. Ke nan addu’a ita ce roƙon Allah ya biya mutum
buƙatarsa. Haruna Aliyu Ningi ya yi amfani da tubulin addu’a a ƙoƙarinsa na miƙa saƙon waƙar ga masu sauraro. Ga abin da yake cewa:
‘Y/Amshi: Addu’a ce
za mu yi ta,
: A kan kowane azzalumi ne,
: Ko da kuwa malami ne,
: Ko da mai unguwa ne,
: Sarki, attajiri ne,
: Ko mai mulkin jaha ne,
Jagora: Ko mai mulkin ƙasa ne,
: Ko ko jami’in tsaro ne,
: Kowa ya rufe gun ibada,
: Saboda Coronar kasuwanci,
: In har mai shiryiwa ne,
: Jirgin sama in yah au, ka kaɗo wannan jirgin ya ƙone,
: In mota ce ya hau ka kifar wannan mota ta ƙone,
: In babur ne ka sa shi ya kama wuta shi ma ya ƙone,
: In bai da abin hawa, a cikin ɗaki nai ya ƙone.
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 12)
A nan Haruna Aliyu Ningi ya yi addu’a ne a inda yake roƙon Allah da ya hukunta duk wanda yake da hanu wajen hana yin
Sallah a watan Azumi saboda cutar Corona, ko da kuwa wannan mutumin malami ne
ko mai unguwa ko sarki ne shi ko mai kuɗi ne ko kuma gwamna ko
shugaban ƙasa. Haka kuma Haruna ya yi masa addu’ar shiriya
in har zai shiryu, in kuma bai shiryu ba Allah ya hukunta shi da irin abubuwan
da ya jero a ɗiyan waƙar tasa.
4.8 Faɗakarwa
Faɗakarwa na nufin gargaɗi ko nasiha ko kuma
ilmantarwa ko tarbiyantarwa tare da wayar da kai ko hannunka-mai sanda
gami da tunasarwa (Kurawa, 2019, sh.
88). Ga abin da Haruna yake cewa a wani misali na ɗan waƙar kamar haka:
Jagora: A hana mana jam’i a
cikin Ramadan ai isgili ne,
: Saƙon farko ku ji shi,
: Kafin Coɓid 23 ta iso,
: Mu ci…... Uhmmmmm!!!
(Haruna Ningi: waƙar’Almajiri’ ɗa na 13)
A nan Haruna yana yi wa waɗanda suka hana yin jam’i
a watan Azumi saboda cutar Corona Ɓirus hanunka-mai-sanda,
a inda yake gaya musu cewa abin da suka yi isgilanci ne, sannan kuma za su gane
kuransu a zaɓen shekara ta 2023.
5.0 Kammalawa
Kamar yadda bayanai suka gabata a wannan takarda, an yi nazari ne
dangane da yadda Haruna Aliyu Ningi yake amfani da mabambanta tubala waɗanda suka haɗa da mai da martini da asali da nuna takaici da
shawara da habaici da yabon Ubangiji da addu’a kuma faɗakarwa wajen isar da manufar waƙarsa. A cikin takardar
an kawo bayani kan ma’anar turke da tubalan ginin turke da kuma bayani a kan
almajiri. An yi amfani da hanyoyi da dabaru waɗanda suka haɗa da samo matanin waƙar da hira da makaɗi Haruna Aliyu Ningi. Haka kuma an kawo misalai na waɗannan tubala tare da yin sharhinsu.
Manazarta
Abba, M. &
Zulyaidaini, B. (2000). Nazari kan waƙar baka ta Hausa. Gaskiya Corporation Company.
CNHN, (2006). Ƙamusun Hausa na jami’ar Bayero. Ahmadu Bello University Press.
Gusau, S. M.
(2003). Jagoran nazarin waƙar baka. Benchmark Publishers.
Gusau, S.M. (2008). Waƙoƙin baka a ƙasar Hausa:
yanaye-yanayensu da sigoginsu. Benchamark Publishers.
Gusau, S.M.
(2011). Adabin Hausa a sauƙaƙe. Century Rearch and
Publishers.
Gusau, S. M.
(2014). Waƙar baka bahaushiya, Bayero University.
Gusau, S. M. (2015
A). Abdu Karen Gusau. Century Research and Publishing.
Haramde, M. M. (2014).
The practice of almajiri: Prospect and socio-medical challenges in Northern
part of Nigeria. Journal of African studies and Deɓelopment, 6 (7), 128-131.
Hussaini, B.
(2009). Haruna Aliyu Ningi da wasu waƙoƙinsa. Ramadan Press.
Kurawa, M. A.
(2019). Nazarin turke da awon baka a waƙoƙin Asharalle a Jahar Katsina. [Kundin digiri na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeirya, Jami’ar
Bayero, Kano
Lawal, N. (2016). Nazarin
waƙoƙin makaɗan bege na Hausa. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Jami’ar Bayero, Kano
, B. L. & Idris, A. I. & Musa, Y. (2018). The chellenges
of amajiri system of education to social peace Mashema in Nigeria: A
cross-sectional inɓestigation. International Journal of Innoɓatiɓe Research and Adɓance Studies, 5 (8),
44-50.
Muhammad, A.S. (2012). Nazarin
ayyukan makaɗa Sa’idu Maidaji Sabon Birni (1938-2000). [Kundin Digiri
na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da
Afrika. Jami’ar Ahmadu Bello,
Zariya
Muhamamd, H. I.
(2019). Nazarin adon harshe a waƙoƙin sarauta na Haruna Aliyu Ningi. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya. Jami’ar Bayero, Kano.
Satatima, I. G. (2009). Waƙoƙin ɗarsashin zuciya na makaɗan baka. [Kundin digiri na Uku]. Sashen
Koyar da Harsunan Nijeirya, Jami’ar Bayero, Kano
Saulawa, B.S. (2017). Nazarin turken
yabo a waƙoƙin Hafsatu Garba Nijar. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano
Taiwo, F. J. (2013).
Transforming the almajiri education for the benefit of Nigerian society.
Journal of Education and Social Research, 3 (9), 67-72
Usman, A. (2017). Tarkakken
nazarin wasu waƙoƙin Sadiƙ Zazzaɓi. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya. Jami’ar Bayero,
Kano
Usman, H.S. (2016). Nazarin turken
ta’aziyya a waƙoƙin Dr. Mamman Shata Katsina. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Rataye na Ɗaya: Matanin Waƙar Almajiri
Jagora: Ni almajiri ne,
: Kai ma almajiri ne,
: Kuma almajirai ne,
: Ai waƙar almajiri ce,
: Gwamnoni kun ji kunya,
: Kuna sukar almajiranci.
: Amma kuma ga jaharku,
: Ana buga harkar karuwanci.
Jagora: E! Allah Rabbi
Allah,
: Da ka sa mu mu dinga Sallah,
: Kai wa Manzo kamala,
‘Y/Amshi: Kwarai,
Jagora: Da Sahabbai nai
jimilla,
‘Y/Amshi: Na’am,
Jagora: Ka hana mu da yin
baɗala,
‘Y/Amshi: Kwarai,
Jagora: Maganar ba ƙila-ƙala,
: Ga zance sala-sala,
‘Y/Amshi: Faɗi,
Jagora: Da na ɗauko ba kasala,
: Wa za ya tayan in cilla,
: Ya iso har gun amilla,
: Gwamnoni kun ji kunya,
: Kuna sukar almajiranci.
: Amma kuma ga jaharku,
: Ana buga harkar karuwanci.
‘Y/Amshi: Subhanallah,
Jagora: E!
Jagora: Farko ga tambaya mu
ji mene ne almajiranci?
: Daga kan almajiri aka san kalmar almajiranci,
‘Y/Amshi: Shi ko almajiri
mabiɗin ilimi ne in ka gan shi,
: Kuma ko da taimako ne sai in kai ra’ayi ka ba shi.
Jagora: E!
Jagora: Wasu ne suka ɓata harkar,
: Masu jidon yara ƙanana,
: Su saka su bara a titi,
: Wai haka ɗin sun ɗau amana,
‘Y/Amshi: E! Lalle na
fahimta ta nan haka illar ta fara,
: Sai dai ko mai ya faru abin da ya dace sai a gyara,
: Kwarai!
Jagora: Ni ma na yarda Yaya
a gyara ya fi a ce a rusa,
: Gyaran abu in ya ɓaci a nan sai mai hange
na nesa.
Jagora/’Y/Amshi: Domin in
za a gyara za ai don an ba da amsa.
Jagora: Makarantun ne na
boko wa ya gina musu ne y aba su?
‘Y/Amshi: Ah to!
Jagora: Gwamnati ce ta yi
su,
: Sannan da kuɗin ƙasarsu,
‘Y/Amshi: Kwarai!
Jagora: Bayan haka tai
asusu,
: Da ta ɗauki ma’aikata da duka wata sai ta biya su,
‘Y/Amshi: Kundin
mulkin ƙasarsu,
: Yin zaɓi shi ya ba su,
: Amma almajirai aka ƙi su a kan sun zaɓi nasu,
Jagora: Ayya!
‘Y/Amshi: Amma kuma
Jonathan ya yarda da su ɗin’yan ƙasa ne,
: Kuma dole suna da hakki za a kula su kamar su wane,
: Bayan yai makarantu sai suka wai kyale arne,
: To ai su kafirai ne sun ɗara kowane arne,
‘Y/Amshi: Kwarai!
Jagora:’Yan kut……..
‘Y/Amshi: Haruna tsaya haka
ban da zagi.
Jagora: Abin ne babu tsari,
: Babu kishi,
: Babu darajawa,
: Ba mutunci,
: Mun yarda bara a
daina,
: Tun da a tsari ta
haramta,
: Amma almajiranci kar a
hana don ya halarta.
‘Y/Amshi: Ɗanningi bugu da ƙari su ma sai sun daina sata,
: Domin illa ta sata ta
fi bara girman haramta,
Jagora: Ka gani.
Jagora: Gwamnonin nan da sata sun ɗara ɓeraye aradu,
: Su dai su gani
su ɗauka ,
: Hakkin kowa su taka,
: Wani gwamna har da
duka,
: Wai ai shi ba yi
shakka,
: Sun girma a cin amana,
: Masu idanun dubarudu.
‘Y/Amshi: Ai na gane shi mungu ɗan kuturu mai hura hanci,
: Don na ji yana faɗin sun rusa shirin almajiranci,
Jagora: Amma kuma ga jaharsa,
: Ana buga harkar
karuwanci,
: Shan maye ga kawalci,
: Bayan harkar dabanci.
Jagora: Sun zo da Corona Ɓirus sun hana kowa
kasuwanci,
: Domin sun zo da nasu
su Da’u iyayen fasiƙanci,
: Sun kulle gidan ibada
ka ji irin ɗanyan hukunci,
: Ku ma sun kulle
kasuwanni, sun rufe gun harkar fatauci,
: Sun bar jama’a da
yunwa
: Ba sunna babu aya,
: Ba sisi babu hanya
: Ba sa da Corona jinya,
: Wannan abu ya ƙazanta an shiga mummunan talauci,
Jagora: Shi Allah adali ne,
: Kuma mai son mumini ne,
: Mai ƙyamar kafiri ne,
: Bai kunyar fasiƙi ne.
‘Y/Amshi: Addu’a ce za mu
yi ta,
: A kan kowane azzalumi ne,
: Ko da kuwa malami ne,
: Ko da mai unguwa ne,
: Sarki, attajiri ne,
: Ko mai mulkin jaha ne,
Jagora: Ko mai mulkin ƙasa ne,
: Ko ko jami’in tsaro ne,
: Kowa ya rufe gun ibada,
: Saboda Coronar kasuwanci,
: In har mai shiryiwa ne,
: Jirgin sama in yah au, ka kaɗo wannan jirgin ya ƙone,
: in mot ace ya hau ka kifar wannan mota ta ƙone,
: In babur ne ka sa shi ya kama wuta shi ma ya ƙone,
: In bai da abin hawa, a cikin ɗaki nai ya ƙone.
Jagora: A hana mana jam’i a
cikin Ramadan ai isgili ne,
: Saƙon farko ku ji shi,
: Kafin Coɓid 23 ta iso,
: Mu ci……. Uhmmmmm!!!
[1] Jigo ko turke suna magana ne a kan manufa ko saƙon da waƙa ta ƙunsa. Jigo kamar yadda
masana suka kawo ya shafi rubutacciyar waƙa ne, shi kuwa turke ya
shafi waƙar baka kamar yadda Gusau (2003) ya kawo. Amma a
wurin Abba da Zulyadaini (2000) sun kalli jigo a manufar rubutacciya da kuma waƙar baka.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.