Citation: Musa Shehu & Muhammad Mustapha Umar (2017). Sasantawa a Bahaushen Tunani: Nazari Daga Rikicin Boko Haram. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 5. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
SASANTAWA
A BAHAUSHEN TUNANI: NAZARI DAGA RIKICIN BOKO HARAM
Na
Da
Muhammad
Mustapha Umar
GABATARWA
Sasantawa kalma ce da ke
nuni da sulhu wanda akan gudanar tsakanin mutum da mutum ko tsakanin ƙabila da ƙabila
ko tsakanin mabiya addinai mabambanta ko tsakanin ƙasa da ƙasa
domin kawo ƙarshen wata fitina da
ke yi wa zaman lafiya barazana. Ƙasar
Hausa ta jima cikin gumurzun tashe-tashen hankula, kama daga rigingimun addini
da ƙabilanci da siyasa da ɓangaranci
da sauransu. A duk lokacin da irin wannan matsala ta taso akan yi ɗauki-ba-daɗi
domin huce haushi ko ganin bayan abokin husuma ko kawo ƙarshen matsalar, amma yunƙurin ya faskara. A ƙarshe, tilas a zauna tabarmar sasantawa
domin a ga bayan matsalar. Babban tashin hankalin da ke damun ƙasarmu Nijeriya a yau shi ne rikicin Boko Haram wanda ya kwashe shekaru kusan
bakwai ana artabu. An yi amfani da ƙarfin
soje da dabarun Yahudu da Nasara na taron dangi amma har yau ba a kai ƙarshensa. Manufar wannan takarda ita ce,
fito da tunanin Bahaushe na dabarun da yake amfani da su wajen sasanta rikici
musamman irin na Boko Haram, wataƙila
a yi gamo da katar na shawo kan rikicin da ya ƙi ci
ya ƙi canyewa. Ban ce ita kaɗai
ce mafita ba, amma na so a yi taron dangin tunani a ga ko za a samu madafa. Don
haka, tattaunawar takardar zai kasance kamar haka:
2.0
MENE NE BOKO HARAM
Boko Haram ƙungiya ce mai iƙirarin fafutikar kafa gwamnatin
Musulunci musamman a Arewacin Nijeriya. Sunan ƙungiyar
ta asali shi ne Jama’atu Ahlus Sunnah
Lid-Da’awati Wal Jihad. Sun samu wannan suna ne na Boko Haram daga mutane
saboda irin ƙyama da haramta
karatun boko da wasu abubuwa da ƙasashen
Yamma suka zo da shi a duk lokacin da suke wa’azinsu saboda ya saɓa wa
tafarkin Musulunci.[1]
A cewar shugaban ƙungiyar,
duniya ba ta bisa turbar addinin Musulunci, don haka dole a barranta da
abubuwan da masu shugabantanta suka taho da shi musamman waɗanda
suka saɓa wa
koyarwar Musulunci.[2]
Ƙungiyar ta fara kafuwa ne a wajajen
shekarar 2001, amma ta fito sarari ne a shekarar 2009 lokacin da ta fara ƙaddamar da hare-hare a Arewacin Nijeriya
musamman a yankin Maiduguri. Shugaban ƙungiyar
na farko shi ne Muhammad Yusuf wanda aka zargi jami’an ‘yan sanda da kashewa a
shekarar 2009. Bayan mutuwar Muhammadu Yusuf ne ƙungiyar
ta naɗa
Abubakar Shekau a matsayin sabon shugaba.
A farko, ƙungiyar ta fara neman ‘yan boko su aje
aiki su kama sanaa idan gwamnati ba za ta sauya akala zuwa ga shariar Musulunci
ba. Daga nan ta fara takin saƙa da
dokokin gwamnatin Ɗagutu.
Fitinar ta faro ne lokacin da ɗaya daga cikinsu ya rasu
wasu suka tafi maƙabarta
bisa babura ba tare da hular kwano ba. Tilasta sa hular kwano ne tushen rikicin
, inda ‘yan’sanda suka fara kashe su, su kuwa suka ɗauki
fansa. Tun a wannan lokaci ne al’amurra suka ci gaba dagulewa har zuwa halin da
ake ciki yau.
3.0
HARE-HAREN ƘUNGIYAR
BOKO HARAM A KAFOFIN YAɗA LABARAI
Haƙiƙa
‘yan jarida sun taka rawa wajen ƙara
rura wutar rikicin Boko Haram a Nijeriya ganin yadda suke rura rahotanninsu a
kan rikicin. A shekarar 2013 ‘yan ƙungiyar
ta Boko Haram sun kai wani mummunar hari a garin Baga da ke jihar Barno, inda
aka kashe aƙalla mutum 185 tare
da banka wa garin wuta. A wani ƙididdiga
da Jaridar Aminiya ta wallafa a watan Maris ɗin
shekarar 2014, tsakanin farkon watan Janairu zuwa watan Maris ɗin shekarar
2014, sun kasance makonnin laƙume
rayuka a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, inda hare-haren da ake jingina su
ga ƙungiyar Boko Haram suka jawo mutuwar
dubban mutane da ƙone
garuruwa da dama, tare da sanya dubban jama’a yin hijira zuwa garuruwa
daban-daban.[3]
‘Yan ta’addan da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun ƙaddamar da miyagun hare-hare da fara
karya kumallo da wani Coci a jihar Adamawa a ranar 28 ga watan Janairun 2014,
mutum 30 suka halaka. A wannan rana cikin dare ƙungiyar
ta kai wani hari a ƙauyen
Kawuri da ke ƙaramar hukumar
Konduga a jihar Barno, rahotanni suka nuna cewa, an hallaka mutum 83, yayin da
aka raunata wasu, aka kuma banka wa gidajen ƙauyen
baki ɗaya
wuta da masallatai suka ƙone ƙurmus. Ana cikin jimamin wannan hari ne,
sai maharan suka faɗa garin Konduga a ranar 11
ga watan Fabrairun shekarar, nan ma suka kashe mutum 34 tare da jikkata da dama
da kuma ƙona gidaje masu yawa.
A ranar 15 ga watan
Fabrairun, sai ‘yan bindigar da ake zaton ‘yan Boko Haram ne suka auka wa garin
Izge da ke jihar Barno suka kashe sama da mutum 106. Haka ma, a ranar laraba 19
ga watan Fabrairun, maharan suka kashe mutum 60 a garin Bama da ke jihar Barno,
suka kuma banka wa gidajensu wuta. Daga bisani shugaban ƙungiyar ta Boko Haram ya fitar da
sanarwar cewa, su ne suka kashe Sheikh Muhammad Auwal Albani na Zariya.[4] A ranar
27 ga watan Fabrairun kuma, ‘yan ƙungiyar
ta Boko Haram suka kai wani harin a garin Michika da Shuwa suka kashe mutum 28.
Wani harin da ya ɗaga hankalin jama’a har da ƙasashen waje shi ne, wanda ‘yan ƙungiyar ta kai ranar 24 ga watan
Fabrairun shekarar 2014 a wata makaranta a garin Buni Yadi da ke jihar Yobe aka
kashe ɗalibai
59. A ranar asabar 1 ga watan Maris ɗin
shekarar 2014, an kashe mutum 25 a yankin Askira a wani harin bamabamai ta sama
da dakarun Nijeriya suka kai a garin Daglun. A ranar lahadin makon, ‘yan ƙungiyar suka kai hari a garin Mainok da
ke jihar Barno suka kashe ƙimanin
mutum 97 tare da ƙone
gidaje da dama. Haka kuma, a ranar ne aka samu fashewar bamabamai a unguwar
Binta Suga a Ngomari cikin birnin Maiduguri waɗanda
suka yi sanadiyyar mutuwar fiye da mutum 50. Bayan kwana ɗaya
kuma, aka kashe mutum 35 a garin Mafa da ke jihar Barno.
A shekarar 2015 aka bayyana
cewa, ƙungiyar Boko Haram ta kai wani ƙazamin hari mafi muni a tarihin rikicin
da ke ci gaba da wakana a Arewa maso gabashin Nijeriya a garin Baga da ke jihar
Borno aka bayyana cewa, an rasa rayukan mutane ƙimanin
dubu biyu (2000) da kuma ƙone
garin ƙurmus haɗi da
wasu ƙauyuka16.[5]
4.0
TUNANIN MUTANE A KAN RIKICIN ƘUNGIYAR
BOKO HARAM
Boko Haram ƙungiya ce da ke iƙirarin da’awar Musulunci, sai dai masana
da malaman addini da sauran jama’a sun musanta hakan. Masana addinin Musulunci
sun bayyana cewa, babu inda Musulunci ya yi umurni da kashe rayukan mutane ba
tare da haƙƙin shari’a ba. Babu
inda aka ce a kai wa Musulmi farmaki suna cikin Sallah a tayar musu da
bamabamai a bi su ana harbi da bindiga. Ko a kai wa Musulmi hari suna cin
kasuwa a buɗe musu wuta a kwashe dukiyoyinsu da
sunan jihadi. Ƙari ga tabbacin cewa,
babu Musulunci a cikin da’awarsu shi ne, an sha kawo rahoto a gidan rediyon BBC
Hausa da Faransa da Jamus na kama ‘ya’yan ƙungiyar
a lokacin kai hari a wasu wurare waɗanda
aka tabbatar ba Musulmai ba ne, Kirista ne. Jama’a da dama na kallon rikicin
Boko Haram shiri ne kawai na gwamnatin Nijeriya (2011-2015) domin a gurgunta
wani yanki na ƙasar. Fitacciyar ‘yar
siyasar nan wato Naja’atu Muhammad ta
bayyana cewa: “Da dama daga cikin tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Arewacin
Nijeriya gwamnati ke haddasa su”.[6]
Shi kuma wani malamin
addinin Musulunci Sheikh Umar Farouk
cewa ya yi, rigingimun Boko Haram shiri ne kawai na tarwatsa Arewa da
siyasarta. A fahimtar malamin, tashe-tashen hankulan da suke ci gaba da faruwa
ana laɓawa
ne kawai a cikin rigar Boko Haram ta Yusufiyya ana aikata aika-aika. Amma a
mizanin hankali da tunani an san ba ainihin mabiya Boko Haram ne ke wannan
ta’addanci ba. A kan haka malamin yake bayyana cewa, akwai wata maƙarƙashiya
a ciki, ya Allah ta siyasa a buƙatar
ɗorewar
mulki ko wani abin daban. Babbar manufar ita ce, wani gawurtaccen shiri ne na
tarwatsa da wargaza tattalin arziki da siyasar al’ummar Arewa.[7] Waɗannan
ra’ayoyi suna da ƙamshin
gaskiya musamman idan aka yi la’akari da irin riƙon
sakainar kashi da gwamnatin da ta gabata (2011-2015) ta yi wa rikicin a wancan
lokaci. Ƙara tabbatuwar hakan kuma shi ne, bayan
da gwamnatin 2011 ta sha kaye a zaɓen
2015 aka kafa sabuwar gwamnati, sai ga shi ana ta bankaɗo
almundahana da yasoso da kuɗaɗen
da aka ware domin yaƙi da
ta’addancin Boko Haram wanda ya hana al’ummar ƙasar
sakewa da walwala da ci bayan tattalin arziki. Masu sharhi a kan al’amurran yau
da kullum suna ganin zaluncin gwamnatin Nijeriya ya haifar da ƙungiyar Boko Haram. Bayan ɗimbin
arzikin da Allah ya albarkaci ƙasar
da shi, amma kusan kashi tamanin cikin ɗari
na ‘yan ƙasar suna fama da talaucin gaske, ga
rashin aiki da ya yi wa matasa katutu. Wasu ‘yan tsirarun mutane sun mamaye
arzikin ƙasar sun kai ajiya wasu ƙasashe sun bar mutane cikin wahalan
rayuwa. A tunanina, Boko Haram ƙungiya
ce kawai ta ta’addanci da aka kafa da ɗaurin
gindin ƙasashen Yamma da ‘yan barandarsu daga
ciki da wajen Nijeriya domin cim ma wata manufa maras alfanu.
MENE
NE RIKICI
Ƙamusun
Hausa (2006:372) ya bayyana ma’anar rikici da hargitsi. Godwin Onu (2009:84)
cewa ya yi, rikici shi ne wanzuwar taƙaddama
tsakanin mutane ko ƙungiyoyi.
Rikici dai wani abu ne da ɗan Adam ba zai iya hana
aukuwarsa a rayuwa ba, domin matuƙar
ana haɗuwa
ko a samu wata alaƙa
tsakanin mutane, dole wata rana a samiu saɓani
komai tsananin ƙauna
da ke tsakani. Sanin haka ya sa Hausawa ke da karin maganar da ke cewa, “Zo mu
zauna, zo mu saɓa”.
Tarihin ƙasar Hausa cike ya ke da ƙuran yaƙe-yaƙe da rikice-rikice tun zamanin zamunna
har zuwa wannan lokaci. Ta fuskar yaƙe-yaƙe, ƙasar
Hausa ta fuskanci yaƙi
iri uku. Akwai yaƙe-yaƙen duhun kai wanda aka gudanar kafin
shigowar Musulunci. Akwai yaƙe-yaƙen jihadi wanda Mujaddadi Ɗanfodiyo ya ƙaddamar domin jaddada addinin Musulunci.
Sai kuma yaƙe-yaƙen Turawa da aka fafata domin mulkin
mallaka. Ta fuskar rikice-rikice kuwa, a yau ƙasar
Hausa na fama da rikice-rikice masu nasaba da dalilai mabambanta. Akwai rikicin
mai nasaba da addini, akwai na siyasa, akwai na ƙabilanci,
akwai na sarauta, akwai na makiyaya da manoma, akwai na zamantakewa, ga su nan
dai. To sai dai kuma, babban rikicin da ke ci gaba da tayar da hankalin
jama’armu da ma ƙasa
baki ɗaya
shi ne na Boko Haram wanda ake dangantawa da addini ko siyasa. A kan wannan ne
wannan takarda za ta fito da tanadin Hausawa na sasanta rikici makamancin
wannan domin a jaraba amfani su ga rikicin Boko Haram wataƙila a samu maslaha domin Hausawa na
cewa, “magani sai da gwaji”.
MENE
NE SASANTAWA
Sasantawa (Conflict Resolution) al’amari ne mai muhimmancin
a rayuwar kowace al’umma. A duk lokacin da rigingimu ko tashe-tashen hankula ko
ta da zaune tsaye suka wanzu a tsakanin al’umma, hanya mafi dacewa don warware
su cikin ruwan sanyi ita ce sasantawa. Dangane da ma’anarta kuwa, masana sun yi
tsokaci a rubuce-rubucensu da suka shafi rikici da sasantawa. Sasantawa wata
hanya ce ta samar da maslaha a kan wani rikici tsakanin ɓangarori
biyu. Rikicin kuwa na iya kasancewa wanda ya shafi mutum ko kuɗi ko
kuma siyasa. Duk lokacin da wani rikici ya taso, hanya mafi dacewa na warware
shi shi ne sasantawa.[8]
A Ƙamusun Hausa (2006), sasantawa shi ne:
“Shiga tsakanin masu husuma biyu, ko kuma sulhu.”[9] A cikin Ƙamusun Oɗford
(bugu na bakwai) an kawo ma’anar sasantawa da cewa: “Yanayi ne na warware ko
daidaita matsala, jayayya, da sauransu.”[10]
Balarabe (2013) ya kawo ma’anar sasantawa da cewa, sasanta jayayya ko taƙaddama, ko kuma yayyafa ruwa, ko daƙushe kowane irin nau’in rikici.[11]
Sasantawa shi ne shiga tsakani da nufin kawar da ko kawo ƙarshen husuma ta hanyar tattaunawa.[12] Gulbi
(2016) ya kira sasantawa da sulhu, wanda ya ƙunshi
duk wata hanyar tattaunawa da za a yi amfani da ita domin shawo kan wata
matsalar yaƙi ko tarzoma ko
bijirewa ko tawaye tsakanin masu jayayya da nufin samar da zaman lafiya mai ɗoewa.[13]
Idan aka rairaye waɗannan
ma’anoni sarai, za a ga dukkansu bori ɗaya
suke yi wa tsafi, wato kowanensu ya kalli sasantawa da warware rikici ta hanyar
siyasa ba tare da kai ruwa rana ba. A nawa tunani, sasantawa wata dabara ce ta warware
ko kawo ƙarshen wani rikici, ko kawo ƙarshen duk wata matsala da ta shiga
tsakanin wasu mutane ko ƙabilu
ko addinai ko ƙasa da ƙasa cikin ruwan sanyi ba tare da an ɗauki
artabu ba.
7.0
DALILAN SASANTAWA A TUNANIN BAHAUSHE
Al’ada muhimmin al’amari ne
a kowace irin al’umma. Bunza (2013) yana cewa,
Ci gaban al’umma yakan
dogara ne ga riƙon
al’adunta na gado. A tsarin dokokin al’adu na Nijeriya an ce, al’ada ita ce
tarsashin hanyoyin rayuwar mutane na yunƙure-yunƙurensu wajen tunkarar abubuwan da ke yi
wa rayuwarsu barazana, wanda zai fassara rayuwar jin daɗinsu,
siyasarsu, zamantakewarsu, tattalin arzikinsu, sha’awarsu, addininsu, da ɗabi’u
ko halayensu, tsare-tsarensu da shirye-shiryensu waɗanda
za su bambanta su da wasu ba su ba.[14]
Babu shakka, duk wani abu da
aka gudanar ko ake gudanarwa a rayuwa akwai dalilin gudanar da shi, ko an san
shi, ko ba a sani ba. A duk lokacin da maganar sasantawa ta taso, akwai wani
al’amari da ya auku tsakanin ɓangarori biyu na rashin
jituwa da ke ƙoƙarin hana ruwa gudu tsakaninsu. Dalilan
da ke kawo maganar sasantawa a tunanin Hausawa suna da yawa: Ga bayanin wasu
daga ciki:
7.1
HANA AUKUWAN RIKICI/KAWO ƘARSHEN
RIKICI
Sau da yawa idan aka hango
rikici na ƙoƙarin kunno kai tsakanin wasu mutane ko
tsakanin ƙabilu ko addinai ko ɗasa
da ƙasa, akan yi ƙoƙarin
daƙile shi ta hanyar hawa teburin sasantawa
tun bai kai ga munana ba. Masana da dama suna da ra’ayin cewa, sasantawa ita ce
hanya mafi dacewa a yi amfani da ita domin kawo ƙarshen
kowane irin rikici. Idan aka hangi rikici na kunno kai ba a samu nasarar daƙile shi ba har ya kai ga bayyana,
al’amurra suka cakuɗe, aka rasa gaba da baya,
daga nan ne za a fara tunanin a zauna sasantawa domin warware matsalar. A
lokuta da dama, rikici kan auku har a kai ga zubar da jini da hasaran dukiya
domin huce haushi ko ƙwato
‘yanci, amma hakan ya kasa samuwa, a ƙarshe
sai ka ga an fara kira zuwa ga teburin sasantawa. Saboda haka, maganar
sasantawa kan taso ne a duk lokacin da aka hango rikici na son ɓallewa
ko kuma idan ya riga ya auku.
7.2
SAɓANIN FAHIMTA
Da yawa daga cikin
rikice-rikicen da ke aukuwa a ƙasar
Hausa musamman rikicin addini (Musulunci) da ke yawan aukuwa tsakanin mabiyansa
(Hausawa), saɓanin fahimta ke kawo su. A nassi ɗaya
sai wani ɓangare ya kalle shi ta wata fuska, a
yayin da wani ɓangare zai fassara shi da wata fahimta
ta daban. Fahimtar “Boko Haram” a kan nassoshin da suka ambaci jihadi da hijira
da kafa hukumar Musulunci dole a sake bitar su. A gurguwar fahimtarsu, karatun
Boko bai halatta ga Musulmi ba, don haka tilas a jingine shi, wanda suna da
tabbacin ba abu ne mai yiyuwa ba, kuma bai ci karo da karantarwar Addinin
Musulunci ba kamar yadda Malamai suke bayyanawa. Rikicin ƙungiyoyin Izala da Ɗariƙa da
Shi’a da ke yawan faruwa a ƙasar
Hausa babban misali ne da ke aukuwa a sakamakon saɓanin
fahimta tsakaninsu. Irin wannan yanayi kan haifar da cece-ku-ce da haddasa
husuma tsakanin ɓangarorin, har wani lokaci a
kai ga yin artabu. Saboda haka, a duk lokacin da aka ga irin wannan matsala ta
kunno kai gadan-gadan, daga nan buƙatar
sasantawa za ta taso domin warware matsalar.
Baya ga saɓanin
fahimta, akwai wani saɓani da kan auku tsakanin
mutane kamar tsakanin aboki da aboki ko tsakanin mata da miji ko tsakanin ɗa da
mahaifi ko tsakanin maigida da yaro ko tsakanin talakawa da masu mulki, wanda a
lokuta da dama kan lalata dangantakar da aka jima da ginawa. Saɓani
kan haifar da mutuwar aure, ko raba abokantakar tun yaranta zuwa girma, ko kawo
ƙarshen hulɗar
zamantakewar maigida da yaronsa, ko yanke zumunta tsakanin ‘yan’uwa. Idan irin
haka ya auku, akwai buƙatar
sasantawa domin dawo da dangantakar da ta salwanta, a ci gaba da rayuwa kamar
yadda aka saba.
7.3
RASHIN CIKA ALKAWALI/KARYA YARJEJENIYA
“Kyawon alkawali cikawa”
kuma “Dattijo ba ya magana biyu”. A addinance, an yi horo da cika alkawali,
rashin cika shi alama ce ta munafunci. Rashin cika alkawali/yarjejeniya babbar
musiba ce da ke haddasa fitina da lalata zamantakewa. Duk lokacin da ɓangarori
biyu suka ƙulla wata yarjejeniya
ko alkawali, fitina na iya ɓarkewa idan ɓangare
ɗaya
ya saɓa,
dangantakar da ke tsakani na iya lalacewa. Rikicin Boko Haram da ya ƙi ƙarewa
a yau, rashin cika alkawali da rashin mutunta yarjejeniyar da aka ƙulla na daga cikin dalilan faruwar
hakan. Yana da kyau a sake duba yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla tsakanin Boko Haram da Hukuma.
Kwamitocin da aka naɗa, waɗanne
alkawulla suka yi da Boko Haram? A sake duba wa ya saɓa?
Me ya sa ya saɓa? Yaya za a yi a cika alkawullan da aka
ƙulla? Madalla da musayar fursunoni da
aka fara yi tsakanin Boko Haram da Hukuma domin zai taimaka wajen warware taƙaddamar da ke tsakani. A ƙasashen duniya ma akan gudanar da
musayar fursunoni a ƙoƙarin warware husuma. Saboda haka, kamata
ya yi Hukuma da Boko Haram a zauna a sake bitar sauran alkawulla da
yarjejeniyoyin da aka ƙulla,
a mutunta su don kawo ƙarshen
matsalar.
7.4
YAUDARA/HA’INCI
Yaudara ko ha’inci ɗabi’u
ne marasa kyau da sukan gudana tsakanin mutane ko ƙasashe. Galibi yaudara ko ha’inci
nau’o’i ne na cin amanar zamantakewa. Ɗabi’u
ne masu haddasa ruɗani da raba kawunan mutane.
Mutane da dama ba su cika bar wa Allah ba yayin da aka yaudare su, sukan ɗauki
alwashin ɗaukar fansa ko ta halin ƙaƙa
domin ramuwar gayya. Idan aka fahimci irin haka na son faruwa, akan yi ruwa da
tsaki na ganin an sasanta masu husumar kafin a kai ga ɗanyen
aiki.
8.0
DABARUN SASANTAWA A TUNANIN BAHAUSHE
Wasu masana na ganin
hanyoyin sasantawa kan bambanta sakamakon nau’in husuma ko ƙumshiyarta ko tarihinta ko al’adun masu
husumar.[15]
Godwin 2009 ya ƙara
da cewa, ana amfani da tanadin al’ada da koyarwar addini wajen sasantawa. Ya
bayyana cewa, a addinin Musulunci, duk husumar da ta faru tsakanin ɓangarori
biyu akan sasanta ta bisa tanadin Addinin Musulunci. Haka ma yake a addinin
Kirista. Hanyoyin sasantawa na gama gari da Malamin ya kawo sun haɗa da
yin yarjejeniya, da samun mai sasantawa, da samun wakilan masu husuma, da sa
hannun masu shari’a da masu ruwa da tsaki a kan sasanta husuma. Hausawa na
cewa: “Zo mu zauna zo mu saɓa”. Babu wata al’umma da ke
rayuwa a doron ƙasa
da ba a samun matsala a zamantakewar yau da kullum. To sai dai idan matsala ta
auku, akan yi ƙoƙarin sasantawa domin ci gaba da rayuwa
cikin lumana. Al’adar Hausawa ba ta rage komai dangane da wani abu da ya shafi
rayuwarta ba. Akwai tanadi na musamman da al’da ta yi domin sasanta duk wata
fitina da ta kunno kai take ƙoƙarin kawar da zaman lafiya daga shimfiɗar
da aka yi mata. Daga cikin dabaru ko hanyoyin sasanta husuma sun haɗa
da:
8.1
SAMAR DA MASU SASANTAWA
Abu na farko da ya zama
wajibi a samu domin sasanta husuma shi ne masu sasantawa, wato waɗanda
za su shiga tsakanin masu husuma su daidaita al’amurra. Al’adar Hausawa ta yi
tanadin mutane na musamman da ta ɗora
wa alhakin sasanta duk wata husuma da ta taso a cikin al’ummarta. A irin fitina
ta Boko Haram, malaman addini na kowane ɓangare
na kowace aƙida sai sun sa baki.
Tilas a nemo wasu malamansu a yi zama da su. Matuƙar
babu malamansu ciki, komai aka ƙulla
dole ya kwance. Kure ne babba malaman gwamnati su yi ale-ale a ciki a samu
nasara. A da, da gwamnati suke yaƙi,
malamin gwamnati kuwa ɗan gwamnati ne. Don haka,
dole a samu malamai ‘yan ba ruwanmu su shiga tsakanin sasantawar.
8.2
SAURAREN MASU HUSUMA
Saurare ba zai yiwu ba sai
an zauna da kowa da kowa. Ba za a yi saurare yau a yi sulhu yau ba, domin ba a
fafe gora ranar tafiya. Bayan an saurara sai a tsayar da yaƙi je a yi tunanin ranar mayar da gami.
Bahaushe ya yi imani da cewa, karen duk da ya yi kora shi ke gwajin hanya.
Wanda ya tayar da ƙayar
baya shi zai amayo ƙorafe-ƙorafensa, wanda ake yi wa tawaye ya kare
kansa. Idan aka saurara da kunnen basira, dole a ga wurin da salka ka tsatsa. A
sake tunanin yin haka da Boko Haram dare bai yi ba.
8.3
YARJEJENIYA
Bayan an yi saurare, sai
maganar yarjejeniya. A lokacin da za a yi yarjejeniya tsakanin masu husuma babu
wanda zai samu yadda yake so ɗari bisa ɗari.
Dole kowane ɓangare ya sassauto da buƙatunsa a haɗu
tsakiya domin a samu maslaha. Bayan an yi yarjejeniya an samu haɗin
kan masu husuma, abu na gaba shi ne sa ido wajen ganin an mutunta yarjejeniyar
ba tare da karya shi ba. Samun haka shi zai sa a ga bayan husumar. Wannan ya
tabbata a lokacin mulkin Sarkin Musulmi Ahmadu Rufa’i wanda ya kawo ƙarshen hare-haren da ake kai wa juna
tsakanin Sakkwato da Kabi ta hanyar yarjejeniyar sulhu da Sarkin Kabi Toga
(1860-1863). Sarkin Musulmi Ahmadu ya kuma ƙulla
yarjejeniyar zaman lafiya da Sarkin Gobir Ibrahim ɗan
Ali. Shi ma wanda ya gadi Ibrahim ɗan
Ali ya sake ƙulla kyakkywar hulɗa ta
zaman lafiya da Sarkin Musulmi Umaru da Abdurrahman.[16]
8.4
TSAGAITA WUTA
Bayan an samar da
yarjejeniya, sai a tsagaita wuta. Idan aka samu tsagaitawar wuta, zaman lafiya
ne zai biyo baya. Sasantawa ba zai yiwu cikin ruwan harsasai da bamabamai ba.
Dole sai an sarara amon wuta domin mutunta yarjejeniyar da aka cim ma. Duk wani
rikici da ke aukuwa, tun daga rikicin auratayya da na addini da na ƙabilanci da na kasuwanci ko sarauta ko
na makiyaya da manoma a ƙasar
Hausa, ana buƙatar jingine makamai
a yayin da ake shirin sasantawa. Hakan zai sa a samu nasarar sasantawar, domin
a lokacin zukata sun fara sanyi, alwashin ɗaukar
fansa ya yi rauni, ƙurar
da ta rufe zuciya ta fara yayewa. Dubi yadda tsagaita wutar yaƙi tsakanin daular Usmaniyya a lokacin
Sarkin Musulmi Ahmadu Rufa’i da daular Kabi a lokacin Sarkin Kabi Toga wanda
aka kira “Lafiyar Toga” wanda ya ba da kyakkyawar yanayi, da ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin
daulolin biyu.[17]
9.0
SASANTA RIKICIN BOKO HARAM A BAHAUSHEN TUNANI
Kowace al’umma ta duniya da
irin matsalar da ke ci mata tuwo a ƙwarya,
sai dai ba za a ce an kasa shawo kanta ba sai dai idan ba a yi amfani da
dabarun da suka dace wajen warware ta ba. A tarihin rikicin duniya, an yi yaƙin duniya na farko da na biyu kuma an
wayi gari sai dai a ba da tarihinsu. A gida Nijeriya an yi fama da yaƙin Biyafara da rikicin Maitatsine, amma
duk an ga bayansu. Rikicin Boko Haram da ya zama ƙadangaren
bakin tulu a yau za a iya ganin bayansa matuƙar
an jaraba amfani da waɗannan matakai:
9.1
SULHU
Sulhu shi ne tattaunawa
cikin hikima tsakanin ɓangarori biyu ko ƙasashe biyu musamman domin warware
matsala ko kawo ƙarshen
rikici.[18] Sulhu
shi ne sasantawa ko shirya tsakanin wani da wani.[19] Sulhu
wata hanya ce ta tattaunawa domin warware wata matsala tsakanin mutum da mutum.
Misali, akan sasanta tsakanin mata da miji idan wata matsala ta faru, ko
tsakanin aboki da aboki ko maigida da yaronsa ko maƙwabci da maƙwabci ko al’umma da al’umma.[20] Saboda
haka ana iya cewa, sulhu shi ne sasanta husuma da ta wanzu tsakanin wasu mutane
ko ƙasashe domin warware husumar. Sulhu wani
babban makami ne da ya kamata a yi amfani da shi wajen shawo kan rikicin Boko
Haram a Nijeriya. Kamata ya yi a nemi wakilan wannan ƙungiya da wakilan gwamnati a zauna
teburin sasantawa a ji cikakken manufofin ƙungiyar
da buƙatocinsu, sa’annan a nemi mafita.
Bayanai sun nuna an sha yin
farfagandar zaunawa sulhu amma ba a ba shi muhimmancin da ya dace ba. A cikin
shekarar 2016 ƙungiyar ta sako wasu
daga cikin ‘yan matan Chibok da ta kama fiye da shekara biyu wanda mutane ke
ganin musayar fursunoni ne aka yi da ‘yan ƙungiyar
aka saki wasu kwamandodinsu. Sai dai gwamnati ta ƙaryata
cewa ta saki wasu ‘ya’yan ƙungiyar
a madadin ‘yan matan na Chibok. Rashin yin sulhu da Boko Haram tun lokacin da
suka kunno kai aka so a yi amfani da ƙarfin
bindiga don murƙushe
su, shi ya kawo halin da muke ciki a yau. Babu tsananin bala’in yaƙi da hasaran rayuwa da dukiya da za ta
hana a hau kujerar sulhu da abokan fafatawa. Dole mu jingine bambance-bambancen
kowane irin addini mu zauna da abokan yaƙi mu
kai ƙarshen wannan musiba. Rashin ba sulhu
muhimmanci takkwalci ne ga shugaba, daƙiƙanci ne ga hukuma, dambala ce ga abokan
yaƙi, hauka ce ga mutanen ƙasa, jahilci ne ga ma’ilmanta. Babu ƙasar da ba a yi yaƙi ba, babu ƙasar da ba a yi sulhu ba. A duk duniyar
da ake yaƙi, idan an zauna sulhu
ba a karanto ƙazantaccen tarihin da
ya gabata.[21]
Masu ganin rikicin Boko Haram ba ya buƙatar
sulhu marasa tunani ne, maƙiya
ne masu son ganin Arewa ta durƙushe.
Dubi tarihin gabar da ke tsakanin Sakkwato da Kabi wanda aka sha ɗauki-ba-daɗi,
daga bisani aka ƙulla
yarjejeniyar zaman lafiya da aka kira “Lafiyar Toga” a lokacin Sarkin Kabi
Toga. Wannan mataki ya taimaka wajen samun zaman lafiya tsakaninsu.[22]
9.2
AMFANI DA MALAMAN ADDINI
A duk lokacin da al’amurra
suka dagule, Malaman addini ne kan gaba wajen daidaita su. A al’adar Hausawa,
duk lokacin da wata matsala ta kunno kai mai nasaba da addini, malamai ake sawa
gaba don shawo kansa. Malaman addinin Musulunci na da rawar da za su taka wajen
shawo kan matsalar Boko Haram, ganin cewa ‘yan ƙungiyar
suna farfagandar kafa daular Musulunci ne. Saboda haka, dole gwamnati ta sanya
su cikin waɗanda za su jagoranci tattaunawar sulhu
da ƙungiyar ta Boko Haram. Haka ma, akwai buƙatar Malaman su riƙa wayar da kan mutane dangane da illolin
ƙungiyar, da kuma yadda da’awar ƙungiyar ta yi hannun riga da koyarwar
addinin Musulunci.
9.3
SAMAR WA ‘YAN ƘUNGIYAR
BOKO HARAM MUHALLI A CIKIN HUKUMA
A duk lokacin da wani ke ƙoƙarin
hamɓarewa
daga cikin jama’a saboda wata fahimta tasa, kamata ya yi a sa hikima a jawo shi
a tafi tare da shi. Idan ma akwai shugabanci, a sa shi cikin ‘yan majalisa.
Abin nufi shi ne, duk ‘ya’yan ƙungiyar
da suka ajiye makamai a yi ƙoƙarin samar musu aikin yi a cikin
gwamnati, sauran waɗanda ba su aje makaman ba a
yi musu alkawalin ba su aiki a cikin hukuma. Dalili kuwa shi ne, da yawa daga
cikin ‘yan ƙungiyar sun shige ta
ne saboda talauci da rashin aikin yi da za su iya dogara da kansu, sai aka yi
amfani da kuɗin da ba su taka kara ba aka ja
ra’ayinsu. Da gwamnatin 2015 za ta yi wa Boko Haram kamar yadda gwamnatin
‘Yar’adua ta yi wa tsagerun Neja Delta na yi musu afuwa da samar musu ayyukan
yi, wataƙila a kawo ƙarshen rikicin. Rashin aikin yi babbar
musiba ce a cikin al’umma, domin zai iya jefa mutane hanya mara ɓullewa,
su shiga fashi da makami ko ƙungiyoyin
aisiri ko na tsafi ko ta’addanci irin Boko Haram.
A duk inda ɗan
adawa ko tawaye yake, jawo shi kusa ake yi a tafi tare. Dubi yadda Sarkin
Musulmi Ahmadu ɗan Atiku ya yi da Sulluɓawa
na kawo ƙarshen gabar da ke tsakaninsu, ya jawo
su a jiki kusa da mulkinsa har ya shawo kansu suka riƙa bin doka da umurni, shi kuma yana kula
da rayuka da dukiyoyinsu a kowane lokaci.[23] A
siyasar ƙasar nan ma, bayan an ci zaɓe
akan nemi ‘yan adawa su taho a haɗa
kai domin ciyar da ƙasa
gaba kamar dai yadda ya faru a siyasar NPN da GNPP a wancan lokaci da dai
sauransu.
9.4
AURATAYYA TSAKANIN BOKO HARAM DA WASU
Aure na daga cikin manyan
abubuwan da da ke ƙulla
zumunta da mayar da mutane abu ɗaya da ƙulla hulɗa ta
arziki tsakanin wannan ƙabila
da waccan. Ƙulla auratayya
tsakanin ’yan ƙungiyar Boko Haram da
wasu ko da zauna gari banza ne (mata masu zaman kansu), zai sa a sami
kyakkyawar dangantaka, za a iya samun asirransu, da maɓoyarsu,
da waɗanda
ke ba su gudunmuwa da ɗaure musu gindi. Wannan ya
tabbata a lokacin da wasu daga cikin ‘yan matan Chibok suka kuɓuta
daga hannun Boko Haram, inda ake samun bayanan sirrin ƙungiyar a wajensu. Sarkin Gulbi 2016 ya
bayyana cewa, auratayya ya taka muhimmiyar rawa wajen kawar da gaba da wutar
rikici tsakanin Fulani da Kabawa. Sarkin Musulmi Ahmadu ɗan
Atiku ya yi ƙoƙarin kawo ƙarshen
gabar da ke tsakanin Sulluɓawa da daular Usmaniyya ta
hanyar auratayya, inda ya ba da auren wata ƙanwarsa
ga Arɗon
Sulluɓawa
Muhammadu Inna. A sakamakon wannan aure ne ɗan
da suka haifa ya zama Arɗo. Shi ma Sarkin Gobir ɗan
Halima ya ba Sarkin Musulmi Ahmadu ƙanwarsa
aure, don dai a sami sulhun zaman lafiya mai ɗorewa.[24]
9.5
TSAGAITA WUTAR YAƙI
A duk lokacin da ake son
kawo ƙarshen wata fitina ko yaƙi tsakanin ɓangarori
biyu, dole a tsagaita wuta a daina kai wa juna farmaki. Yin haka zai sa a sami
damar zaunawa teburin sulhu domin magance matsalar. Bunza 2015 ya bayyana cewa,
tsagaita wuta hanya ce ta kawo ƙarshen
yaƙi tsakanin masu husuma, domin daular
Usmaniyya ta aminta da tsagaita wuta tsakaninta da daular Kabi a zamanin Sarkin
Kabi Toga 1860-1863 shekaru biyu bayan da Sarki Toga ya hau kujerar mulkin
Kabi. Saboda haka, idan ana son ganin bayan matsalar Boko Haram dole a kafa
yarjejeniyar tsagaita ruwan wuta tskanin ‘yan ƙungiyar
da gwamnati, kowa ya mayar da wuƙarsa
a kube, a zauna a yi sulhu ba na cin amana da yaudarar juna ba. Kada ana cikin
sulhu ana yaƙi. Kada a kira sulhu
a kashe ko a kama abokan sulhu. Kada abokan sulhu su zo da yaƙi a duƙunce
matuƙar ana son cin gajiyar sulhun.
9.6
SAMAR DA NAGARTACCEN TSARO
A duk lokacin da aka hangi
zaman lafiya a gudane, yana neman ceto ko mafaka, to rashin tsaro ya koro shi.[25] Tsaro
shi ne tabbatar da abubuwan da ke wanzar da zaman lafiya, a dinga kiwonsu, da
kula da su, da ba su muhimmanci a hukumance da ɗaiɗaice.
Asalin kalmar tsaro daga “tsari” ne. Abin da aka tsare yana ɗaukar
ma’ana biyu. Na farko a hana masa motsi da zuwa ko’ina; Na biyu a kiyaye shi da
hana duk wani abin da ake ƙyama
kar ya same shi. Idan ana buƙatar
kawo ƙarshen ƙungiyar
Boko Haram, tilas a yi tankaɗe da rairaya ga jami’an
tsaron ƙasar nan, a zubar da ɓara-gurbi,
sannan a ƙara yawansu, a ba su
makamai isassu. Waɗannan matakai na amfani da
isassun barade, da isassun kayan artabu, da baza barade masu kula da muhimman
wurare, da kuma amfani da siddabaru, da su ne daular Kabi ta yi amfani domin
samar da tsaro a zamanin yaƙe-yaƙe don kare kanta daga maƙiya.[26] Saboda
haka, ya kamata a jarraba dabarun Kabawa da ma na sauran ƙasashen Hausa domin shawo kan matsalar
Boko Haram.
9.7
MAYAR DA ‘’YAYAN ƘUNGIYAR
A MUHALLINSU
A cikin shekarar 2016 ne aka
sami wasu ‘ya’yan ƙungiyar
Boko Haram da suka aje makamai, suka ba da kai bori ya hau. Idan so samu ne sai
a yi musu afuwa a yafe musu tun da sun yi nadama, kamar dai yadda aka yi wa
tsagerun Neja Delta a can baya. Idan aka samu haka, sai a kwashe su a mayar da
su garuruwansu a kyautata shi, a saki tubabbinsu, a ba su ayyukan yi domin sake
sabon rayuwa mai tsafta. Ba mamaki wannan gatanci ya jawo hankalin sauran da ba
su tuba ba, su ma su jingine nasu makaman su bi sahun ‘yan’uwansu.
10.0
SAKAMAKON BINCIKE
Wannan bincike ya gano cewa,
Boko Haram ba ƙungiya ce ta addinin
Musulunci ba kamar yadda take iƙirari,
ko yadda wasu ke kallon ta. Wannan ya tabbata idan aka yi la’akari da yadda
suke kai wa Musulmi hari a Masallatai da wuraren ibada. Haka ma an sha kama
‘ya’yan ƙungiyar waɗanda
masu bincike suka tabbatar da Kirista ne ba Musulmi ba. Binciken ya kuma gano
cewa, rashin ba sulhu muhimmancin da ya kamata ya sa har yau aka kasa kawo ƙarshen rikicin, domin a shekarar 2012 an
kafa kwamitin sasantawa a ɓangaren gwamnati da suka haɗa da
shugaban ƙasan yanzu wato
Muhammadu Buhari da Shatima Ali Monguno da Sanata Bukar Abba Ibrahim da Jakada
Gaji Galtimari da Barista A’isha Alƙali
Wakili da mijinta Alƙali
wakili. Ɓangaren ‘yan Boko Haram akwai
Abdul’azeez da Abu Abbas da sheikh Ibrahim Yusuf da sheikh Sani Kontagora da
kuma Mamman Nur wanda ake zargi da dasa bam a ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Abuja, amma aka kasa
aiwatar da komai.
Binciken ya fahimci azabar
da jami’an tsaro na sojoji da ‘yansanda da na farin kaya suke gwada wa kamammu
waɗanda
ake tuhuma (‘yan Boko Haram) shi ke hana wa abokan arangama amincewa da sulhu.
Shi ke sa su fito su yi ƙunar
baƙin wake a mutu har liman. Shi ke sa
‘yan’uwansu na jini su tausaya musu har su shiga tunanin shigar musu komi taka
zama ta zama. Shi ke sa su ɗaura wa kansu bam ko su ɗaura
wa ‘ya’yansu domin sun san in aka kama su ba adalci da tausayawa za a yi ba.
Shi ke haifar da bi-ta-da-ƙulli
ko wakilin tsaro ya yi ritaya ba za su yafe masa ba. Shi ke sa su kama yaranmu
su yi garkuwa da su. Shi ke sa ba su da ranar ajiye makamai har sai an ƙare su ko sun ƙare mu. Kamata ya yi idan an kama su a
hannunta su ga shari’a don bincike da hukunta su daidai da laifin da suka
aikata. Har wa yau, binciken ya tabbatar da cewa, ƙungiyar Boko Haram ƙungiya ce kawai ta ta’addanci kamar
yadda binciken ya kalato ra’ayoyin masana daban-daban. Ba shakka ƙungiyar na da ɗaurin
gindin wasu mutane idan aka yi la’akari da yadda suke samun makamai da abinci
da sauran abubuwan buƙatan
rayuwa, shi ya sa har yanzu ba su lafa ba. A ƙarshe,
binciken ya fito da tunanin Bahaushe na warware husuma domin a jarraba amfani
da su ga rikicin Boko Haram, domin Hausawa sun ce: “Magani sai da gwaji”.
11.0
NAƊEWA
Duk wata hanya ko dabarar ci
gaban rayuwar ɗan Adam sharaɗinta
samun zaman lafiya. Sasantawa babban al’amari ne da ya kamata mutane su ɗauka
a matsayin makamin warware kowane irin rikici. Rashin ba sulhu muhimmanci ga
kowace irin matsala babban kuskure ne ga mahukunta da talakawa. Rikicin Boko
Haram matsala ce da ya kamata gwamnati ta yi amfanin da makamin sasantawa domin
kawo ƙarshensa. Lokuta da dama ƙungiyar kan ba da ƙofar zaunawa teburin sasantawa, sai dai
ba a ɗauki
lamarin da muhimmanci ba. A watan Agustan shekarar 2016 ne ƙungiyar ta Boko Haram ta sake buɗe
kafar sasantawa ta musayar fursunoni na ‘ya’yan ƙungiyarsu
da ke hannun gwamnatin Nijeriya da ‘yan matan Chibok da ke hannunsu tun a
shekarar 2014. A kwanakin baya ne kakakin shugaban Nijeriya Garba Shehu ya ce, ƙungiyarta ce shirye take ta tattauna da
gwamnati idan tana so don sake sako ‘yan matan na Cibok 83. To sai dai ministan
yaɗa
labarai Lai Mohammed ya musanta labarin da ke cewa musayar fursunoni gwamnati
ta yi da Boko Haram. Ya ce, Boko Haram sun sako ‘yan matan ne don nuna wa
gwamnati cewa shirye suke su tattauna da ita don sako sauran ‘yan matan da ke
hannunsu. Wannan ya nuna idan aka zauna teburin sulhu za a iya warware rikicin.
MANAZARTA
Abba, M.T. (1982). The Maitatsine and War in Kano. Kano:
Salma-Yaseen Publishers.
Adamu, H. (1973). The North and Nigerian Unity: Some
Reflections on the Political and Social Problems of Northern Nigeria.
Zaria: Gaskiya Corporation.
Adamu, M. (1978). The Hausa Factor in West African History.
Zaria: Oɗford
Press.
Aminu, N. (2016). Tanadin
Tsaro a Tunanin Kabawa: Gudummawa ga Nijeriyarmu ta Yau”
Balarabe, I. (2013).Third
Party Mediation in Conflict Management and Resolution” in Kanta
Bunza, A.M. (2015). Zaman
Lafiya da Tsaro a Daular Musulunci ta Sakkwato: Abin Koyi ga Shugabannin
Zamaninmu”. Takardar da aka gabatar a taron yini ɗaya
da Centre for Intellectual Serɓices
on Sokoto Caliphate ta shirya na faɗakarwa
a kan muhimmancin tsaro da zaman lafiya.
Bunza, A.M. (2013). Makamin
Demokoraɗiyya
a Falsafar Al’ada Takardar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa na farko a kan Harshe, Adabi da
Al’adun Hausawa a Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
C. N. H. N. (2006). Ƙamusun Hausa, Kano: Jami’ar Bayero.
Gulbi, A.S. (2016). Sulhu a
Gargajiyance: Darasi Daga Daular Sakkwato da Kabi” Takardar da aka gabatar a taron
ƙara wa juna sani na ƙasa da Tsangayar Fasaha da Nazarin
Addinin Musulunci, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo,
Sakkwato.
Last, M. (2009) Daular Sakkwato. Fassarar A.M. Bunza, S.S.
Ibrahim, da B.B. Usman.
Onu, G. (2009). The Methods
of Conflict Resolution and Transformation” in Peace Studies
Onuoha, J. (2009).
Negotiation and Mediation Process” in Peace
Studies and Conflict Resolution in Nigeria: A Reader. Ibadan: Spectrum
Books Limited.
Oɗford
Adɓanced
Leaners’ Dictionary, Seɓenth Edition. Resolution in Nigeria: A Reader. Ibadan:
Spectrum Books Limited.
Ya’u, Y.Z. (2016)
Understanding Community Resileince in the Conteɗt of
Boko Haram Insurgency in Nigeria. Kano: Centre for Information Technology and
Deɓelopment.
Jaridar “Daily Trust” ta
ranar 9 ga watan Janairun shekarar 2013.
Jaridar “The Sun” ta ranar 6
ga watan Janairun shekarar 2013.
Jaridar “Aminiya” ta ranar 7
ga watan Maris na shekarar 2013.
Jaridar “Aminiya” ta ranar
28 ga watan Agustan shekarar 2013.
https:/en.m.wikipedia.org
[1] Daga shafin Intanet na
www.naijajist.com
[2] Tattaunawar da gidan rediyon
BBC Ingilishi ya yi da shugaban ƙungiyar
Boko Haram na farko, Muhammadu Yusuf kafin a kashe shi a shekarar 2009 a watan
Agustan shekarar 2008, daga shafin www.nairaland.com
[3]
Domin ƙarin bayani, a dubi Jaridar
Aminiya ta ranar 7 ga watan Maris ɗin shekarar 2013, shafi na 2.
[4]
Bayanin kafar yaɗa labarai na BBC Hausa a kan faifan bidiyon da ƙungiyar Boko Haram ta fitar
na tsawon minti biyar a ranar 7 ga watan Fabrairun shekarar 2014.
[5] Rahoton da kafar yaɗa labarai na BBC Hausa ta bayyana a kan ci gaba
da rikicin Boko Haram a ranar 7 ga watan Janairun shekarar 2015.
[6]
Hirar da Jaridar
Aminiya ta yi da Naja’atu Muhammad a kan rikice-rikicen da ke faruwa a Arewacin
Nijeriya musamman rikicin Boko Haram, a ranar 26 ga watan Mayun shekarar 2013,
shafi na 18.
[7] Hirar da Jaridar Aminiya ta
yi da Sheikh Umar Farouk a ranar 28 ga Agustan shekarar 2013, shafi na 32.
[8]
https:/en.m.wikipedia.org
[9]
Ƙamusun Hausa, wallafar
Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano, shafi na 393.
[10]
Oɗford Adɓanced Leaners’ Dictionary, Seɓenth Edition, shafi na 1244.
[11]Balarabe, I. 2013 “Third
party mediation in conflict management and resolution” a cikin Kanta Journal of General Studies Maiden
Edition.
[12]
www.businessdictionary.com
[13] Gulbi, A.S. 2016, “Sulhu a
Gargajiyance: Darasi daga Daular Sakkwato da Kabi” Takardar da aka gabatar a
taron ƙara wa
juna sani na ƙasa da
Tsangayar Fasaha da Nazarin Addinin Musulunci ta Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato ta shirya.
[14] Aliyu Muhammad Bunza 2013,
“Makamin Dimokuraɗiyya a Falsafar Al’ada”
Takardar da aka gabatar a taron ƙara
wa juna sani na ƙasa na
farko a kan Harshe, Adabi da Al’adun Hausawa da Cibiyar Nazarin Harsunan
Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano ta shirya.
[15] Onu, G. 2009:89, “The Methods
of Conflict Resolution and Transformation” in Peace Studies and Conflict Resolution in Nigeria: A Reader. Edited
by Miriam Ikejiani-Clark. Ibadan: Spectrum Books Limited.
[16]
Last, M. 2009:179. Daular Sakkwato. Fassarar A.M. Bunza da
wasu, wallafar Hukumar Fassara, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
[17]
Dubi lamba ta 9 na
wannan takarda, shafi na 180.
[18]
Dubi lamba ta 3 na
wannan takarda, shafi na 403.
[19]
Dubi lamba ta 2 na
wannan takarda, shafi na 400.
[20] Onuoha, J. 2009,
“Negotiation and Mediation Process” in Peace
Studies and Conflict Reoslution in Nigeria: A Reader. University of Nigeria
Nssuka. A cikin Abdullahi Sarkin Gulbi 2016.
[21]
Bunza, A.M. 2015, “Zaman Lafiya da Tsaro a Daular Musulunci ta Sakkwato: Abin
Koyi ga Shugabannin Zamaninmu”. Takardar da aka gabatar a taron yini ɗaya
da Centre for Intellectual Serɓices
on Sokoto Caliphate ta shirya na faɗakarwa
a kan muhimmancin tsaro da zaman lafiya.
[22]
Dubi lamba ta 21 na
wannan takarda don ƙarin
bayani.
[23]
Dubi lamba ta 9 na
wannan takarda don ƙarin
bayani.
[24]
Dubi lamba ta 6 na
wannan takarda don ƙarin
bayani.
[25]
Dubi lamba ta 3 na
wannan takarda don ƙarin
bayani.
[26] Aminu, N. 2016. “Tanadin
Tsaro a Tunanin Kabawa: Gudummawa ga Nijeriyarmu ta Yau”. Takardar da aka
gabatar a taron ƙara wa
juna sani na ƙasa
karo na farko da Tsangayar Fasaha da Nazarin Addinin Musulunci ta Jami’ar
Usamnu Ɗanfodiyo,
Sakkwato ta shirya.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.