𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum. Limamin masallacin da yake zuwa sallah ba ya natsuwa a cikin sallar, shi kuma gidansa yana da nisa daga masallacin, kuma yana fama da matsalar ƙafa. To wai ko waɗannan matsalolin sun isa hujja a kan ya riƙa yin sallah a gida?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Ramatul Laah:
A gaskiya saboda Allaah! Ba
su isa ba, saboda dalilai kamar haka:
1. Sallah a cikin jama’a
wajiba ce a kan kowane musulmi namiji baligi mai lafiya, wanda kuma ya ji kiran
sallar. Wannan ita ce mazhabar Hanaabilah kuma ita ce daidai, in shaa’al Laah.
Saɓanin
Hanafiyyah da Maalikiyyah da suke ganin ita Sunnah ce mu’akkadah kawai, ko kuma
Shaafi’iyyah da suke ganin ita farali ce ta kifaayah kaɗai,
ko kuma Zaahiriyyah da suka zaƙe
har suka ɗauke ta a matsayin sharaɗi ga
ingancin sallar!
2. Sallar Tsoro da Allaah ya
wajabta wa musulmin da suka fita jihadi domin kare addini cewa su yi ta a cikin
jama’a, duk kuwa da tsananin da suke ciki:
وَإِذَا كُنتَ فِيهِمْ فَأَقَمْتَ لَهُمُ الصَّلَاةَ فَلْتَقُمْ طَائِفَةٌ مِّنْهُم مَّعَكَ وَلْيَأْخُذُوا أَسْلِحَتَهُمْ فَإِذَا سَجَدُوا فَلْيَكُونُوا مِن وَرَائِكُمْ وَلْتَأْتِ طَائِفَةٌ أُخْرَىٰ لَمْ يُصَلُّوا فَلْيُصَلُّوا مَعَكَ وَلْيَأْخُذُوا حِذْرَهُمْ وَأَسْلِحَتَهُمْ وَدَّ الَّذِينَ كَفَرُوا لَوْ تَغْفُلُونَ عَنْ أَسْلِحَتِكُمْ وَأَمْتِعَتِكُمْ فَيَمِيلُونَ عَلَيْكُم مَّيْلَةً وَاحِدَةً وَلَا جُنَاحَ عَلَيْكُمْ إِن كَانَ بِكُمْ أَذًى مِّن مَّطَرٍ أَوْ كُنتُم مَّرْضَىٰ أَن تَضَعُوا أَسْلِحَتَكُمْ وَخُذُوا حِذْرَكُمْ إِنَّ اللَّهَ أَعَدَّ لِلْكَافِرِينَ عَذَابًا مُّهِينًا
Kuma idan ka kasance a
cikinsu, sai ka tsayar musu da salla, to, wata ƙungiya
daga gare su ta tsaya tare
da kai, kuma sai su riƙe
makamansu. Sa'an nan idan sun yi
salla, to, sai su kasance daga bayanku.
Kuma wata ƙungiya ta dabam (ta)
waɗanda
ba su yi sallar ba, ta zo, sa'an nan su yi sallar tare da kai. Kuma su riƙi shirinsu da makamansu. Waɗanda
suka kafirta sun yi gũrin da dai kuna shagala daga makamanku da kayanku domin
su karkata a kanku, karkata guda. Kuma babu laifi, a kanku idan wata cũta daga
ruwan sama ta kasance a gare ku, ko kuwa kun kasance masu jinya ga ku ajiye makamanku
kuma dai ku riƙi shirinku. Lalle ne,
Allah Ya yi tattali, ga kafirai, azaba mai walakantarwa. (Surah
An-Nisaa’: 102).
Wannan shi ne babban dalili
a kan wajibcin jam’in a kan duk wanda yake zaune a cikin gari lafiya lau.
Sannan idan da sallar jam’in Sunnah ce kawai da bai farlanta wa mujahidai da
suke cikin halin firgici da rashin natsuwa ba. Kuma in da farilla ta kifaya ce
kaɗai
da bai wajabta ta a kan jama’a ta biyu a cikin sallar tsoron ba.
3. Hadisin makahon da ya
nemi Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya sama masa sassaucin yin
sallah a gida. (Sahih Muslim: 653).
Idan dai har makaho mara ɗan-jagora
zai rasa samun sassaucin yin sallah a gida daga Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa
Alihi Wa Sallam), to ina kuma ga mai matsala a ƙafa
kawai a irin waɗannan zamunnan na ƙarshen zamani?!
4. Babu ranar da Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya taɓa
zama bai yi sallah a cikin jama’a ba, har a lokacin rashin lafiyarsa na ajali!
(Sahih Al-Bukhaariy: 687).
Shiyasa manyan malamai daga
cikin Sahabbai irinsu Ibn Mas’ud (Radiyal Laahu Anhu) yake cewa:
مَنْ سَرَّهُ أَنْ يَلْقَى اللَّهَ غَدًا مُسْلِمًا فَلْيُحَافِظْ عَلَى هَؤُلاَءِ الصَّلَوَاتِ حَيْثُ يُنَادَى بِهِنَّ فَإِنَّ اللَّهَ شَرَعَ لِنَبِيِّكُمْ -صلى الله عليه وسلم- سُنَنَ الْهُدَى وَإِنَّهُنَّ مِنْ سُنَنِ الْهُدَى وَلَوْ أَنَّكُمْ صَلَّيْتُمْ فِى بُيُوتِكُمْ كَمَا يُصَلِّى هَذَا الْمُتَخَلِّفُ فِى بَيْتِهِ لَتَرَكْتُمْ سُنَّةَ نَبِيِّكُمْ وَلَوْ تَرَكْتُمْ سُنَّةَ نَبِيِّكُمْ لَضَلَلْتُمْ وَمَا مِنْ رَجُلٍ يَتَطَهَّرُ فَيُحْسِنُ الطُّهُورَ ثُمَّ يَعْمِدُ إِلَى مَسْجِدٍ مِنْ هَذِهِ الْمَسَاجِدِ إِلاَّ كَتَبَ اللَّهُ لَهُ بِكُلِّ خَطْوَةٍ يَخْطُوهَا حَسَنَةً وَيَرْفَعُهُ بِهَا دَرَجَةً وَيَحُطُّ عَنْهُ بِهَا سَيِّئَةً وَلَقَدْ رَأَيْتُنَا وَمَا يَتَخَلَّفُ عَنْهَا إِلاَّ مُنَافِقٌ مَعْلُومُ النِّفَاقِ وَلَقَدْ كَانَ الرَّجُلُ يُؤْتَى بِهِ يُهَادَى بَيْنَ الرَّجُلَيْنِ حَتَّى يُقَامَ فِى الصَّفِّ.
Duk wanda yake sha’awar ya
haɗu da
Allaah gobe a halin yana musulmi, to ya kiyaye a kan waɗannan
sallolin a duk inda aka yi kiran sallarsu. Domin Allaah Ta’aala ya shar’anta wa
Annabinku (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) Sunnonin Shiriya, kuma su ɗin
suna daga cikin Sunnonin Shiriya. To idan da kun tsaya yin sallah a cikin
gidajenku kamar yadda wannan da yake ƙin
zuwa jam’in yake yin sallar a cikin
gidansa, to da kuwa kun bar Sunnar Annabinku. Idan kuma da kun bar Sunnar
Annabinku, to da kuwa kun ɓace. Babu wanda zai yi
tsarki, kuma ya kyautata tsarkin sannan ya taka da nufin zuwa ɗaya
daga cikin waɗannan masallatan, face Allaah ya rubuta
masa lada da kowace takawa da yake yi, ya ɗaga
masa daraja da ita, kuma ya kankare masasa laifi da ita. Haƙiƙa!
Na gan mu (a zamanin Sahabbai), babu mai ƙin
zuwa sallar jam’i
sai dai munafukin da kowa ya san munafuncinsa. Kuma haƙiƙa!
Ya kasance ana rungumo mutum (mara lafiya) a tsakanin mazaje biyu, har sai an
tsayar da shi a cikin sahu. (Sahih Muslim: 654).
A cikin riwaya sahihiya da
ke cikin Sunan Abi-Daawud: 550, ya ce:
وَلَوْ تَرَكْتُمْ سُنَّةَ نَبِيِّكُمْ -صلى الله عليه وسلم- لَكَفَرْتُمْ
Idan kuma da kun bar Sunnar
Annabinku (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) to da kuwa kun kafirce!
Wannan kuwa shi ya fi
tsananin wurin razanarwa.
5. Rashin natsuwar liman shi
ta shafa, saboda hadisin Abu-Hurairah wanda Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa
Alihi Wa Sallam) ya faɗa a cikinsa cewa:
« يُصَلُّونَ لَكُمْ ، فَإِنْ أَصَابُوا فَلَكُمْ ، وَإِنْ أَخْطَئُوا فَلَكُمْ وَعَلَيْهِمْ »
Limamai suna yi muku sallah,
to idan suka dace da daidai kun haye. Idan kuwa suka kuskure wa daidai, to kun
haye su kuma sun nutse. (Sahih Al-Bukhaariy: 694).
A ƙarshe dai abubuwan da malamai suka
ambaci cewa yana iya hana mutum zuwa jam’in
sallah a masallaci sun haɗa da:
• Rashin jin kiran Sallah
saboda nisan inda ya ke daga masallaci.
• Idan ladan ya ce: ‘Ku yi
sallah a gida’, saboda sanyi ko ruwan sama.
• Larura mai tsanani, kamar
ta rashin lafiya ko rashin kyawun hanya domin ruwa.
• Samuwar abincin da yake
sha’awarsa.
• Matsuwa ta buƙatar kewayawa. (Mausuu’atul Fiƙhiyyah: 2/217-220).
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.