Ticker

6/recent/ticker-posts

Hausa Fulani a Idon Na Kusa Da Na Nesa

Daga

Muhammad Abubakar Zabi
Department of Nigerian Languages and Linguistics
Sa’adu Zungur University, Bauchi
08136844199
muhammadabubakarzabi@gmail.com

Da

Abdulsalam Alhaji Jibrin,
School of Secondary Education (Languages).
Aminu Saleh, College of Education, Azare
abdulsalamalhajijibrin@gmail.com

Tsakure

Fulani da Hausawa al’umma ce daɗɗiya wadda ban Allah ba wanda ya san lokacin haɗuwarsu, sakamakon ƙarancin kayan rubutu a wancan lokacin. Fulani na cikin ƙabilu na farko-farko da Hausawa suka fara cuɗanya da su. Wannan shi ya kawo bazuwar Fulani ko’ina cikin ƙasar Hausa. Shi ya sanya wasu maƙwabtansu na nesa ke yi musu kallon abu guda. Haka kuma shi ya samar musu da sunan Hausa-Fulani sakamakon daddediyar mu’amala wace ta saka suka cakuɗa da juna, wanda yanzu an kai fagen da Bafulatani ko Bahaushe ba zai iya tantance cewa shi kaza ne, saboda an yi auratayya an kuma gauraya waje guda. Wanda zai yi wuya ka ƙirga kaka biyu ko uku na zuriyarku ba ka tarar da wani sirki na Bahaushe ko Bafulatani ba. Ko ta wajen Uwa ko ta wajen Uba. Wannan aikin zai waiwaci asalin Fulani a takaice da na Hausawa da zamatakewa da suturar Fulani da kuma suturar Hausawa. A taƙaice wannan takarda za ta duba yadda ake kallon Hausa Fulani a idon na kusa da na nesa.

1.0 Gabatarwa

Hausawa da Fulani, wasu al’umma ce da Allah kaɗai ya san irin ajiyar da ya yi. Ku san za a iya cewa haɗin Allah ne, wanda duk ya ce zai raba Hausawa da Fulani to! Tamkar zai iya raba hanta da jini ne. Dangantakar zamantakewar Hausawa da Fulani mahdi ne mai dogon zamani. Abu ne mawiyaci a iya gano lokacin da Hausawa da fulani suka fara hulɗa. A ruwayar Maigandi Attahiru (2003) masana irin su Malam Abdullahi Gwandu da Waziri Sakkwato da suka yi faɗi tashin gane hakan sun yi kirdadon gano cewa, Fulani na cikin ƙabilu na farko-farko da Hausawa suka fara cuɗanya da su. Wannan shi ya kawo bazuwar Fulani ko’ina cikin ƙasar Hausa. Shi ya sanya wasu makwabtansu na nesa ke yi musu kallon abu guda kawai, kamar Iyamurai da Yarbawa da sauransu ƙabilu na nesa. Haka kuma shi ya samar musu da sunan Hausa-Fulani sakamakon daɗɗeɗiyar mu’amala wace ta haɗa juna, wanda yanzu an kai fagen da Bafulatani ko Bahaushe ba zai iya tantace cewa shi kaza ne, saboda an yi auratayya an kuma gauraya waje guda. Wanda zai yi wuya ka ƙirga kaka biyu ko uku na zuriyarku baka tarar da wani sirki na Bahaushe ko Bafulatani ba. Ko ta wajen Uwa ko ta wajen Uba.

1.1 Waiwaye

Funtua (2010) ya gabatar da muƙala mai taken Tufafin Hausawa da Fulani na gargajiya. Bayan ya kawo gabatarwa sai ya kawo ire-iren tufafin Hausawa na gargajiya. Yanda ya yi bayanin tufafin maza da mata, da kuma tufafin da baƙi suka kawo. Alaƙar wannan muƙala da wannan takarda shi ne ya taɓo wani abu daga cikin abin da takardar take son duba wa wato tufafin Hausawa da Fulani, amma ta yadda suka bambanta shi ne ta yadda shi yana Magana a kan tufafi ne ita kuma tana Magana akan yadda na kusa da na nesa ke kallon Hausa fulani.

Shi kuma Ɗanmaigoro, (2010). Ya gabatar da takardarsa mai taken Magungunan Hausawa da Fulani. Bayan ya kawo gabatarwa sai ya duba Bokanci da Bori da Maita da Tsibbu da Magori da Ungozoma. Sannan sai ya duba Magungunan sana’o’i, yanda ya duba Wanzamai da Maƙera da Mahauta da Masunta da kuma Maɗora. Daga ƙarshe kuma ya kawo muhimmancin magungunan gargajiya ga Hausawa da Fulani. Wannan takarda alaƙarta da wannan shi ne yana Magana akan al’ummun Hausawa da Fulani, amma ta yadda a ka bambanta shi ne, yana magana akan magani ita kuma wannnan takarda tana magana akan kallon da makwabtan Hausa- Fulani ke yi musu.

Busa da Isa (2015) sun gabatar ta takardar su mai taken kalmomin Makwabtan ƙabilu a harshen Hausa. Yanda suka duba mene ne harshen Hausa da kuma Hausawa da makwabtansu, da are-aren kalmomi daga makwabtan Hausawa zuwa harshen Hausa. Sai kuma su ka yi bayani dangane da al’ummar Fulani da kuma kalmominsu da aka ara. Yarbanci da kalmominsu. Da Barebari da kalmominsu da aka ara, da al’ummar Azbinawa da kalmominsu da aka ara, da al’ummar Nufe da kalmominsu da aka ara, da kumaal’ummar Gwari da kalmomin da Hausawa suka ara. Ita kuma wannan alaƙar da ke akwai tsakani, yana magana akan harshen maƙwabtan Hausa, ita ma wannnan takarda tana magana akan maƙwabta ne, don haka zuwan wannan takarda zai taimaka wa aikin wajen kammaluwa.

1.2 Ra’i

Wannan takardar ta yi amfani da Tsarin Mu'amala (Contact Theory) a matsayin hanyar nazari don gano yadda hulɗa tsakanin mutane daga al'ummu daban-daban ke shafar yadda suke kallon Hausawa da Fulani. An zaɓi wannan ra’i ne saboda yana bayyana cewa, idan mutane suka yi mu'amala mai kyau, za su canza ra'ayoyinsu game da juna."

1.3 Asalin Hausawa A Taƙaice

Sanin asalin Bahaushe kundi ne mai faɗin gaske. Domin Bahaushe mutum ne mai daɗaɗɗen tarihi bisa doron ƙasa. Masana da dama sun ambaci haka akan wa za a kira Bahaushe. Masana ilimin kimiyyar harshe da tarihi da al’ada sun sha gwagwarmaya wajen gano wane ne Bahaushe. Haƙiƙa an daɗe ana ɗauki ba daɗi wajen bin diddigin gano Bahaushe na asali. Daga cikin irin waɗannan masana ilimin harsuna akwai, Schuh da Yalwa (1993) sun bayanna cewa:

Yaren Hausa harshen na ɗaya daga cikin Harshen Chadi (ɓangaren iyalan Afro-Asiatic). Sun bayyana cewa Hausawa na a yammacin Tafkin Chadi ne, amma sun warwatsu a wurare daban-daban. Daga cikin wannan akwai Arewacin Nijeriya da Nijar da Chadi. Haka kuma, Harshe ne da ya bunƙasa wajen kasuwanci a ƙasashen Afrika ta yamma, da Afrika ta tsakiya da kuma ɓangaren Arewa maso Yamma da Sudan.

Jinju, (1985) a nasa binciken ya ce: Mutanen Masar baƙar fata ne kuma sarakunansu (Fir’aunoni ne), baƙaƙe ne har lokacin sarautar gida na ashirin da huɗu. Su waɗannan mutanen Masar su ne a ganina suka yiwo ƙaura zuwa Afirka ta yamma suna zaune a bakin tafkin Chadi wanda can da maƙil yake da ruwa. A wannan lokaci ne mutanen farar fata suka riƙakai masu hari, sai suka yi ƙaura suka canza wurin zama tare da harshen su na misiranci wanda ya canza ga tarihi ya koma Hausa.

Duka waɗannan bayanai ba su isa su tabbatar muna da asalin Hausawa da harshensu ba. Domin harshe kaɗai ba iya tabbatar da asalin mutum. Zancen zaman Hausawa a gaɓar Kogin Chadi da alaƙar harsunan gidan Chadi wani wuri ne da Hausawa suka zauna na ɗan lokaci, daga baya suka canza wurin zama.

Haƙiƙa Smith ya ce, wani abu game da wane ne Bahaushe, kasancewar kowane Bahaushe yana iƙirari da harshensa na Hausa a matsayin asali. Hausawa da dama sukan yi kamannu da junansu. Ra’ayin Smith ya so ya yi kama da na Adamu (1978) da yake cewa:

Hausawa ne daɗaɗɗun mazauna Hausa da dukkanin zuriyarsu ta fuskar maza, ko kuma waɗanda suke amfani da al’adun Hausawa da riƙe harshensu da addininsu.

Shi kuwa Bunza (1990) ya bayyana cewa:

Hausawa dai mutane ne da suke zaune a ƙasar Hausa tun

Farkonta, kuma suna da zuriya a cikinta har ya zuwa yau

Kazalika, suna magana da harshen Hausa ba su da wani

Harshen in ba Hausa ba, suna da ɗabi’u da al’adu irin na

Hausawa. Idan sun saɓa haka to barbarar yanyawa ne.

Kamar yadda muka gani cewa masana sun kawo wane ne Bahaushe: Bisa ga yadda masana da manazarta suka ce za mu iya cewa, Bahaushe shi ne, mutumin da yake zaune a ƙasar Hausa, ta fuskar launi kuma baƙi ne; kuma iyayensa Hausawa ne, idan kuma ba a ƙasar Hausa yake zaune ba, ya kasance yana jin Hausa, kuma wasu al’adun Hausawa sun yi tasiri a gare shi, to wannan shi ne Bahaushe.

1.4 Asalin Fulani A Taƙaice

Masana da suka yi rubutu a kan asalin Fulani sun bayyana shi a zaman mai sarƙaƙiya kamar na Hausawa. Daga cikin waɗanda suka yi wannan ƙoƙarin sun haɗa da Malam Abdullahi Gwandu ƙanin Mujaddadi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo da Wazirin Gwandu.

Malam Abdullahi A cikin littafinsa, Tazyin al-waraƙat cewa, Fulani sun fito ne daga tsatson Uƙubatu ɗan Nafi’u wanda ya ce Balarabe ne kuma Sahabi Babba. Ya zo ƙasar Masar inda ya auri ýar Sarkin garin mai suna Bujja Mugga sai suka haifi ýaýa huɗu waɗanda su ne asalin Fulani da Fulatanci.

Shi kuma Wazirin Sakkwato Malam Junaidu a littafinsa Tarihin Fulani cewa ya yi Fulani sun ta so ne daga Durisininata ƙasar Sham har suka iso futa Toro ta ƙasar Sinigal suka zauna garin har suka yi yawa. Nan ne a cewarsa Uƙubatu ya sadu da su har suka shiga addinin musulunci. (Junaidu, 1978)

Ƙari ga wannan ra’ayin Waziri Junaidu ya rawaito cewa akwai masu ra’ayi Fulani asalinsu zuriyar Rama ne ɗan Annabi Ishaƙɗan Annabi Ibrahim (A.S) ya kuma bayyana ta la’akari da wannan ra’ayi cewa, sun ta so ne daga futa Toro da nufin komawa ƙasar Larabawa a ƙarƙashin jagorancin wani babban Malami Musa jakollo. Daga cikin zuriyyarsa ne aka haifi Shehu Usmanu Ɗanfodiyo. Sun zauna a ƙasar Gobir ana kiransu da suna Torankawa saboda fitowa daga Futo Toro. (Junaidu, 1978)

Haka kuma bincike ya nuna cewa zaman farko na Fulani yan yankin ƙasar Senegal ne na Afirka ta yamma. Daga nan ne sannu a hankali suka ba zu zuwa ƙasashen chadi da Kamaru. A cikin ƙarni na sha huɗu ne suka shigo ƙasar Hausa. Dalilin shigowar Fulani ƙasar Hausa kuwa shi ne, sanadiyar ƙaura da suke yi daga Senegal zuwa gabashi, domin neman makiyaya mai kyau. A cikin farkon ƙarni na sha shida akwai al’umomin Fulani masu yawan gaske a ƙasar Hausa . sannu a hankali kuma a cikin ƙarni na sha bakwai wasu Fulani da ke zaune ƙasar Hausa suka yi kudu maso gabas har suka iso kogin Gongola suka mamaye wurin saboda yanayinsa na dausayi da makiyaya mai kyau. Fulani ba su da wata sana’a wadda ta wuce kiwo. A yau al’ummar Fulani sun haɗe da ta Hausawa har ma ana ganinsu a matsayin al’umma ɗaya. (Funtua 2010)

Ta la’akari da yadda masana da manazarta suka ce dangane da asalin Fulani za mu iya cewa,asalin Fulani Larabawa ne wanda asalinsu a gabas ta tsakiya suke, kuma suna daga cikin zuriyar Annabi Ibrahim (A.S). Saboda yanayi da kuma ƙaura-ƙaura ce na neman abinci da wajen kiwo ya sa Fulani barin wajen su na asali suka zo yadda suke zaune a yanzu.

1.5 Zamantakewa

Zamantakewa na nufin kamar yadda sunan ya nuna daga Kalmar zama, wato abin nufi a nan shi ne zaman tare, ya’allah ko dai ta fuskar zumunta ko makwabta, ko kuma ta fuskar yanayin sana’a, ko da yake ma’anar takan iya wuce wannan idan aka yi la’akari da ire-iren dangantakar da ake samu tsakanin al’umma.

Hausawa sun daɗe suna hulɗa da ƙabilun da ke zagaye da su. Wannan kuwa ya faru ne a sanadiyar kasuwanci ko ƙaurace-ƙaurace. A cikin gida Nigeriya za a iya kasa zamantakewar Hausawa da sauran ƙabilu zuwa gida biyu. Gidan farko shi ne Hausawa da sauran ƙabilu da suke a rewancin Nigeriya. A arewa harshen Hausa ya zama harshen ƙasa wanda da sauran ƙabilu ne ke amfani da shi. Idan ƙabilu uku ko huɗu sun haɗu harshen da suke amfani da shi wanda kowannensu na ji shi ne harshen Hausa. Don haka ma a jamhuriya ta farko aka mai da harshen Hausa ya zama harshen da ake amfani da shi a majlisar dokoki ta kaduna. Hausawa sun bazu ya zuwa sauran garuruwan ƙabilun arewacin Najeriya irinsu Jos, da Adamawa, da Borno da Bauchi da Kaduna da kuma Niger da sauransu. Haka kuma al’adunsu da suka haɗa da abinci da tufafi da muhalli duka sun sami karɓuwa a jahohin Nigeriya, da wanda ba na Hausa ba.

ɓangaren zamantakewa kuma da makwabtan Hausawa a kudanci da gabashin Najeriya kuwa, Hausa na da kyakkyawar alaƙa ta kasuwanci da su. Da yake zamantakewar Hausawa da ƙabilun da ke kewaye da su ta bambanta da yadda take da jama’ar kudanci ko gabashi, wannan ne ya sa Hausa cakuɗuwa da waɗannan al’ummu, sai suka kakkafa unguwanni nasu yasu-yasu. A kudanci Nijeriya. Hausawa kan kira waɗannan unguwanni da suna “Sabo” Don haka, ne suke da sabo-Ibadan, Sabo- ile-ife. A kudancin Najeriya kuwa akwai unguwannin Hausawa irinsu Agana Bodi da sauransu. A sakamakon zamantakewar Hausawa da Fulani, aka samu alaƙa ta kusa sosai wanda har ta kai yanzu ba a iya bambance Bahaushe da Bafulatani. Auratayya tsakanin Hausawa da Fulani, Fulani suka wanke Bahaushe ya zama kyakkyawa mai kyan siffa, koma bayan a da Bahaushe baki gajere mai

ƙaton kai.

1.6 Hausa-Fulani Gani Daga Nesa

Bisa dukkan alamu makwabtan Hausa-Fulani da suke nesa suna yi wa Hausa-Fulani kusan abu ɗaya, amma abin ba haka yake ba, saboda duk wani Bahaushe da ya taho daga Arewa ko Bafulatani, wanda ya yi karatu da wanda bai yi karatu ko ɗan kasuwa gani suke duk abu guda ne. Domin su ba sa la’akari da wasu ɗabi’u ko halaye ko kuma al’adu da ke bambanta su. In dai ba shanu suka ga mutum yana kiwo ba, ko Bafulatana tana tallan nono ba; to kawai Hausa-Fulani ne. Su a kallonsu wanda yake kiwo shi ne Bafulatani, amma duk wanda ya zo da saɓanin haka kawai za su kira shi da Hausa-fulni ne.

1.7 Hausawa A Idon Maƙwabtansu

Masu kallon Hausawa da Fulani na kusa da alama kallonsu ya sha bamban da kallon da maƙwabtansu na nesa su ke yi musu. Su makwabta na kusa suna iya bambance Bahaushe da Bafulatani ta waɗannan fuskoki:

- Sunaye

- Sutura

- Muhalli

- Al’adunsu na bukukuwa da

- Addini

1.7.1 Sunaye – Ta hanyar Suna maƙwabta na kusa na iya bambanci Hausawa da Fulani. Ma’anar suna a fannu yana nufin wata keɓɓeɓiyar kalma da wata al’umma ta yarda da ita domin ƙira ko ambaton wani mutum ko wata dabba ko tsiro ko wani abu mai rai ko maras rai (mace ko namiji) ta yadda za su bambanta da junansu ko makamantansu.

Masana da manazarta sun tofa albarkacin bakin su game da ma’anar suna kamar haka:

CNHN (2006) sun bayyana suna da cewa kalma ce da ake amfani da ita wajen ƙira ko ambaton wani abu.

Bargery (1963: 956) ya ce suna kalma ce da ake ƙiran mutum ko bukin da ake yi a rana ta bakwai ta haifuwar yaro ko yarinya a cikin al’ummar Hausawa.

Daga waɗannan bayanai, muna iya cewa suna wani abu ne da mutune suke saka wa wani abu mai rai ko maras rai domin ƙiransa da shi, a tantancewa da bambantawa.

Misalin Sunayen sun haɗa da:

Hausa Fulantanci

Gambo Haro

Juji Lari

jinjiri Yiɗi

Zinaru Innayo

Kyauta Toka

Kanta Kaku

Ayashe Junguɗo

Talle Bello

Magaji Shanono

Korau Juli

Tunau Ori

Haka kuma, ta waɗannan sunaye maƙwabtan Hausawa da Fulani na kusa na iya tantace waye Bahaushe ko Bafulatani daga zarar an ambaci sunansu.

Haka kuma, ta fuskar suturar Hausawa da Fulani maƙwabtansu na iya bambance su. Ita dai asalin kalmar sutura dai ararriyar kalma ce daga larabci(suturatu) da manufar tufafi da ke rufe wa mutum al’aurarsa, wato dai duk tufafin da ke isar mutum Musulmi ga yin sallah. Amma a wajen Bahaushe Kalmar tana da ma’anar tufafi isassu da za su kare mutuncika daga tsiraici da kowanne iri ne, sababbi ne, ko tsofaffi in dai sun kare tsiraici, ana kiransu sutura. Misalin tufafin sun haɗa da:

1.7.2 Tufafin Hausawa

Gyauto Wando Fatari

Zani Rawani Mayafi

Riga Taggo Fatala

 

Tufafin Fulani

Fulani kamar yadda aka sani Makiyaya ne. Don haka akasarin tufafinsu ƙanana ne ba kamar na Hausawa ba. Haka kuma Fulani suna rikon al’ada matuƙa. Dalili kenan ake ganin ba su cika aron al’adun wasu baƙi ba ta fuskar tufafi. Ɗan dama- dama a wannan lokaci yaransu sun ɗan ari suturar Turawa, wato ƙanana riga da jeans. Sakamakon yadda tela yake ba su wahala. Daga cikin tufafin Fulani akwai na maza da na mata kamar haka:

Tufafin Fulani maza manya da yara, Fulani suna sa rigar saki ce mai kama da yar shara wadda aka yi wa ado da ulu a wuya da gaba. Tana da aljihu biyu a gefenta. Sukan kuma haɗa ta da wando wanda ake kira “ka-haye-ruwa” . Sannan su sa hula haɓar kada wadda ita ma aka yi wa ado da zaren ulu. Haka kuma suna ya fa gwado a saman rigar sannan su rike sanda, da madubi, wani sa’in da malafa da jallo. Mata kuma suna sa rigar saki ce wadda aka yi wa ado sosai a gabanta da zaren ulu ja da kuma fasasshen madubi. Tsawon rigarsu bai wuce cibiya. Suna ɗaura adiko a ka, su kuma ɗaura zane da ake kira mudukare. Fulani mata ba su da tufafi da yawa kamar na Hausawa.

Amma a wannan zamani, su Fulani ba su aro kayan wasu daban ba, sai dai kayan Hausawa. Sakamakon zamantakewar da ke tsakaninsu. Bisa ga yadda maƙwabtan Hausawa da Fulani suke tare da su, da zarar sun ga tufafin za su iya bambance su, cewa wannan Bahaushe ne ko Bafulatani

1.7.3 Muhalli

Muhalli yana nufin wajen da al’umma ke zaune, suke gudanar da hidimomin rayuwarsu na yau da kullum a wajen. Yanayin muhallin Hausawa da Fulani ya ɗan bambanta da juna, Bahaushe muhallin da yake zaune za ka tarar da shi yana haɗe da ‘yanuwansa da abokanai da sauran al’umma. Bafulatani kuma, yanayin wajen zamansa ya sha bamban da na Hausawa domin shi kowa gonarsa yake zuwa ya yi gida da shi da iyalansa. Aliyu (2015) Ta wannan tsarin ne maƙwabtan Hausawa da Fulani na iya bambance su.

1.7.4 Al’adun Bukukuwa

Al’ ummar Hausawa da Fulami kamar kowace al’umma ta duniya tana da tata al’ada da ta gada kaka da kakanni. Waɗanda suka bi don tafiyar da rayuwarsu ta yau da kullum. Al’ada ta shafi dukkan matakan rayuwar Bahaushe da kuma Fulani tun daga aure da haihuwa har mutuwa.

A cikin al’adun Hausawa da Fulani, biki yana daga cikin abin da ke da muhimmanci a cikin hidimomin da suke gudanar wa a rayuwarsu ta yau da kullum.

Bukukuwa:

A tsari na Bukukuwan Hausawa da Fulani za a samun al’adu daban daban da suka keɓanta ga waɗanda bukin ya shafa misali, a lokacin da za a fara gudanar da bukukuwan aure ko haihuwa ga al’ada za a sami sunaye da suka shafi waɗanda bukin ya shafa misali.

a. Amarya a. Ɓagaɗo

b. Ango b. Angojo

c. Yaro na c. Ɓingeljo

d. ‘Yar amarya

e. Mai jego

f. Suruka ko Sarakuwa

g. yarbiƙi/ Ungozoma

Haka kuma, maƙwabtan Hausawa da Fulani na iya tantance su ta wannan tsari, siffa da halaye da kuma wasu al’adunsu. Misali, ta hanyar siffa duk inda ka ga Bafulatani fari ne akasari, haka kuma gashinsu a murɗe yake. kuma ma fi yawansu sirara ne, dogaye. Haka kuma ba su da sakin jiki, suna da kunya. Bahaushen ƙwarai za a sami shi baƙi ne sosai, kuma zubin kansa na da tsawo da kurungun kai mai ɗan jemo. Bunza (2015) Ta fuskar Gaisuwa, Tafiya da Mu’amula da Auratayya da Mutuwa da Shugabanci da Sana’a da kuma Tsarin gine-gine, duk waɗannan ɗabi’u makwabta Hausa-fulani na iya bambance su ta waɗannan hanyoyi (Adamu 2015). Kuma zai yi wuya ka ga Bafulatani ya ci maka abinci a kan hanya, amma Bahaushe ya sha bamban da wannan ɗabi’a ta Fulani.

Haka kuma Bafulatanin jeji za ka same shi da malafa da sanda da kuma jallon ruwa. Idan kuma saurayi ne za ka same shi da madubi da sanda da kuma wuƙa. Wanda wannan halayya ta sha bamban da ta Bahaushen ko da kuwa na jeji ne ba za ka same shi da waɗannan abubuwa ba. Ta fuskar abincinsu kuwa, makwabtan suna iya bambance su. Ta fuskar abinci su, Bahaushe yana da tuwo da Ɗan wake da Tubani da Dambu da Waina da Ɗanbagalage da Ƙuli-ƙuli da kwaɗo da kuma Daƙuwa da sauransu. Bafulatani kuma za ka same shi da Fura da nono da Kunun kanwa da Kunun tsamiya da Kwaɗon rama da Tantaɗi da Shaɓe da Kasambara, da sauransu.

Ta ɓangaren furuci kuwa maƙwabtan Hausawa na kusa na iya bambance su. Misali Bafulatani ya kan ce “Zan shi maimakon Zan ci”. Haka kuma Bahaushe ba iya faɗin ƙosan sai dai ya ce Kwasan. Duk waɗannan makwabtan Hausawa na kusa suna iya bambance Hausawa da Fulani ta waɗannan hanyoyi da aka lissafa a sama. Koma bayan na nesa. Sabi da ba sa tare da su. Balle su ga wasu ɗabi’unsu ko halaye domin su iya bambance waye Bahaushe ko Bafulatani.

A takaice kallon da na nesa ke yi wa Hausawa da Fulani a matsayin abu guda. Ya sa mu ne a sakamakon ba tare da su suke ba a waje guda. Kuma sun tashi sun ga Hausawa da Fulani waje guda, Da rashin sanin waye Bahaushe da Bafulatani, sannan kuma sun lura da kowanensu Hausa yake yi. Haka kuma su a tunaninsu duk wani ɗan Arewa Hausa Fulani ne. Haka kuma sun kula da cewa yanayin zamantakewarsu da auratayya tsakaninsu duk guda ne. Kuma suna kishin junansu a waje. Don haka ne ma suke cewa Hausa-Fulani. Amma na kusa na yi musu kallo ne, irin na mutum da makwabcinsa. Domin tare suka tashi, Kuma za a iya cewa tare aka haife su har suka yi wayo tare. Don haka ne, su kallon da suke yi ya sha bamban da wanda na nesa ke yi musu.

1.9 Kammalawa

Kamar yadda aka gani cewa, mun ga waye Bahaushe da kuma Bafulatani. Sannan muka ga irin zamantakewar da ke a akwai tsakanin Hausa-fulani da makwabtansu. Bayan haka kuma mun ga irin kallon da na kusa suke yi wa Hausawa da Fulani. Sannan mun ga yadda na nesa ke yi musu kallo. Sannan sai muka duba ainihin suturarsu. Kamar yadda aka sani cewa tun fil azal Hausawa da Fulani suna da tufafinsu na gargajiya, masu ƙima da ban sha’awa a idanun sauran ƙabilun da suke kewaye da su.

Shawarwari:

* Ya kamata a ƙara yin mu'amala tsakanin al'ummu daban-daban da kuma Hausa Fulani, domin haɓaka fahimtar juna.

* Ya kamata a gudanar da ayyuka da za su haɗa al'ummu daban-daban, domin kawar da rashin fahimta da kuma nuna halayen ƙauna da juna.

* Ya kamata a riƙa yin tattaunawa game da al'adu da ɗabi'u daban-daban, domin sauƙaƙe fahimtar juna.

* Ana bada shawara ga al'ummu daban-daban da su ƙara hulɗa mai kyau da Hausawa da Fulani domin inganta fahimtar juna da kuma kawar da ra'ayoyin da ba su dace ba.

Manazarta

Adamu, M. (1978), Hausa Factor In West African History. Ahmadu Bello University Press, Zaria.

Aliyu, M. (2015) “Yanayi muhallin Hausawa da Fulani A Ƙasar Katagum” Kundin N.C.E: Azare, Aminu sale, Collage of education.

Bargery, G. P. (1933)Hausa-English Dictionary and English- Hausa

Bunza, A.M. (1990), Hayaƙi Fid Da Na Kogo: Nazarin Siddabaru Da Sihirin Hausawa. Kundin Binciken Don Digiri Na Biyu. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

Bunza Aliyu Muhammad, (2015) “A ji Bahaushe, a ga Bahaushe, a san Bahaushe ya yi Bahaushe. (Tsakuren ficen Bahaushe da Tasirinsa a Duniyar Ƙarninsa)” Takardar da aka gabatar a Sashen Nazarin Harsunan Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Bunza Aliyu Muhammad, (2015) “Matakan Kyallaro Asalin Bahaushe:( Ruwa na ƙasa sai ga Wanda Bai Tona Ba)” Takardar jagora da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa-da-ƙasa na farko a Jami’r Jihar Kaduna, ƙarƙashin inuwar Hausa Studies Scholars Association, kulawar Department of Nigerian Languages and Linguistcs bisa taken ‘The Hausa People, Language and History: Past Present and Future’ Ranar 15-17 Disamba 2014 a Arewa House, Kaduna.

Funtua, A. I; Gusau Sa’idu Muhammad (2010) Al’adu da ɗabi’u Hausawa da Fulani. Eds

Junaidu, (1978) Tarihin Fulani. Zariya: NNPC Publisher

Jinju, H. (1985), “Asalin Hausawa Da Harshensa” Maƙala Da Aka Gabatar A Taron Ƙasashen Duniya Akan Hausa Da Adabi Da Al’ada. Jami’ar Bayero, Kano.

CNHN (2006). Kamusun Hausa na Jami’ar Bayero Kano. Ahmadu Bello University Press.

Maigandi Attahiru, (2013) “Fulani da Hausawan gundumar Sakkwato: Birɓishin dangantaka ta share jini a koma wasa” Ɗunɗaye Vol. 1: Number 6: Journal of Hausa Studies. Department of Nigerian Languages, Usmanu Ɗanfodiyo University, Sokoto.

Nashayya, B. M da Bisalla, B.A (2015) Who Are The Hausa/Fulani? 1st International Conference Organized by The Department Of Nigeria Languages And Linguistics, Kaduna State University, Kaduna State.

Schuh, R.G. and Yalwa, L.D. (1993), Hausa (illustration of the IPA) Journal of the international Phonetic Assocition. 23 (2): 77-82.

Hausa Fulani

Post a Comment

0 Comments