Citation: Abubakar Barde Kukuri & Adamu Ago Saleh (2017). Nazarin Salon Hoton Gurbi Da Aiwatarwa A Labarin Baƙin Kishina Muhammad Lawan Barista. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 5. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
NAZARIN
SALON HOTON GURBI DA AIWATARWA A LABARIN BAƘIN KISHINA
MUHAMMAD LAWAN BARISTA
Daga
Abubakar
Barde Kukuri
Da
Adamu
Ago Saleh
ABSTRACT
The aim of this paper is to
examine
how the author of Baƙin
Kishi employs the stylistic devices
of scene description and performance and how the characters were used to achieve
the aim of the book. The paper begins with brief explanation
on the theme of the book, thereafter; the theoretical framework (Mukhtar, 2004)
was applied. The paper conludes with the analsysis on the occurances of the two
stylistic devices where it was
found that, the writer uses scene description and action simultaneously in some
instances while in other places seperates them.
TSAKURE
Manufar wannan takarda ce ta
nazarci yadda marubucin labarin
Baƙin Kishi
ya yi amfani da salo da dabarar ƙulla
zance ta hanyar zayyana hoton gurbi a cikin labarin da kuma yadda ake amfani da
taurari su aiwatar da ita wajen isar da saƙon labarin. Takardar ta fara
da yin taƙaitaccen
tsokaci kan labarin Baƙin
Kishi, sannan ta waiwaici ra’in Dabarun Bayar da Labarin na Mukhar (2004). An
fito da hoton gurbi da kuma aiwatarwa da ke cikin labarin, kana aka ƙalailaice su inda aka gano
cewa, marubucin labarin kan kawo hoton gurbi da aiwatarwa a lokaci guda, a wusu
lokuta kuma yakan raba su.
1.0
GABATARWA
Mukhtar (2004: 34-43) ya
bayyana hanyoyin ruwaita labari a cikin littattafan ƙagaggun labarai na Hausa. Kamar yadda ya
nuna, marubuci kan iya bayar da labari kai tsaye ko kuma ya yi amfani da wasu
daga cikin taurarin labarin, ko ma ya sami wani daga bayan fage. A irin bayar
da waɗannan
labarai ne, ake samun bayyanar wuraren da wasu abubuwa suke aukowa; ko ma
bayyana yanayinwuri, wanda yin haka yana taimakawa wajen zaburar da mai karatu
jin shauƙi da annashuwa yayin karantawa.Wannan
takarda za a nazarci yadda marubucin labarin Baƙin Kishi ya
yi amfani da hoton gurbi da aiwatarwa ya isar da saƙon littafinsa. Za a fara da yin bayani a
kan hoton gurbi da aiwatarwa, sannan taƙaitaccen
sharhi kan labarin, daga ƙarshe
a zaƙulowaɗannan
dabaru a cikin labarin.
1.1
HOTON GURBI
Mukhtar
(2001:152)ya bayyana Hoton Gurbi da cewa:
“Hoton
gurbi na nufin wuri da wani abu ya faru ko zai faru cikin labari. Misali a
gindin wata bishiya marubucin ya yi ta kawo bayanin hoton yadda gindin bishiyar
yake ko kuma bayanin hoton ƙofar
wani gida a cikin labari ko kuma cikin gidan da dai sauransu”.
Shi
kuwa Yahaya (2004:84) cewa ya yi:
“Hoton
gurbi kuwa yana bayyana taswirar wurin da wani abu ya faru ko zi faru a cikin
littattafan ƙagaggun labarai na Hausa”
Wannan
ya nuna cewa hoton gurbi kamar yadda sunan ya nuna, ƙoƙarin nuna shatice ta wani wuri da wani abu ya faru
ko kuma ake tsammanin faruwarsa. Haka zalika shi ma hoton gurbi a cikin
littattafan ƙagaggun labarai yana nufin dukkan wurare da aka
bayyana faruwa ko kuma tsammanin faruwar wani abu a wani kafaffen wuri.
1.2 MA’ANAR AIWATARWA
Kamar
dai hoton gurbi, aiwatarwa ma Mukhtar(2001:152) ya bayyana fahimtarsa da cewa:
“Ita
ce ainihin yadda tauraro ya aikata wani abu, misali inda Ganɗoki
yake bayyana yadda yake aiwatar da yaƙi
a cikin labarin. Misali ya ce na buɗe takobi, na zaburi dokina na ce maza bisa kanku”.
Yahaya
(2014:69) kuwa, ƙarawa ya yi da cewa, “..., aiwatarwa hanya ce ta
yin wani abu ta hanyar amfani da ƙarfi
ko tasiri”.
Bisa
bayanan da suka gabata za a iya cewa, aiwatarwa a cikin ƙagaggun labarai na Hausa na nufin yadda taurarin
cikin labari suka aikata wani abu. Shi kuma Hoton gurbi a iya cewa duk wani
wuri ko wata da’irar da wani abu ya wakana ko zai wakana cikin ƙagaggun labaran Hausa. Wannan dabara ta ƙulla zance cikin labari da mawallafa ƙagaggun labarai suke amfani da ita tana da tasiri ƙwarai da gaske, domin tana ƙara wa mai karatu azamar sanin abubuwan da za su
faru a shafuka na gaba na littafin da yake karantawa.
1.3
LABARIN BAƘIN KISHI
Baƙin Kishi
labari ne a kan wani magidanci mai suna Alhaji Basiru da matarsa Hajiya Ruƙayya. Sun kasance suna rayuwa ta jindaɗi ba
tare da ana jin kansu ba. Kwatsam wata rana sai mai gidan ya sanar da matarsa
cewa zai ƙara aure. Wannan
zance ya haifar da rashin jituwa a tsakaninsu matuƙagaya. Yai ta mata nasiha amma ba ta
gamsu ba.Shi kuwa Alh.Basiru ya auro amaryarsa mai suna Zainab. Wannan abu ya
baƙantawa Haj. Ruƙayya rai. Ana cikin wannan hali, sai ƙawarta Baraka ta ziyarce ta, ta kuma
fahimci halin da take ci. Da yake masu iya magana kan ce, “Abokin kuka ake faɗa
mutuwa”, sai Haj. Ruƙaiya
ta kwashe labari ta faɗawaƙawarta. Baraka kuwa, sai ta ba ta
shawarar su je gun boka don samun mafita. Haka kuma aka yi. Boka ya ba da
magani cewa ta haɗa da alewa ta bai waɗan
Zainab Mujahid. Amma kash! Sai reshe ya juye da mujiya, domin kuwa bai sha
alewar da ta ba shi ba, ya manta a aljihun wandonsa na makaranta. Ko da
mahaifiyarsa Zainab ta gani sai ta kawo wa mahaifinsa. Shi kuwa Alhaji Basiru
ya raba musu shi da yayunsa, ‘ya’yan Haj.Ruƙaiya,
wato Hauwa da Sailuba. Nan fa ya yi fushi, ya jefar da tasa, saboda cewa sun
sha nasu a makaranta, kuma nasa a raba musu. Shan alewar da su Hauwa da Sulaiba
suka yi, nan take suka faɗi suna shure-shure har suka
mutu. Shi kuwa, Alh.ya yi ta fama da jinya, kana daga bisani ya warke. Haj.Ruƙaiya ta kai ƙara kotu, amma dai gaskiya ta yi
halinta, aka fahimci cewa ita ta sanya gubar. Alƙali
ya yanke mata hukuncin rai-da-rai.Shi kuma, Alh. Basiru da Zainab suka ci gaba
da zamansu na aure lafiya.
2.1 HOTON GURBI DA
AIWATARWA A LABARIN
Dabara ta ƙulla zance cikin labari ta hanyar amfani
da Hoton Gurbi da Aiwatarwa tana taka muhimmiyar rawa, musamman wajen ƙarawa mai karatu fahimtar labarin, kamar
yadda aka fara cin karo da hoton gurbi a shafi na 7 cikin labarin:
“Ta sunkuyar da kanta da
sauri kana ta sa tafukan hannunta ta rufe idanunta, “Alhaji da gaske ka ke
Allah” Ta buƙata
da muryar kunya”
(shf na 7).
Wannan Hoton Gurbi da shi
aka buɗe
labarin cikin littafin, a inda mawallafin yake ƙoƙarin kawo hoton tattaunawa da take
faruwa tsakanin Alhaji Bashiru da budurwar da yake nema zai aura Zainab.
Daganan kuma sai aiwatarwa ta biyo baya kamar haka:
“Ta yi gaggawar girgiza
kai,” Wallahi baHaka ba ne Alhaji. Ta faɗa da
saurin baki,A lokaci guda kuma tana mai ci gaba da girgiza kai.”
(shf na 7)
Haka kuma, bayan wannan
akwai wata aiwatarwar ma da ta biyo baya duk dai hira ce da take gudana
tsakanin Zainab da Alhaji Basiru a kan jaddada ƙaunarsu
da juna, wannan ta zo ne a lokacin da:
“Ta ɗaga
kai ta dube shi fuskarta ƙunshe
da alamar tambaya.”
(shf na 8)
Haka dai aiwatarwa ta ci
gaba, mawallafin ya kawo wani gurbi lokacin da yake ƙoƙarin
kawo tattaunawar da take gudana tsakanin shi Alhaji Basiru da uwargidansa
lokacin da yake ƙoƙarin shawo kanta a kan ta yi haƙuri game da ƙarin aure da zai yi, amma kuma ta ƙi ta fahimce shi, kamar haka:
“Alhaji Bashiru ya yi
murmushi a karona farko tun tsawon kusan mintuna talatin da suka shafe suna
musayar yawu da maiɗakinsa
Hajiya Ruƙayya.” (shf
na 10).
Daga nan kuma sai mawallafin
ya yi amfani da aiwatarwa inda ta biyo baya kamar haka:
“Hakan shi ya haifar da
shirunwucin gadi a tangameman falon”.
(shf na 10).
A nan ma mawallafin Baƙin Kishi ya
sakekawoHoton Gurbi a lokacin da ya nuna Hajiya Ruƙayya a cikin ɗakinta
kamar haka:
“Kamar kowace safiya yau ma
ita kaɗaice zaune cikin ɗakin
nata, ta yi tagumi tana ta saƙe-saƙen hanyar da za ta bi don
ganin bayan kishiyar tat (shf na 14).
Aiwatarwa ta biyo wannan
hoton gurbin lokacin da tana cikin saƙe-saƙen sai ga wata baƙuwaƙawarta
ta yi sallama, ganin ƙawarta
ke da wuya sai ta karɓe ta da cewa:
“A, a ah! Baraka………. Yaushe
a gari in ji maƙi baƙo.Saukar yaushe? Ta ce cikin
fara’a bayan ta kawar da alamun tunani da damuwar da suke kan fuskarta, sannan
da gaggawa ta miƙe ta
tari ‘yar siririyar matar da take ƙoƙarin shigowa ɗakin”. (shf na 15)
Haka kuma mawallafin ya kawo
wani hoton gurbi lokacin da baƙuwar
ta nemi zama, tana cewa:
“Wayyo Allah makashin
kakana!Baraka ta ce daidai lokacin da taZauna a ɗaya
daga cikin manya-manyan kujerun laushin da ke cikin ɗakin”
(shf na 16).
Haka suka ci gaba da
maganganu har ta fahimci cewa ai kishiya aka yi wa ƙawar tata, daga nan kuma ta saka ta a
hanyar neman magana, domin kashe ɗan
kishiyar tata, wanda ya jawo abubuwa da dama cikin labarin. Mawallafin ya kawo
Aiwatarwa kamar haka:
“Ba ta yi tunanin komai ba
ta amsa, “Allah ya kai mu goben lafiya. Amma fa kin san ba na son a fara ta
kanta, na fi son a fara ta kan wannan shegen ɗan
musamman ma illar rayuwarsa da ki ka fito mini da ita”
(shf na 23).
Wannan ya nuna irin halaye
na rashin imani da mata suke shiga, musamman ma idan idonsu ya rufe wajen
kishi, wanda rashin tsoron Allah yake kawowa. Mawallafin ya kawo wani hoton
gurbin da ba mamaki wani abu zai faru; domin ya zo ne a lokacin da Hajiya Ruƙayya take tattauna yadda za su fito wa
lamarin kishiyarta da baƙuwarta
Baraka, kwatsam, sai ga amaryar tata Zainab cikin ɗakin,
kamar yadda aka kawo:
“To, a daidai lokacin ne
Zainab taɗaga labulen ɗakin
ta shigo gamida sallama, shigowar da ta zamar mata da-na-sani”
(shf na 23).
Wannan yanayi ya haifar da
amfani da wannan dabara ta ƙulla
zance, a lokacin da Baraka ta nemi amsa sallamar Zainab, amma kuma Hajiya Ruƙayya ta jawo hankalinta da wannan
aiwatarwar:
“Yunƙurin amsawar da Baraka ta yi
ya gaza kai gaci saboda zungurarta da Hajiya Ruƙayya ta yi gami da cewa, “ke
ita ce fa!”
(shf na 23).
Mawallafin ya ci gaba da
kawo hoton gurbi, wato lokacin da wata mata ta shigo gidan Alhaji Basiru, daga
nan kuma sai aiwatarwa ta biyo baya kamar haka:
“Wata dalleliyar mota ƙirarkia picanto shuɗiya,
ta cusa kai cikin tafkekiyar harabar makeken gidan bayan buɗe
babbar ƙofar
da mai gadi ya yi”
(shf na 26).
Mawallafin ya kawo
aiwatarwa, domin ya nuna cewa gidan Alhaji Basiru motar ta shigo, tare da mai
gidan.
“Alhaji Basiru, baƙi, kakkaura mai Matsakaicin
tsawo ya fito. Kallo ɗaya
za ka yi masa ka laƙanci
ya na da fara’a sosai duk da wadatattun kumatun da yake dasu”
(shf na 26).
Daga wannan kuma wata
aiwatarwar ta biyo lokacin da Alhaji Basiru ya yi sallama, domin shiga falo
inda mawallafin ya kawo hoton gurbi na Zainab zaune a falo:
“Zainab kyakkyawa fara da ke
zaune kanɗaya daga cikin
tausasan kujerun da ke kewaye da falon ta amsa sallamar da tuni ta gane muryar
da ta yi ta, cikin fara’a ta miƙe ta
tare shi, ta karɓi ƙaramar jakar da ke riƙe a hannunsa”
(shf na 27).
Mawallafin ya kawo wani
hoton gurbi na Hajiya Ruƙayya
tana gyara kwalliyarta a gaban wani madubi da ta saba amfani da shi duk lokacin
da ta yi wanka, wanda ba mamaki wani abu ya biyo baya:
“Ta isa ga wani tafkeken
madubi da ke kafe a jikin bango wanda a shi ne take yin kwalliya a duk sa’ar da
ta yi wanka. Ta ƙarewa
kanta kallo tsaf a cikin madubin kana ta yi murmushi”
(shf na 34).
Bayan ta gama kwalliya sai
ta nufi wajen mijinta domin neman izinin zuwa unguwa wato za ta je gaisuwar
mutuwa. Ko da yake ƙarya
ta shirya, wurin boka za su je ita da ƙawarta
Baraka. Ta nemi Alhaji Basiru mijinta da ya ba ta damar tuƙa mota da kanta, domin kar su je da
direba asirinta ya tonu. Ga abin da ya biyo baya:
“Ta langwaɓar
da kai a kan majinginar kujerar kana tana kuma fari da fararen idanunta, waɗanda
sau da yawa ta san fari da sukan yi tasiri wajen jan hankalinsa. Sannan da
sababbiyar muryarta ta yaudara ta ce, Alhaji, ina so na je unguwa ne idan an
jima.
(shf na 39).
Daga baya da kyar da ta sha
kan Alhaji Basiru ya yarda, amma ba domin yana so ba, a inda mawallafin ya yi
amfani da wannan aiwatarwan domin ƙarin
haske lokacin da:
“Ta mayar da kanta ta
jingina jikin majinginar kujerar saboda daɗin
da ya mamaye ta. A hankali ta shiga furta, “Na gode Alhaji, Allah ya ƙaradanƙon soyayya tsakaninmu”
(shf na 43).
Mawallafin ya kawo wannan
dabara ta hoton gurbi domin ya nuna cewa wani abu zai faru, wato anan Hajiya Ruƙayya za ta tsaya da mota domin ƙarasawa wajen bokan, lokacin da Baraka:
“Ta ɗaga
yatsanta manuni, ta yi nuni da wata ‘yar karkatacciyar bishiya da ke gabansu kaɗan,
idan kin isa ga bishiyar can sai ki tsaya, mun iso gidan”
(shf na 45).
Bayan sun sauka daga mota
sun nufi ɗandurƙusasshen
gidan cikin fargaba da tsoro sai suka ji wata murya mai ban tsoro ta ratsa su
tana ce da su:
“Ku tsaya nan, karku kuskura
ku kuma takawa, idan ba haka ba fuskokinku za su komo ƙeya, mutanen banza,”
(shf na 46)
Daga nan sai kuma aka sami
aiwatarwa kamar haka:
“Karfe takwas dai dai agogon
dake rataye jikin bango cikin makeken falon ya saki wani daddaɗanƙara, ƙaran da ya ja hankalin
Zainab da yaran uku da ke cikin falon zuwa gare shi”
(shf na 52).
A nan, ana bayyana wani
hoton gurbi ne da wani abu zai wakana. Wato lokacin da Zainab da ‘ya ‘yan
Alhaji uku wato Mujahid ɗanita Zainab ɗin
da kuma Hauwa’u da Sailuba ‘ya’yan Hajiya Ruƙayya
suna jiran zuwan direba, domin ya kai su makaranta.
A “cikin wannan hali na
damuwa da Zainab take ciki Hajiya Ruƙayya
ta shigo falon da sauri kamar wadda aka biyo a guje” (shf na 53)
“Lokacin da suka isa
makaranta tuni ɗalibai Sun jima da
shiga azuzuwa, wasu ma har sun fara karatu. Amma duk da haka wannan bai hana
Hajiya Ruƙayya
tsayawa a wani ɗan madaidaicin shagon
sayar da kayan tsotse-tsotse, dangin su alewa da ke cikin makarantar ba.”
(shf na 55).
A nan mawallafin ya kawo
hoton gurbin shagon da Hajiya Ruƙayya
ta tsaya ta saya wa yaran biskit da alewa, amma maimakon ta bai wa Mujahid daga
cikin alewar da ta saya, sai kawai ta ɗauko
alewar da ta sa wa gubar da Boka ya ba ta ta ba shi. Sauran yaran kuma ta ba su
wadda ta saya a shagon. Kamar yadda bayanin aiwatarwa ya zo kamar haka:
“Yi haƙuri Mujahid, kai bari na ba
ka taka alewar mai daɗi ka
ji. Ta ce tana yin wani irin murmushi, sannan ta buɗe
‘yar ƙaramar
Jakarta da ke ajiye gaban mota, ta ɗauko
alewa. Riƙe da
kyau, kar ka kuskura ka ba kowa. Kowa ya sha tasa, kun ji ko? Ta gargaɗe
su.”
(shf na 57).
“Tafiyar ruwa ta so ta yi da
su ba don sun ba ta hanya ba. Shakka babu ta tsorata su ganin shigar ta falon
kamar kibiya”
(shf na 70).
Wannan hoton gurbi an kawo
shi, domin a nuna aiwatarwar da ta biyo bayansa, kamar yadda mawallafin ya
kawo.
“A ka ta ɗora
hannunta biyu ta ƙwalla
wani irin ihu mai gauraye da kuka. Lokaci guda ta nufe su, ta dire gwuiwoyinta
biyu a kan kilishin da ke shimfiɗe a
falon, ta tallafo kan Sailuba, ta girgiza ta, kana da sauri ta mayar da ita ta
tallafo Hauwa’u ta girgizata, a yanzu sun daina motsi, Jikin su ya saki kamar
matattu,”
(shf na 70).
Wannan lamari ya faru ne
lokacin da reshe ya juye da mujiya, domin maimakon Mujahid ɗan
amaryar tata ya sha alewar da ta ba shi mai guba, sai ‘ya’yan ta suka sha.
Ganin haka ne ta shiga wannan hali nakiɗimewa,
ba ta san ma lokacin da ta aiwatar da waɗannan
kalamai ba:
“Take ta kuma kurma wani
uban ihucure da wani kuka mai tsuma zuciya.wayyo Allahna……….. yan biyu
sunmutu.”
(shf na 71).
Waɗannan
su ne wuraren da mawallafin ya yi amfani da wannan dabara cikin littafinsa,
domin ƙulla zance. Ga bayanin sakamakon
binciken a jadawali nan ƙasa.,
kamar haka:
2.2 JADAWALIN BAYANIN AMFANI DA DABARAR ƘULLA
ZANCE A WASU SHAFUKA: LITTAFIN BAƘIN KISHI (BK)
|
Lambar
shafi |
Hoton
Gurbi (Adadi) |
Aiwatarwa
(Adadi) |
|
7 |
1 |
1 |
|
10 |
1 |
1 |
|
14 |
1 |
0 |
|
15 |
0 |
1 |
|
16 |
1 |
1 |
|
23 |
1 |
2 |
|
26 |
1 |
1 |
|
27 |
1 |
0 |
|
34 |
1 |
0 |
|
39 |
1 |
0 |
|
43 |
1 |
0 |
|
45 |
1 |
0 |
|
46 |
0 |
1 |
|
52 |
1 |
0 |
|
53 |
0 |
1 |
|
55 |
1 |
0 |
|
57 |
0 |
1 |
|
70 |
1 |
1 |
|
71 |
0 |
1 |
Wannan jadawali ya yi ƙoƙarin
kawo bayanin yawan amfani da wannan dabara ta ƙulla
zance ta Hoton Gurbi da Aiwatarwa a cikin samfurin wasu shafuka na littafin BaƙinKishi.
An kawo samfurin shafuka
goma sha tara (19) daga cikin littafin. Hoton gurbi ya zo cikin shafuka goma
sha huɗu
(14),,aiwatarwa kuma sau goma sha biyu (12). Idan aka duba jadawalin, shafi na
15, ba a sami hoton gurbi ba sai aiwatarwa. A shafi na 23 kuwa, duk da cewa an
sami hoton gurbi 1, amma aiwatarwa sau biyu ta bayyana. Sai da kuma, marubucin
ya jingine aiwatarwa, ya yi ta amfani da hoton gurbi har sau biyar a shafuka
mabambanta, kafin aka sami aiwatarwa. Haka dai marubucin ya riƙa sarrafa hoton gurbi da aiwatarwa a
labarin har zuwa ƙarshe,
inda aka gano cewa, da aiwatarwa ya rufe. Amm duka da haka, alƙaluma sun nuna cewa hoton gurbi ya ɗara
aiwaatarwa da guda biyu a labarin. Wannan ya nuna cewa hoton gurbi yana da kaso
53.8%, a yayin da aiwatarwa ke da 46.2%.
3.0 KAMMALAWA
Wannan takarda ta yi nazarin
hoton gurbi da aiwatarwa a labarin Baƙin
Kishi,Mun ga yadda marubucin labarin ya yi amfani da waɗannan
dabaru wajen ƙulla zaren
labarinsa.Yin haka, ya sanya, kamar yadda muka fahimta sun taimaka wajen fito
da babban saƙon labarin da
mabiyansa cikin sauƙi.Daga
ƙarshe, yayin kammala wannan takarda an
gano cewa, bincike bai yawaita a wannan ɓangarena
duba ƙagaggun labarai ta sigar hoton gurbi da
aiwatarwa ba. Yawanci aikace-aikace da aka gabatar a kan labaran zube sun shafi
nazarin zubi da tsari da salo da jigo ne, don haka, ake kira da a rungumi
wannan dabara ta ƙulla
zance cikin labari, kamar yadda Mukhtar (2004) ya samar domin haɓaka
nazarce-nazarcen salo a cikin adabi.
Adamu, G. (1995). “A
Stylistics Criticism of the Hausa Noɓel ShaihuUmar”,
Kudin Digiri na Biyu, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Sokoto: Jami’ar Usman Ɗanfodio.
Adamu, G. (2002). “A
Stylistics Study of Hausa Classic Noɓels:
ShaihuUmar, Ruwan Bagaja, and Kitsen Rogo”. Kundin Digiri na Uku,
Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Auta, A. L. (1988). “Sharhin
Ciki da Waje A Kan Littafin So
AljannarDuniya”.Takardar da aka gabatar a Taron Ƙara Wa Juna Ilimi, Sashen Koyar da
Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.
Buhari, I. M. (1988).
“Nazarin Jigogin Ƙagaggun
Labaran Hausa”. Kundin Digiri na Biyu, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Kano:
Jami’ar Bayero.
Dutsenma, L. A. (2002).
“Tarbiya A Ƙagaggun Labarai Na
Hausa”. Kundin Digiri na Biyu, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar
Bayero.
Ɗangambo,
A. (1974). “Nazari a Kan Na Gari Na Kowa Na Jabiru Abdullahi”.Cikin Harsunan
Nijeriya, IƁ. CSNL.Kano; Ahmadu
Bello Uniɓersity, Abdullahi Bayero College.
Ɗangambo,
A. (1989). “Ƙagaggun Labarai:
Yanayinsu da Sigoginsu”. Takarda da aka gabatar a Taron Ƙungiyar Hausa ta Babbar Makarantar
Sakandare ta St. Thomas, Kano.
Gusau, S.M. (1995). Dabarun Nazarin Adabin Hausa Kaduna:
Fisbas Media Serɓices.
Lawal, M. B. (2008). Baƙin
Kishi. Kano: Iya Ruwa Publishing Company Ltd.
Mukhar, I. (1987). “Bitar
Nazarce-Nazarcen Salo a Cikin Rubutu”. Takarda da aka gabatar a taron ƙarawa Juna Ilimi na huɗu
kan Harshe da Adabi da Al’adu na Hausa. Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya,
Kano: Jami’ar Bayero.
Mukhar, I. (1990). “A
Stylistics Study of Suleiman Ibrahim Katsina’s Hausa Noɓels”.
Kundin Digiri na Uku, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.
Muktar, I. (1993). “Yanayin Ƙagaggun Labarai Na Hausa”. Takarda da
aka Gabatar a Taron Ƙarawa
Juna Sani na uku kan Harshe da Adabi da Al’adun Hausa. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero
Mukhtar, I. (2001).
“Al’amuran Dubawa Cikin Fasalin Nazarin ƘagaggunLittattafai”.
A Cikin Algaita Journal of Current
Research in Hausa Studies. Ɓol 1
No. 1 Sashen Koyar Da Harsunan Nigeriya, Kano: Jami’ar Bayero.
Mukhar, I. (2004). Jagoran Nazarin Ƙagaggun Labarai.
Kano: Benchmark Publishers Ltd.
Yahaya, U. (2004). “Sigogin
Bayar Da Labari: Kamar Yadda Aka Yi Amfani da Su A Kan Littafin AmadiNaMalamAmah
da TauraruwarHamada” Kundin Digiri na Biyu. Sashen Koyar da Harsunan
Nijeriya. Kano: Jami’ar Bayero.
Yahaya, U. (2014). “Dabarun
Bayar da Labari: Tsokaci a Kan Hoton Gurbi da Aiwatarwa a Littafin Amadi Na
Malam Amah” a cikin Akwanga Journal of Hausa Studies. Ɓol. 5, No. 1 pp 66-77

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.