Daga
Muhammad Abubakar Zabi
Sashen Nazarin Harsunan
Nijeriya
Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato
08136844199
Muhammadabubakarzabi@Gmail.Com
Da
Adamu Halilu
Sashen Nazarin Harsunan
Afirka
Jami’ar Amadu Bello,
Zaria
08032307714
Tsakure
Hausawa al’umma ce da ta
ginu bisa matakan rayuwa har guda uku. Da farko Hausawa sun gudanar da
rayuwarsu bisa tsarin al’adun gargajiya wanda ya fara tun daga haifuwa da aure
da kuma mutuwa. Hatta bautarsu a gargajiya suka gudanar da ita a wannan matakin.
Haka kuma sun gudanar da rayuwa bayan karɓar addinin musulunci duk da haka ba su watsar da
al’adunsu na gargajiya ba. Bayan zuwan turawan mulkin mallaka rayuwarsu ta
gudana bisa sabon tsari. Duk da waɗannan sauye-sauyen matakan rayuwa bai sa su Hausawa
sun watsar da al’adunsu ba. Bori da Malantaka suna daga cikin hanyoyi da
Hausawa suka ɗauka a matsayin hanyar
warakar da al’ummarta. Aikin daga ƙarshe zai duba waye
Bahaushe, sannan ya duba ma’anar Bori, da Malanta da kuma ma’anar magani tare
da duba mene ne adabi. A duba ma’anar Bori da Malanta a taskar adabi, kamar waƙa baka, da Karin magana
da sauransu.
1.0 Gabatarwa
Hausawa al’umma ce da ta
ginu bisa matakan rayuwa har guda uku. Da farko Hausawa sun gudanar da
rayuwarsu bisa tsarin al’adun gargajiya wanda ya fara tun daga haifuwa da aure
da kuma mutuwa. Hatta bautarsu a gargajiya suka gudanar da ita a wannan matakin.
Haka kuma sun gudanar da rayuwa bayan karɓar addinin musulunci duk da haka ba su watsar da
al’adunsu na gargajiya ba. Bayan zuwan turawan mulkin mallaka rayuwarsu ta
gudana bisa sabon tsari. Duk da waɗannan sauye-sauyen matakan rayuwa bai sa su Hausawa
sun watsar da al’adunsu ba. Akwai hanyoyi da dama da za a iya duba ire-iren
al’adun Hausawa, ɗaya daga cikin hanyoyin
ita ce hanyar nazarin Bori na gargajiya wanda suke amfani da shi tun matakin
rayuwar farko har ya zuwa wannan zamani da kuma irin tasirin zamanin da aka
samu a cikin harƙar Bori a yau, wanda yanzu Malantaka ta maye gurbin
bori.
Daga cikin al’adun
gargajiya na Bahaushe, babu wani ɓangare da ya samu karɓuwa, da farin jinni ga manazarta ýan ƙasa da na waje kamar
Bori. Rubuce-rubucen da aka yi kan Bori sun fi kowane rubuce- rubuce yawa a
fannonin nazarin al’ada. Bunza (2015).
Bori wani nau’i ne daga
cikin sassan addinin Bahaushe, wato Tsafi, camfi da kuma Bori. Don haka wannan
nau’i na Bori ya samu karɓuwa a wajen Hausawa
sosai, suna amfani da Bori da Malanta a matsayin wata hanya ta samun magani.
Bori dai a nahawun
ma’ana, Kalmar ta ci sunanta. A farfajiyar adabi ba ta tsallake ma’anar wasa
ba. A ɓangaren al’ada kuma wata
hanya ce wadda al’ummar Hausawa suka yi Imani da ita Bunza (2015).
Aikin daga ƙarshe zai duba waye
Bahaushe, sannan ya duba ma’nar Bori, da Malanta da kuma ma’anar magani tare da
duba mene ne adabi. A duba ma’anar Bori da Malanta a taskar adabi, kamar waƙar baka, Karin magana da
sauransu. Sannan sai a kammala aikin.
2.0 Asalin Hausawa
A Taƙaice
Sanin asalin Bahaushe
kundi ne mai faɗin gaske. Domin Bahaushe
mutum ne mai daɗaɗɗen tarihi bisa
doron ƙasa. Masana da dama sun ambaci haka akan wa za a kira
Bahaushe. Masana ilimin kimiyyar harshe da tarihi da al’ada sun sha gwagwarmaya
wajen gano wane ne Bahaushe. Haƙiƙa an daɗe ana ɗauki ba daɗi wajen bin diddigin gano Bahaushe na asali. Daga
cikin irin waɗannan masana ilimin
harsuna akwai, Schuh da Yalwa (1993) sun bayanna cewa:
Yaren Hausa harshen
na ɗaya daga cikin Harshen
Chadi (ɓangaren iyalan
Afro-Asiatic). Sun bayyana cewa Hausawa na a yammacin Tafkin Chadi ne, amma sun
warwatsu a wurare daban-daban. Daga cikin wannan akwai Arewacin Nijeriya da
Nijar da Chadi. Haka kuma, Harshe ne da ya bunƙasa wajen kasuwanci
a ƙasashen Afrika ta yamma, da Afrika ta tsakiya da
kuma ɓangaren Arewa maso Yamma
da Sudan.
Jinju, (1985) a nasa
binciken ya ce:
Mutanen Masar baƙar fata ne kuma
sarakunansu (Fir’aunoni ne), baƙaƙe ne har lokacin sarautar gida na ashirinda huɗu. Su waɗannan mutanen Masar su
ne a ganina suka yiwo ƙaura zuwa Afirka ta yamma suna zaune a bakin tafkin
Chadi wanda can da maƙil yake da ruwa. A wannan lokaci ne mutanen fara fata
suka riƙakai masu hari, sai suka yi ƙaura suka canza wurin
zama tare da harshen su na misiranci wanda ya canza ga tarihi ya koma Hausa.
Duka waɗannan bayanai ba su isa
su tabbatar muna da asalin Hausawa da harshensu ba. Domin harshe kaɗai ba iya tabbatar da
asalin mutum. Zancen zaman Hausawa a gaɓar Kogin Chadi da alaƙar harsunan gidan Chadi
wani wuri ne da Hausawa suka zauna na ɗan lokaci, daga baya suka canza wurin zama.
Haƙiƙa Smith ya ce, wani abu
game da wane ne Bahaushe, kasancewar kowane Bahaushe yana iƙirari da harshensa na
Hausa a matsayin asali. Hausawa da dama sukan yi kamannu da junansu. Ra’ayin
Smith ya so ya yi kama da na Adamu (1978) da yake cewa:
Hausawa ne daɗaɗɗun mazauna Hausa da
dukkanin zuriyarsu ta fuskar maza, ko kuma waɗanda suke amfani da al’adun Hausawa da riƙe harshensu da
addininsu.
Shi kuwa Bunza (1990) ya
bayyana cewa:
Hausawa dai mutane ne da
suke zaune a ƙasar Hausa tun
farkonta, kuma
suna da zuriya a cikinta har ya zuwa yau
Kazalika, suna magana da
harshen Hausa ba su da wani
Harshen in ba Hausa ba,
suna da ɗabi’u da al’adu irin na
Hausawa. Idan sun saɓa haka to barbarar
yanyawa ne.
Kamar yadda muka gani
cewa masana sun kawo wane ne Bahaushe: Bisa ga yadda masana da manazarta suka
ce za mu iya cewa, Bahaushe shi ne, mutumin da yake zaune a ƙasar Hausa, ta fuskar
launi kuma baƙi ne; kuma iyayensa Hausawa ne, idan kuma ba a ƙasar Hausa yake zaune
ba, ya kasance yana jin Hausa, kuma wasu al’adun Hausawa sun yi tasiri a gare
shi, to wannan shi ne Bahaushe.
2.1 Ma’anar Bori
Yana da kyau kafi a fara
kallon ma’anar Bori, mu kalli Kalmar Bori. Kalmar Bori takan ɗauki ma’anoni
daban-daban idan aka sarrafa ta yadda al’umma ke kallon ta. Bahaushe ya samu
Kalmar Bori daga Kalmar “Bore”, Bore na nufin zanga zanga ta fito-na-fito, da
nuna rashin yarda, da burin ta’adanci, domin ramuwar gayya, ko tawaye, ga wanda
ba a so, ko zanga-zangar tabbatar da wanda ake so. Wasu suna ganin daga nan ne
aka samo Kalmar bori.
A wata fassarar kuwa,
ana hasashen Kalmar bori daga Borin tukunya, ko tuwo, ko fura, ke yi idan
an ɗora ta a kan wuta ana
girki. Yayin da ruwa suka tafasa zafi ya ci ƙarfinsu suka fara zaɓarɓaka, za a ga
dahuwar/girkin ta shiga wasu halaye kamar haka.
-
Za
ta ture marfin da aka rufe.
-
Ruwan
za su fito waje da ƙarfi.
-
Za
ta riƙa fitar da kumfa.
-
Wutar
za ta mutu ta kowane gefe..
Idan girki ya shiga
wannan halin, za a kira mai shi a ce zo da sauri tukunyarki ta fara Bori. Komai
tafasar da ta yi idan ba a samu abu biyu ba, ba a cewa ta yi Bori.
-
Faɗuwar marfi ƙasa
-
Fitar
kumfa a bakin tukunya
Haka yake ko a
wajen ɗan Bori, matuƙar bai kai ƙasa baki na fitar da
kumfa ba, ba a cewa an hau bori. Wata ƙila daga nan ne kalmar
ta samo asalinta.
A wani ɓangaren kuma ana ganin
cewa Kalmar Bori ta samu asali daga, Bauri na magani. Bauri sauyoyi ne da
ganyen itace da ɓawo ake haɗawa cikin tukunya a
tafasa domin a sha a matsayin magani. Wasu na ganin cewa Kalmar ta samo asali
ne daga nan.
Bugu da ƙari, Hausawa na danganta
Kalmar da abubuwa da yawa, kamar idan aka ɓata wa yaro rai, ya faɗi ƙasa yana kuka, yana
shure- shure, a kan ce, a ƙyale shi Bori yake yi. Idan gyaɗa aka soya, wata ta
lalace tun gabanin a soya idan aka ɓare aka ga abin ya bayyana, ana ce masa, “Borin gyaɗa”. kaɗan ke nan daga cikin
hasashen da ake yi wa asalin Kalmar Bori. Daga nan kuma za mu duba mu ga mene
ne Bori.
2.1.1 Bori
Wani nau’i ne da ya sa
mu karɓuwa a cikin al’ummar
Hausawa sosai. Haka kuma shi wannan fage ya samu karɓuwa a ɓangaren masana da manazarta na cikin gida da waje. Ga
kaɗan daga cikin wasu
ma’anonin Bori:
“Bori shi ne, shigar
Iskoki a ɗayan gaɓoɓin
hanci ko baki ko kunne
tare da haƙiƙance
bayyanar su a idon mai
bori. Yawo da ake yi
da kai da rawar da ake
yi da fizge-fizge hanaye
da gaɓoɓi na fitar hankali su ne
bori”(Bunza 2015).
Haka kuma ya ƙara da cewa:
“Bori dai wata wasa ce
ta gargajiyar Bahaushe
da ta keɓanta ga wasu ýan
tsirarru da ke da
sha’awar
kwaikwayar ɗabi’un Iskoki da hulɗa
da su . shigan Iskoki na
haƙiƙa, ya wuce bori,
ya zama wata lalura ta
daban. Don haka bori ba
haƙiƙa ba ne kwaikwayon
shigan iska na haƙiƙa ne”(Bunza 2015).
Ya sake bayyana ma’anar
da cewa:
“Bori wata babbar mafaka
ce da mata suka
kafa domin ƙwato ýancinsu na
zamantakewa
da mutuntaka ga hannun
maza tare da ba da tasu
gudumuwa ga al’umma.
Matan da ke bori ba su kai
shi matsayin addini ba
domin ba su yi iƙiirarin barin
addinin da bori ya riske
su da shi ba”(Bunza 2015).
Wata ma’ana ta Bori
kuma:
“Bori wata dabarar
warkarwa ce da Bokaye suka
yi fice da ita.
Bisa waɗannan ma’anoni da muka
gani game da Bori, za a ƙara ganin cewa lallai bori wani fage na musamman wanda
ake yinsa bisa wasu dalilai da daman-daban. Mun fahimci bori ana yin sa saboda
neman Iskoki, da kuma wasa na nishaɗi, tare da mata ma suna yinsa domin isar da wani saƙon da yake damunsu. Haka
kuma yake ana bori domin neman waraka, wato neman magani ga wata cuta da ta
damu al’umma.
Don haka za mu iya cewa,
Bori wani wasa ne da al’ummar Hausawa ke yi, ta hanyar amfani da garaya da
gurmi da goge, tare da ka-ca-kau-ra, da rawa ta fitar hankali, domin nishaɗantarwa, da kuma nema
magani ga wata cuta da ta addabi mutum. Tare da yadda mata ke yin amfani da
Bori domin isar da saƙonsu ga wanda ya matsa musu, ko ya dame su ga wani
lamari na daban. Da kuma neman Iskoki don samun abokan hulɗa.
2.2 Malanta
Wannan fage na Malanta
ya samu kulawar malamai da suka yi rubuce-rubuce a kai. Ga kaɗan daga cikin abin da
wasu suka ce game da Malanta.
Asalin Kalmar Malanta
daga Larabci take ba Bahaushiya ba ce (Bunza 1999) gabanin bayyanar Musulunci
a ƙasar Hausa wannan kalma babu ita, bayan da Musulunci
ya samu karɓuwa, karatu ya samu
gindin zama a ƙasar Hausa, Malantaka ta bayyana (Musa 1999).
Bunza (2004) cewa ya yi
Malanta ita ce samun karatu sahihi mai tushe da aka naƙalto shi ga wani ko wasu
masana bisa tsarin koyo da ɗalibtaka. Haka kuma, ya kasance an samu aminta ko
yarda daga Malaminsa in da aka koyo shi ta cewa ɗalibin ya fahimci abin da aka koya yana da damar ya
koya wa wani..
Imam (1933) shi kuma
cewa ya yi daga cikin sifofinsa akwai tsarin suturarsa ta fuskar naɗi da kawaicinsa da kaɗaitarsa da kamun kansa
da makamantansu. Duk da haka, kowane mutum na iya ya ari waɗannan sifofi da Gangan
ko ɗabi’a har a yi masa
zaton Malanta ko dai bai san komai ba.
BirniTudu (2013) Y aba
da ma’anar malami kuma na nufi mutumin da ya koyi abu kuma ya koyar da shi.
Malami yana ba da bayani ga wanda ya nemi a warware masa wani al’amari na ibada
ko zaman duniya. A fagen addini shi ne mai kiran mutane zuwa ga addinin Allah
ta hanyar yi musu wa’azi. A fagen sana’a shi ne madugu uban tafiya. A
zamnatakewa, shi ne wanda ya fi shekaru. A hulɗa shi ne masani abin da na tare da shi ba su sani ba.
Dangane da yadda masana
suka ce game da Malanta ita ce, Ɗalibi da ya je wajen
wani malami domin koyon ilimi na addini ko na zamani, ko wani fannin wani abu
na daban, kuma ya sami ilimin shi ma ya koyar.
2.3 Magani
Wannan fage na magani ya
samu kulawar masana da mazarta ainun, wanda suka yi ta bayani game da ma’anar
magani. Ga kaɗan daga ciki.
“Maganin gargajiya- shi
ne yin amfani da itatuwa
ko rubutu ko addu’a ko
sulkulle, don warkar da
wata cuta, ko neman wani
amfani, ko gusar da
sharri, ko haddasa wani
abu saboda biyan buƙata”.(Adamu 2012)
“Magani shi ne duk wani
abu da za a yi, ko wata
hanya, ko kuma wata
dabara da ake yi don gusar
da wata cuta daga jikin
mutum ɗungurungum,
ko kuma kwantar da ita
don kawo jin daɗi ga jiki
ko ga zuciya dan sauwaƙa duk wahala da damuwa
da ita cutar kan iya
haifar Ahmad”, (1984:6).
“Magani- wata hanya ce
ta warkar da ko
kwantar da ko rage wata
cuta ta ciki ko ta
waje ko wadda aka samu
ta haɗari ko kuma
neman kariya ga cuta ko
abokan hamayya ko
neman ɗaukaka ta daraja ko ta
buwaya ta hanyar
siddabaru da sihirce-
sihirce na ban al’ajabi” (Bunza, 1990).
Kamar yadda masana da
mazarta suka yi ta faɗi-ta-shi wajen kawo
ma’anar magani, za mu iya cewa magani shi ne, duk wata hanya da mutum ya bi
wajen yaye wata damuwarsa, da ta dami shi. Walau ta jinya ko ta buƙatun rayuwa.
3.0 Ma’anar Bori Da
Malantaka A Taskar Adabi
Adabin babbar fitila ce
ta hasko rayuwar al’umma da yadda take tafiyar da ita.
Haka kuma Ɗangambo ya ƙara da cewa Adabi shi ne
madubi ko hoton rayuwar al’umma. Wannan ya ƙunshi yadda
al’adunsu, ɗabi’unsu, harshensu,
halayyar rayuwarsu da abincinsu, tufafinsu, maƙwancinsu, hulɗoɗinsu, tunaninsu da
ra’ayoyinsu da sauran abubuwa da suka shafi dabarun zaman duniya don ci gaba da
rayuwa; kai har ma da abubuwa da suka shafi mutuwa. Duk wata al’ada da ake
nazari kan al’umma yana da kyau a lalube adabi a ji yadda ya Harare batun. A
nan muna son mu duba Bori da Malantaka ta ɓangaren waraka mu ga me adabi ya ce game da shi, kamar
waƙa, kirari, da Karin magana da sauran ɓangarori na adabi.
3.1 Bori Da Malantaka A
Riwayar Mawaƙan Baka
Mawaƙan baka, adabi Bahaushe
suke ƙara faɗaɗa wa ma’ana, da ƙara fito da shi yadda
yake a cikin rayuwar al’umma. Domin nuna halin da ake cikin ko yadda al’umma
suke. Ana samu Mawaƙa da dama sun yi waƙa a kan Bori, akwai
Mamman Shata, Sa’adu Bori da wasu Mawaƙa da dama. Haka za mu ga
yadda mawaƙan baka suke tabbatar mana da cewa lallai Bori nau’i
ne na Magani, wanda mutum yake nema domin biyan wata buƙata ta daban. Wato jinya
ko wata buƙata ta rayuwa. Ga wani misali a lokacin da ƙwaro daga cikin ƙwarin Gambo mai waƙar ɓarayi ke neman sa’a a
kashe masa Tsoho Tudu cewa ya yi:
Jagora: An yi bori,
an yi bori, an yi bori
:Na yanka awakina da
kaji
:An ce sa’a ta samu
babba
:Y ac ce “Dogon zango
nab biyo Tudu”
:Wai shi ya biyo Tsoho
dag Gyalange.
Wannan ya nuna cewa
lallai Bori yana da tasiri cikin adabin Hausawa yadda har mawaƙa suke kawo shi a
matsayinsa na magani a cikin al’ummar. Idan aka duba abin da ka faɗi a nan, za a fahimci
cewa lallai bori wani nau’i ne daga cikin nau’ikan magani, domin ya nuna cewa
ya nemo sa’a a wajen ýan bori. Ya ce ya yanka awaki da kaji domin neman dacewa.
Haka kuma domin sake
tabbatar da lamarin bori da malantaka cikin adabin Hausa, ga wani ɗiyan waƙa da Narambaɗa yake yi wa wani ɗan sarauta da ya yi
takara. Yana cewa:
Jagora: Ga wani ya
kunna ya ga ba ƙafa
: ýan bori kai shi sun
baro
:Saruru ya baddala
abinai
Yara: Ya koma biɗan kwabon hura
Gindi: Ibrahim na
Guraguri
:Maishinkahi bajinin
zagi
:Mu dai Allah ya bar
muna kaya
Ta kula da wannan waƙar za mu sake tabbatar
da cewa bori magani ne, domin ana zuwa nema magani domin wata buƙatar rayuwa. Domin ya
kawo cewa shi ɗan takarar ya je neman
sa’a wajen ýan bori, suka damfare shi ya zama babu kwabo sai an taimaka masa.
Ke nan Narambaɗa ya nuna cewa ana amsar
magani a wajen ýan bori ko malamai, saboda haka ke nan za mu yarda cewa bori
wani nau’i magani ne.
Haka kuma Mamman Shata
Katsina ya nuna a cikin bakandamiyarsa cewa lallai bori da malantaka magani ne,
ga misali kamar haka:
Gindi; Alolo mai
ganga ya gode, yaran mai ganga sun gode.
: Ba malamai ba ne
:Ba bokaye ba ne
Ikon Allah ne,
Im bori ne
Mai zai hana boka ya
yi ɗansa ya samu.
Ya nuna cewa, bori ma
wata hanya ce ta neman magani, kamar yadda ya faɗi a cikin waƙarsa. Yadda boka ko
malami ke bayar da magani in ya isa ya bawa ɗansa ya samu ɗaukaka irin ta sa. Haka kuma a cikin waƙar ya nuna Arzika cewa
ya nemi magani a wajen malamansa domin magani ya biya buƙatar da ake nema. Ga waƙar kamar haka:
Wata rana antashe shi
lolo
Naj ji Zabarmawa na ta
Zaino! Zaino!
Zaino kowa ka cewa,
Ban san da Zabarmanci
sannan,
Naj ji Nuhwawa na ebeci!
Ban san da Nuhwanci ko
kwabo ba,
Naj ji Hulani na hwaɗinn Gujjo!
Ba jin Hillanci nikai
ba,
Sai Ga Hausawa irin mu
Naj ji suna eho! Ɓarawo!
Nac ce ‘an yi ɓarna’
Wancen bawa ba kai
shikai ba.
Na dubi dut rutsun
kasuwan nan
Sai shina tahiya tai
yanga-yanga!
Hay yas shigajirgi
lahiya lau,
Wane jihwa ko bugawa!
Sai dai nuni ɗan gaton uwa,
Nac ce biya mallanmanka
Arzika
Sun cika aiki babu wasa
Domin idan aka nazarci
wannan ɗiyan za a fahimci cewa
Arzika a kasuwa ya je ya yi sata amma ba a gan shi ba, domin a yanzu wasu suna
kiran boka da malam, boka kuwa yana da nasaba da yan bori. Wannan shi ya sa na
kawo wannan a matsayin misali.
Ga wani misali daga waƙar Ɗankwairo ta Sarkin Gombe
yadda yake nuna cewa lallai bori da malanta wani nau’i ne na magani, domin ya
nuna cewa idan yayan sarakuna suna neman sarauta sukan je gun yan bori da
malamai domin neman magani ko sa’a gunsu
Sarauta tana wurin Allah
Sarauta tana wurin wanda
jallah ya bai girma
Shehu ka biɗa ga Allah ka samu
Sai ga wani ɗan sarkin Gombe bai biɗa ga Allah ba
Ya sai babbakun tumakai
Ya sai babbakun shanu
Sai ya kiraye ýan bori
Kullum ana yi mai bori
Wawa bokaye sun kwashe
masa ƙudinsa
Bokaye sun kwace kuɗinsa
Ba shi ga Allah ba shi
ga Annabi
Ba shi da tsutsu ba shi
ga tarko
Babu kuɗin kuma babu sarauta
Babu kuɗin kuma babu sarauta
Wannan ya nuna cewa ‘yan
bori da malamai suna bayar da magani. Haka kuma Ɗan kwairo yana cewa ‘yan
bori suna bayar da magani ga waɗanda suke nema. Wannan
shi ya ƙara tabbatar mana da cewa lallai bori da malanta wani
nau’i ne na magani.
3.2 Bori Da Malantaka A
Riwayar Karin Magana
Karin magana kusan ya
mamaye kowane fanni na rayuwar Bahaushe. Yana da wuyar gaske a ce ga sha’anin
rayuwar da ba a samun Karin Magana ba, kuma wannan shi ya ba da damar kamar
yadda harshe da al’ada kan sauya su bi zamani, to kwatankwacin haka Karin magana
ke sauyawa. Don haka sau da yawa Karin magana na nuna yadda rayuwar Hausawa
take da irin abubuwan da suke mallake da shi, da wanda ba na su ba.
Za mu duba wasu Karin
magana da suke tabbatar mana da cewa Bori da malanta wani nau’i ne na magani.
Ga misali kamar haka:
An huta Bori ya kashe
Boka
In wata magana? An ce
Bori ya kashe Boka
Yau da gobe karya ta
boka
Da na sani takan kashe
boka da malam
Da malamai da boka Allah
ya fi su
Duhu ɗakin bori
Ɗakin bori, digar maganin
gujajjen bawa
Boka ci kaji, magani sai
Allah
Halin bori, halin godiya
Borin girka ba shi warka
da mayunwaci
Idan muka duba waɗannan Karin magana za mu
fahimci cewa lallai bori da malanta wani nau’in magani ne, don yana nuna
mafitar lamari ko samun sauƙin abin da ya yi tsanani ko warware wata matsala ko
biyan buƙata, da dai sauransu.
3.3 Matsayin Bori Da
Malantaka A wajen Bahaushe
Bori yana ɗaya daga cikin hanyoyin
bauta a lokacin gargajiyar Bahaushe. Baya ga Tsafi da Camfi, sai shi Bori da
Hausawa suka yi Imani da shi a wancan lokaci na gargajiya. Wanda wannan hanya
ce da ta samar wa Hausawa abubuwa da dama, baya ga hanyar bauta, Hausawa suna
amfani da wannan hanya a matsanyin wata hanya ta samar musu da magani, da kuma
kariya daga wasu abubuwan cutarwa. Baya ga lokacin gargajiya, Hausawa sun ci
gaba da wannan hanya wajen samar wa kansu magani. Wanda a yanzu kuma malanta ta
maye gurbin bori wajen bayar da magani da neman waraka ga wani al’amari na
rayuwa.
4.0 Kammalawa
Wannan aikin bayan an yi
gabatarwa an ɗan yi ƙoƙorin kawo waye Bahaushe,
sannan ma’anar bori da Malanta da magani da ma’anar bori da malantaka a taskar
adabi daga ƙarshe kuma bori da malantaka a riwayar mawaƙan baka, da Karin magana
da kuma sanin matsayinsa a wajen al’ummar Hausawa. Wanda nazarin ya tabbatar
mana da cewa lallai Bori da Malanta wani nau’i ne na bayar da magani, wanda
yake nuna mana irin yadda bori da malanta suka yi tasiri a rayuwar al’ummar Hausawa,
wanda suka ɗauke shi a matsayin wata
hanya ta samar da magani ga al’ummarta. Ta kula da hanyar adabin Hausawa
ya ƙara tabbatar mana da hakan, domin a cikin waƙoƙinsu da Karin
maganganunsu duk akwai irin waɗannan maganganu da suke
tabbatar mana da cewa bori da malanta wani nau’in magani ne a ƙasar Hausa. A
kowane ɓangare na waƙa da Karin magana
an ɗan kawo misalai da za su
sake tabbatar mana da haka.
Manazarta
Abdullahi, I. S .S (2012). “Muhallin
Magani A Adabin Bakan Bahaushe” A cikin Ɗunɗaye Journal Of Hausa
Studies, Vol. 1, Number 4. Department Of Nigeria Languages, Usmanu ƊanfodiyonUniversity,
Sokoto
Adamu, M. (1978) The Hausa Factor in West
African History. Zaria: Amadu Bello University Press.
Adamu T. M (2014). Siddabaru
A Ƙasar Hausa. Century publition Ltd, Kano.
Ahmad I. A (1984) Cututtukan ciki da
magugunansu” Kundin BA, Sashen Nazarin Harsunan Nijriya, Jami;ar Bayero, Kano
Alhassan, H; Musa, U. I da Zarruuk, R. M.
(1988). Zaman Hausawa Na Biyu Don Makarantun Gaba Da Firamare. Publications
Bureau, Lagos
Birni Tudu, S.Y (2013) “Falsafar Malanta
Cikin Littafin Ruwan Bagaja” Ruwan Bagaja In Perspectives. Eight Decades Of
Hausa Masterpiece in Prose (1933-2013) zaria: University Press
Bunza, A.M. (1990), Hayaƙi Fid Da Na Kogo:
Nazarin Siddabaru Da Sihirin Hausawa. Kundin Binciken Don Digiri Na Biyu.
Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano
Bunza, A. M (1999) Gwagwamayar
Malaman Ƙasar Hausa Da Turawan Mulkin Mallaka, Fassara daga
Turanci Zuwa Hausa. Ulama and Colonializing translation, Editing And
Introduction By Omar Bello Published by Milled stone Publishers, Sokoto
Bunza, A. M. (2002). Narambaɗa, Lagos: Ibrash Islamic
Publicaiton Centre.
Bunza, A. M (2004) “Gwagwamayar Malam Mai
Katuru da Malaman Ƙasar Hausa.(Darasi ga Malaman Yau Ƙalubale Ga Na Gobe)”. A
Taron Ƙara wa Juna Sani a Bukukuwan Shekara 200 Da Kafa
Daular Musulunci Ta Sakkwato
Bunza A. M (2006). Gadon feɗe al’ada. Tiwal Nigeria Ltd,
surulere Lagos.
Bunza A. M (2015). “Mene ne Bori? Fashin
Baƙin Ma’anarsa cikin Taskar Harshe, Adabi Da al’ada”.
Takarda da aka gabatar a taro na musamman da cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya
Mutuntar ɗan Adam (CSNLF) Jami’ar
Bayero kano ta Shirya mai taken BORI ADDINI KO AL’ADA ranar Talata 16 ga watan
yuni 2015 a harabar cibiyar, Mazaunin dindindin.
Ɗanmaigoro, A. (2010)
“Magungunan Gargajiya na Hausawa da Fulani”. Cikin Al’adu da Ɗabi’un Hausawa da
Fulani”.
Furniss, G. (1996). Poetry, Prose
and Popular Culture in Hausa, London: Edinburgh University Press, for
International Africna Institute.
Gusau, S. M. (2009). Diwanin Waƙoƙin Baka: Zaɓaɓɓun Matanoni na Waƙoƙin Baka na Hausa, Kano: century Research
and Publishing Limited.
Gusau, S. M (2014). Diwanin Waƙoƙin Baka: Juzu’I Na biyu, Kano: century Research
and Publishing Limited.
Imam, A. (1933) Ruwan Bagaja.
Zaria: NNPC
Jinju, H. (1985), “Asalin Hausawa Da
Harshensa” Maƙala Da Aka Gabatar A Taron Ƙasashen Duniya Akan
Hausa Da Adabi Da Al’ada. Jami’ar Bayero, Kano.
Malumfashi I; Ibrahim N. M (2014). Ƙamusun Karin Maganar
Hausa. Garkuwa
Publications, Kaduna.
Sallau, A.B.S.(2005) “A Sha a yi Wanka,
Magani ga ɗan na Gada: Nazari da
Tsokaci kan Magungunan Gargajiya na Wanzaman Hausawa a Wannan Zamani” Takarda
da aka Gabatar a Sas1hen Hausa. Dutsin-ma: babbar Kwalejin Ilimi ta Isa Kaita
Schuh, R.G. and Yalwa, L.D. (1993), Hausa
(illustration of the IPA) Journal of the international Phonetic Assocition. 23
(2): 77-82.
Tremearne, A. J (1914) The Ban of the Bori: Demons and Demon Dancing in West and North Africa. London: Health Creation and Ouseley Ltd
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.