Ticker

6/recent/ticker-posts

Tsakanin Masu "Jarhi" Da Kuma Masu Sakaci Da Guluwwi A Inkarin Jarhin

Kamar yadda aka sani akwai wadanda suka kirkiri sabon Manhaji suka kira shi da sunan Manhajin Salafiyya, wato shi ne amfani da wani Fanni a Ilmin Hadisi wanda aka sani da sunan "Jarhi da Ta'adili", wanda suke nufin magana a kan Malamai da masu da'awa, da sukarsu, sannan yanke hukunci a kansu na Bidi'antarwa da hana fa'idantuwa da su (Tahzeeri). To abin har ya kai ga GULUWWI, na sukar wadanda ba su cancanci suka ba, da bidi'antar da wadanda ba su cancanci bidi'antarwa ba. A cikinsu har akwai wadannan har GULUWWIN nasu ya kai ga Bidi'antar da Imam Abu Hanifa ko ma hukunci fiye da haka.

Ta daya hanun kuma, akwai wadanda suka saba ma wadannan, wadanda suke SAKACI ba sa sukar 'Yan Bidi'a, har suka yi GULUWWI, suke inkarin sukar wadanda suka cancanci sukar, ko inkarin sukar mutane da suke girmamawa, ko da kuwa mutanen da aka soka din sun cancanci suka da bidi'antarwa. Irin wadannan SAKACINSU da GULUWWINSU a sukar "Jarhi" har ya kai ga inkarin sukar irin su Sayyid Qutub, wanda ya shahara da Akidun Khawarijawa.

To kullum shi tafarki madaidaici yana nan ne a tsakanin GULUWWI da SAKACI. Wannan ya sa Malamai ba su gushe ba suna sukar duka hanyoyin guda biyu. Daga cikin wadanda suka yi irin wannan suka akwai Dr. Abdallah al-Qarniy, a wata "Maqala" da ya rubuta mai ban sha'awa, wacce za mu kawo muku fassaranta kamar haka:

Dr. Al-Qarniy ya ce:

Akwai wasu Ginshikai guda biyu na Addini masu girma, wadanda ya kamata a mai da hankali wajen kiyaye su, da kuma hada su ana aiki da su a tare, ba tare da wuce iyaka ba, kuma babu gazawa da sakaci.

Na farkonsu shi ne: Riko da Sunna, da ba ta kariya daga dukkan abin da ya saba mata, na Tahrifi da Tawili masu batar da mutane daga hanya, da kuma Bidi'o'i kirkirarru.

Na biyun kuma shi ne: Kokari a kan hada kan Musulmai da haduwarsu a kan gaskiya da nisantar duk abin da zai kai ga rabuwar kawunansu.

Amma kuma an samu matsala a wajen wasu mutane wajen hada wadannan ginshikai guda biyu da yin aiki da su a tare. Daga cikinsu akwai wadanda suka yi GULUWWI wajen tabbatar da Riko da Sunna da nisantar 'Yan Bidi'a, ta yadda suka fahimci wannan ginshikin ba a bisa hakikaninsa a Shari'a ba. Wanda hakan ya kai su ga wuce iyaka wajen yin hukunci a mas'alolin da za a iya yin IJTIHADI a cikinsu, da daukarsu a matsayin Bidi'o'i. Daga nan kuma suka ketare zuwa ga yin hukunci ga wanda ya aikata su da cewa; shi DAN BIDI'A ne. Sa'annan ba su kiyaye hukunce-hukuncen kauracewa Dan Bidi'a ba, da abin da yake lazimtawa na kiyaye Maslaha da Barna. Don haka sai wannar matsaya tasu ta haifar da raba kan Musulmai, da yaduwar kiyayya a tsakaninsu. Kai, harinsu na farko ya fiskanci Malamai masu yawa, wadanda suka saba musu a GULUWWINSU.

Don haka sai aka samu watsuwar raddodi da tattaunawa masu zurfi wadanda ba sa gadar da ilimi ko tsoron Allah ko samun shiriya, kawai sun zama sababi ne na kawar da mutane masu yawa daga kokari wajen neman ilimi mai amfani.

Kai, har wannan ta'adin nasu ya kai ga kafirta wasu Malamai jagororin al'umma a ilimi, kamar Imam Abu Hanifa (ra), suka danganta masa abin da bai inganta daga gare shi ba, ko kuma ba su fahimce shi a yadda yake ba. Da wannan sai suka saba ma abin da al'umma gaba dayanta ta sani - ba ma Malamai kadai ba - na falalarsa da matsayinsa da jagorancinsa a Addini, cewa; yana da kyakkyawan ambato a cikin al'umma. Allah ya ki, Muminai sun ki - kuma su ne shaidun Allah a bayan kasa - a ce: wanda ya kasance Kafiri ko Fasiki ya samu wannan matsayi da Abu Hanifa ya samu a cikin al'umma.

Manhajin Ahlus Sunna ya barranta daga masu wannan Guluwwi da kuma Manhajinsu. Kamar yadda Shaikhul Islami ne ya fadi a kan wadanda suka kafirta Abu Hanifa da ire-irensa cikin Limaman Muslunci, cewa wannan ra'ayin: ((Jinsin Akidar Rafidha 'Yan Shi ne, wadanda suke kafirta Sahabban Annabi (saw) sai 'yan kadan daga cikinsu, da jinsin Akidar Khawarijawa wadanda suke kafirta Usman da Aliyu bn Abi Dalib, da masoyansu cikin Musulmai)).

Kuma kamar haka wadannan suka afka cikin kafirta gamayyar wasu Kungiyoyin Musulmai, kamar yin hukunci ga Asha'ira cewa; su kafirai ne, sun fita daga Kungiyoyin Musulmai, kuma suka yi ikirarin sun dauko hakan ne daga wasu maganganun Salaf, suka dogara a kan abin da ya zo daga wasu Malamai na hukuncin da suka yi wa 'Yan Jahmiyya, sai suka manta da ka'ida a wannar mas'ala, ita ce; kayyade hukunci sakakke ta hanyar tabbatar da sharudan kafirtawa da koruwan abubuwan da suke hana a kafirta Musulmi, da cewa; Akida ko ra'ayi zai iya zama kafirci, amma ba za a yanke hukuncin kafircin a kan wanda yake da ita ba ba tare da an tabbatar da rashin jahilci da shubuha abin lura ba.

Wannan shi ya sa dole a yaye hada-kashi da wadannan suke yi, a yi bayanin jahilcinsu, da raddin abin da suka kirkira na wadannan abubuwa masu bukatar dalili, bisa da'awar ba da kariya ga Sunna da kiyaye ta, da bayyana abin da Malamai suka tantance na banbancin da ke tsakanin kafirtawa a sake, da kuma kafirta mutum sananne. Kuma batattun maganganun da suka danganta su ga Salaf ya kamata a yi bayanin bacinsu. Haka kuma kuskuren wani Malami ko Ijtihadinsa na kuskure, wanda suka dogara a kansa shi ma wajibi ne a yi bayanin kuskurewarsa, saboda abin da Malami ya yi kuskure, ya saba ma Jama'ar Malamai bai halasta ya kasance hujja ba, wacce za ta sa ya karkace daga Tafarkin Ahlus Sunna ya juya baya wa hakikaninsa.

Sai kuma aka samu wani bangare ya saba ma wadannan, yayin da suka ga GULUWWIN wadannan a Bidi'antarwa da Kafirtawa akwai zalunci a cikinsa, da abin da suka kirkira a tsakanin Musulmai na rarrabuwan kai da barna, duka da sunan Da'awa zuwa ga Sunna da riko da Maganganun Salaf, sai suka kalu-balance su da wani GULUWWIN, guluwwin kiyaye hadin kan Musulmi, don kar a samu rarrabuwa da sabani. Har lamarin ya kai su ga cewa; karkacewar da aka samu a cikin Kungiyoyin Bidi'a a Ginshikan Akida, -wai- kamar irin sabani ne na Fiqhu, wanda za a iya yinsa a Mas'alolin Hukunce-hukuncen Aiki, har suka yi ikirarin cewa; akwai tsanani da guluwwi a cikin abin da Malamai suka karrara na bayanin Ginshikan Akida da raddinsu da inkari ga 'Yan Bidi'a, a cewarsu: sabani a cikin wadannan Ginshikan kusa yake da sabani a lafazi kawai ba a ma'ana ba.

Har wasu daga cikinsu suka wuce makadi da rawa suka yi watsi da ka'idar Manhajin Ahlus Sunnati wal Jama'a wacce ta banbanta da ita daga Manhajin 'Yan Bidi'a. Suka yi ikirarin -wai- ita gaskiya a watse take a tsakanin dukkan kungiyoyin Musulmi, duk mai neman gaskiya zai iya samunta da kokarinsa ba tare da bin Manhajin Ahlus Sunna ba. -Wai- mutum zai iya samun sashen gaskiya a wajen wata kungiya, wani sashen kuma a wajen wata kungiyar daban, ba tare da an samu wata Kungiya guda daya wacce take kan tsantsar gaskiya ita kadanta ba. Wannan tunani ya kai ga har wasu suna kira ga komawa zuwa ga Musluncin kafin sabani. Sai suka wuce iyaka ta yadda suka sanya abin da Malamai suka tabbatar suka yi Ijma'i a kansa (Ginshikan Akida) yana cikin gamayyar Akidun Kungiyoyin da ba sa lazimtar kowa. Suka nuna cewa; babu banbanci a wajensu tsakanin Ahlus Sunna da wasunsu 'Yan Bidi'a.

Mafita daga wannan rikita-rikita da baraka a fahimta da tunani da aka samu a wajen wadannan bangarori biyu masu warware juna shi ne riko da Manhajin Ahlus Sunnati wal Jama'a, wanda ya tsayu a kan Ilmi da Adalci. Da shi ne wadancan Ginshikai guda biyu (Riko da Sunna, da ba ta kariya, da kuma Kokari a kan hada kan Musulmai) za su tabbata, ba tare da GULUWWI da SAKACI ba, da kula da cewa; kar riko da daya daga cikinsu ya kai ga rasa dayan nasu. Kamar yadda GULUWWI a sabani na halas bai halasta ba, kuma yana cikin sababbin Bidi'o'i, da abin da ke biyo bayan haka na hukunce-hukunce na zalunci, wanda shi ma bai halasta ba, to haka kuma SAKACI ma bai halasta ba, sakaci a mas'alolin da aka yi Ijma'i a kansu (Mas'alolin Akidar Ahlus Sunna), da mayar da su mas'alolin da ya halasta a yi sabani a cikinsu, da abin da yake biyo bayan haka na sakaci da lamarin Bidi'o'i karkashin abin da ake kira -wai- hadin kan Musulmi, shi ma bai halasta ba.

To wannan shi ne bayanin Dr. Qarniy, inda ya zargi duka bangarorin biyu, saboda kowanensu ya bar Ginshiki daya daga cikin Ginshikai guda biyu na Addini: (Riko da Sunna, da ba ta kariya, da kuma Kokari a kan hada kan Musulmai), kuma ya yi bayanin hanya madaidaiciya shi ne hada wadannan ginshikai guda biyu a yi aiki da su a tare, ba riko da daya a yi watsi da daya ba.

Insha Allahu a comment na farko zan sako bayanin Dr. Qarniy a cikin harshen Larabci.

Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani

Post a Comment

0 Comments