𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Malam, rikici a masallacinmu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa: Yau a sauke wannan limamin, gobe a kawo wani, jibi shi ma a cire shi. Sannan gata a soke wannan kwamiti, citta a naɗa sabo, bayan kwana biyu shi ma a kawar da shi, a sake naɗa sabo! Wai meye mafita ne a irin wannan halin?
RIKICI A MASALLACINMU YA ƘI CI, YA ƘI CINYEWA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah.
Kafin mu ji mafita a cikin
wannan ya kamata mu gano tushen matsalar: A mafi yawan lokuta kwamitoci suna
taimakawa wurin haifar da matsalolin da ke ruguza shugabanci da kyakkyawan
jagoranci a masallatai.
Galibi ’yan kwamiti a
masallatan Ahlus-Sunnah ba malamai ko ɗaliban
ilimi ba ne, waɗansu ma ba Ahlus-Sunnah ba
ne. Sun zama ’yan kwamiti ne kawai lura da irin matsayin su na alhazan birni ko
manyan ’yan kasuwa ko tsofaffin ma’aikatan gwamnati. Ana tsammanin su masu
kishin addini ne domin halartan sallolin jam’i, ko zama a wurin darussan da
suke yi a masallacin wani lokaci.
Daga cikin abubuwan da sukan
haifar da matsaloli a masallatan Ahlus-Sunnah a fahimtata akwai:
1. Wurin zaɓen
limamin masallacin ba safai akan kula da ɗauko
masanin Alƙur’ani da Sunnah a
gaskiya ba. Galibi akan fi damuwa da wanda ake so ne, kamar ɗan
dangi ko wanda zai yi biyayya ga ’yan kwamiti, wanda kuma kwamitin zai iya juya
shi!
2. Akan bi wasu matakan da
ba muhimmai ba a Shari’a a wurin tantance limaman! A kan kayar da wanda aka so
domin wani abin da ba shikenan ba, kamar wanda ya kasa bayyana kansa sosai da
Larabci, ko ya kasa isowa wurin tantancewar da wuri, ko ya kasa iya amsa wata
tambaya ta Nahawu, ko kuma wanda ya kasa iya warware wata mas’ala ta Fiƙhu kamar a Babin Gado!!
3. Abubuwan da ake karantar
da jama’a a masallaci sau tari ba sa yin daɗi ga
shugabannin siyasa da sarakunan gargajiya da su kansu ’yan kwamitin ma a wani
lokaci. Don haka akan yi ƙoƙarin neman mai karatun ya sassauta, in
ba haka ba kuma a ɗauki matakan tuɓe
shi tare da limamin da ke goya masa baya.
4. Karatu mai rai da ake yi
a masallatan Ahlus-Sunnah ba ya yiwuwa ya bi ra’ayin kowa, sai dai kowa ya bi
shi. Ƙoƙarin
neman matsakaiciyar hanyar bi a nan shi ke janyo a fara takun-saƙa a tsakanin mai karatun da mabiyansa a
gefe ɗaya,
da kuma ’yan kwamiti ko da liman ma a ɗaya
gefen.
5. Yawancin manya a
masallaci ba su samun halartan darussa akai-akai, don haka duk lokacin da aka
so sanya wani abin da aka karanta a aiki sai su ƙi
yarda, suna masu kafa hujja da cewa ba su san wannan abin ba! Har kuma wani
lokaci su riƙa zargin mai karatun
da zuwa da baƙin littaffan da ba a
san su ba!!
6. Yawancin malamai ko ɗaliban
ilimi masu karantarwa a masallatan Ahlus-Sunnah matasa ne masu zafin-kai da ɗimin
ƙirji, kuma masu sha’awar bin Sunnah sak! Saɓanin
yawanci tsofaffi da dattawa masu neman a lallaɓa.
Wannan shi ke kai matasan ga zargin manya da neman yi wa nassi karan-tsaye!
7. Akan samu zargi da gulma
da ƙulla makirci da cin-dunduniyar juna a
tsakanin malamai domin neman kuɗi ko gindin-zama ko matsayi
da sauransu. Wannan kan janyo sa-in-sa a tsakanin manya, wanda hakan kan kai ga
mummunan rikici, wani lokaci ma har da zubar da jini!
8. Rashin wata ƙwaƙƙwarar
sana’a da liman ko malami ke
dogara a kanta kan janyo su riƙa
kallon ɗan
abin sadaka da ake tarawa a masallaci. Daga baya idan sun samu matsala da wani ɗan
kwamiti sai a fara zargin cin kuɗi
tare da ƙoƙarin
tuɓe
liman ko malami ko ’yan kwamitin da suka mara musu!
9. Bambancin ra’ayin siyasa
ko dai wani abu makamancin haka a tsakanin ’yan kwamiti, wanda kuma kan gangara
har zuwa ga malamai da limamin masallacin, kan haifar da mummunar matsala, wani
lokaci ma har ga sauran masu sallah a cikin masallacin.
10. A waɗansu
lokuta rikicin masallacin Ahlus-Sunnah kan yi ƙamari
har ya kai ga zuwa ofishin ’yan
sanda ko fadojin sarakuna, waɗanda yawancinsu ke kallon
malamai da limaman irin waɗannan masallatan a matsayin
tsageru ’yan ta-da-zaune-tsaye. Shiyasa galibi zuwa wurinsu ba ya samar da
mafita ta-dindindin.
MAFITA:
Domin samun mafita daga irin
waɗannan
matsalolin a fahimtata sai a ɗauki waɗannan
matakan, in shaa’al Laah:
1.A cire son zuciya ko
ra’ayi a wurin zaɓen limamin masallaci. A bi
abin da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce kawai:
« يَؤُمُّ الْقَوْمَ أَقْرَؤُهُمْ لِكِتَابِ اللَّهِ ، فَإِنْ كَانُوا فِى الْقِرَاءَةِ سَوَاءً فَأَعْلَمُهُمْ بِالسُّنَّةِ ، فَإِنْ كَانُوا فِى السُّنَّةِ سَوَاءً فَأَقْدَمُهُمْ هِجْرَةً ، فَإِنْ كَانُوا فِى الْهِجْرَةِ سَوَاءً فَأَقْدَمُهُمْ سِلْمًا »
Wanda zai yi wa mutane
limanci shi ne wanda ya fi su karatun Alƙur’ani.
Idan kuma sun zama daidai a karatun, sai wanda ya fi su sanin Sunnah. Idan kuma
sun zama daidai a Sunnah, sai wanda ya riga su yin hijira. Idan kuma sun yi
daidai a wurin hijira, sai wanda ya riga musulunta ko wanda ya fi girma a
shekaru. (Sahih Muslim: 673)
2.A bi matakan adalci wurin
bincike da gano zurfin hardar Alƙur’ani
na ’yan takara. A saurari kyawun karatun kowannensu ko akasinsa a kan ƙa’idojin
Tajweed, da kuma yadda siffar tsarki da sallarsa ta yi kusa ko nesa da ta
Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam). Sai kuma a binciki wani abu na
ilimin Fiƙhun sallah daga
kowannensu.
3. Limamin da aka zaɓe
shi shugaba a cikin al’amarin sallah a amince kuma ya zama shi ne shugaba a
cikin dukkan al’amuran da suka shafi shugabanci da gudanar da masallacin. Bai
kamata a ɗora kwamiti ko wani daga ’yan kwamiti a
sama da liman ba.
4. Sauran ’yan kwamiti su
zama kamar ma taimaka ko mashawarta ne kawai ga Liman. Amma ba waɗanda
suke da ƙarfin zama su tsige shi ba, domin kawai
ya yi wani abin da ya kauce wa wata ƙa’idar da wai suka shimfiɗa
kafin a naɗa shi, wataƙila ma ba da saninsa ba!
5. Liman da ’yan kwamiti su
zama suna da son gudanar masallacin a kan Sunnah, kuma ya zama kowannensu yana
da sana’ar da take riƙe
shi da iyalinsa, wadda kuma ba za ta hana shi sauke nauyin da ke kansa ba.
Domin samun kyakkyawan
sakamako, ana iya sanya wa limami ko malami hanun-jari a cikin wata harkar
kasuwanci ta halal domin kare mutuncinsa daga roƙo ko
bara ko sa-ido a kan kuɗaɗen
masallaci.
6. Liman ya zaɓo
ladani ko ladanai da malaman da ya amince da su da sauran ma’aikata domin su
taimaka masa wurin gudanar da harkokin masallaci, kamar sallah da karantarwa a
cikin masallaci. Ana iya taimaka musu da ɗan
kuɗin
sanya mai a cikin abin hawa lokaci-bayan-lokaci.
7. Liman da mashawartansa su
zama masu yin aiki da duk wata aya ko wani hadisin da masu karatu suka janyo,
musamman waɗanda suka shafi masallacin da
jagorancinsa da gudanar da shi. Wannan shi zai samar musu da alkhairi da
albarka da haɗin-kai a cikin masallacinsu, in shaa’al
Laah.
8. Ana iya ɗaukar
matakan tuɓe liman ne kawai idan ya samu larurar da
ta wajabta haka, kamar in ya haukace ko ya samu rashin lafiyar da ya hana shi
iya gudanar da aikinsa na limanci ko karantarwa, ko kuma idan aka tabbatar ya
aikata wani mummunan aikin fasiƙanci
da ya wajabta hakan. Amma a yi shi a cikin mutuntawa da girmamawa, ba tare da
shahartawa a cikin jama’a
ba.
9. Liman da mashawartansa su
tsara yadda za su riƙa
tara taimako da gudunmawa daga masu hali daga cikin masallata ko ɗaliban
da ake yi musu karatu ko darussa a masallaci. Daga baya a yi amfani da abin da
aka tara wurin gyara masallacin da masallata da ɗalibai
masu halartan masallacin.
10. Liman ya tabbatar ana yi
wa jama’ar masallaci bayanin irin kuɗaɗen
da ake tarawa da yadda ake kashe su dalla-dalla, domin kowa ya san inda kuɗaɗen
da ake bayarwa suke tafiya. Babu laifi a ɓoye
sunaye da abin da kowane ma’aikaci ke ɗauka,
amma a adana bayanansa a ɓoye a cikin rajista.
Ina ganin bakin haka ya isa,
in shaa’al Laah.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.