Citation: Shu’aibu Hassan (2017). Barkwanci Ga Wanzamai: Kwatancin Waƙar “Idi Wanzam” Da Labarin Azrael The Barber Na Tawfiƙ Al-Hakim. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 5. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
BARKWANCI
GA WANZAMAI: KWATANCIN WAƘAR “IDI WANZAM” DA LABARIN AZRAEL THE BARBER NA TAWFIƘ
AL-HAKIM
Na
Shu’aibu
Hassan, PhD
ABSTRACT
Barbers
are people who use sharp knives and other tools to cut low or
completely shave the hair of their clients. This paper
is an attempt to compare barkwanci associated with barbers from two different
cultures: Sa’in Makafin Zazzau of Hausa and Azarel the Barber of Arabic Egypt.
The paper suggests that why barbers are associated with barkwanci is because of
two things: i. the working tools are very sharp hence pose danger to the
clients; ii. considering the nature of the tools, the clients are not so safe
if the barber happened to be insane and not psychologically balanced. So the
society applies barkwanci to some barbers and portrays them as psychos and
poses a threat to the clients. The paper compares the nature of the barkwanci
done to ‘Idi Wanzam’ of Hausa and that of Azaerel by Tawfiƙ al-Hakim in Egyptian society.
1.0
GABATARWA
Wani lokaci akan ga wasu abubuwa da suka danganci
adabi suna kasancewa game-duniya ta yadda za a ga ƃurƃushinsu
cikin adabi na al’ummu
daban-daban, da irin kama guda, ko kuma a ga bambancin da bai
taka-kara-ya-karya ba. Wannan maƙalar
ta ƙyallo wani ɓurɓushi
ne na adabi da ya danganci barkwanci da aka yi wa wanzamai a Hausa da kuma
wanda aka tsinta daga rubutaccen adabi na Tawfiƙ al-Hakim, adibi daga ƙasar Masar.
Irin barkwanci da aka ga an yi wa wanzamai cikin
adabin Hausa da na Tawfiƙ
(Larabci) ne yake da ɗaure kai. Misali, me ya sa Salisu Sa’in Makafin Zazzau
ya yi wa Idi Wanzam waƙa ta
barkwanci? Me kuma ya sa aka ga wani labari na barkwanci ga Wanzam Azrael da
Tawfiƙ al-Hakim ya kawo a
rubuce-rubucensa? Amsa waɗannan tambayoyi ya haifar da wannan kwatanci na adabin
Larabci da Hausa a kan barkwancin da ake yi wa wanzamai.
Abin mamaki game da waɗannan
nau’o’in adabi guda biyu daga mabambanta al’adu, shi ne yadda aka danganta
wanzamai da cutar ƙwaƙwalwa, wato motsuwa ko hauka ko dai wani hali na
rashin lafiya ta yadda za su kasance barazana ga wanda suke yi wa aski ko
gyaran fuska. Sannan in an lura, za a ga barkwanci ne ake yi wa wanzaman domin
nishaɗi: a yi raha. Ta fuskar ma’ana, masana suka ce
barkwanci wasa ne a cikin zance, wanda zai iya haifar da raha. Barkwanci yakan ɗauki
salon ba’a, domin a nuna fifiko ko wata gazawa ta wani ko wasu ko kuma wata ƙabila, domin a yi nishaɗi.
An karkasa barkwanci da cewa akwai wadda yake aukuwa tsakanin mutum da ɗan’uwansa,
la’alla ta fuskar dangantaka, ko tsakanin masu sana’a, ko tsakanin ƙabilu daban-daban. Duk ana aiwatar da irin wannan
barkwanci ne domin a yi wa mutum iya-shege da nufin ƙara danƙon
zumunci a tsakani (Zarruƙ,
R.M. da wasu, 1987:41).
2.0
SANA’AR WANZANCI
Manazarta sun yi
rubuce-rubuce da yawa a kan sana’ar wanzanci da irin gudummuwar da wanzamai
suke bayarwa ga al’umma, musamman al’ummar Hausawa. Alal misali, Habib, A. da
Musa, U.I. da Zarruƙ,
R.M. (1988:58) sun bayyana wanzanci da cewa, “Sana’a ce
ta yin amfani da aska don aske gashi, da yanke loƃa,
da yin tsaga ko ƙaho,
saboda rage ƙazanta da neman
lafiya da tsare al’ada”. Shi kuwa Sallau (2010)
cewa ya yi:
Sana’ar wanzanci tana nufin
amfani da askar aski don yin aski da gyaran fuska da yin kaciya da kuma amfani
da kalaba da ƙoshiya don cire belun
wuya. … ana amfani da ‘yar tsaga don yin ƙaho da cire angurya a farjin mata da yin
tsagar gado da ta kwalliya da ta magani. … ana
yin hujen kunne da yanke yatsan cindo da yanke linzami a cikin bakin jarirai da
wasu ayyuka da dama. Haka kuma, masu yin sana’ar wanzanci na bayar da magungunan gargajiya
ga waɗanda
ke buƙata (Sallau, 2010: 33).
2.1
KAYAN AIKIN SANA’AR WANZANCI
Sana’ar wanzanci ba ta
gudana sai da kayayyaki irin su aska, da fatar wasa asake, da dutsen washi da
almakashi da kofi da sabulu da ruwa da kalaba da ƙoshiya
da hantsaki da ‘yar
tsaga da ƙaho da jijiya da
sauransu. Akasarin waɗannan kayayyaki ana zuba su
ne a cikin zabira, wato wata jaka da ake rataya ta a kafaɗa.
3.0
NAU’O’IN WANZAMAI
Idan aka la’akari da yanayin
sana’ar wanzanci, musamman a jiya da yau, za a iya kasa ta zuwa waɗannan
rukunai:
Wanzaman Кoƙo:
Wanzaman …:
Masu askin Baba (na zamani):
Dalilin kiran su masu askin baba kai tsaye shi ne, idan an lura da aikinsu, ba
sa yin wani abu da ya wuce aski. Askin nan zai iya kasancewa saisaye ko ƙwaryar molo ko kuma gyaran fuska. Kayan
aikinsu kuma su ne kilifa (clipper) da burushi da isga da ƙyalle (na yafawa a wuyan wanda ake yi
masa aski don kar gashi ya ƃata
masa jiki) da hodar hana ƙuraje
da ruwan maganin sifirit (spirit) da sauran mayuka na ƙawa ko hana ƙurajen gashi. Sannan sai uwa uba, wutar
lantaki.
3.1
WANZAMI A MAHANGAR AL’ADA
Wamzami mutum ne mai daraja
da muhimmanci a cikin al’adar Hausa, da ma sauran al’ummu saboda irin
muhimmancin da sana’ar tasa take da shi. Idan dai aka ce al’umma kamila ce
wadda ta fita daga cikin duhun kai na wayewar duniya, ta san yadda za ta
suturta jikinta da tsaftace shi, to dole kuwa a ce al’adar wannan al’ummar ta
tanaji hanyar da za a gyara suma da duk wani gashi da ke jikin ɗan’adam.
Suma da gashi kan kasance abin ƙawa,
amma rashin gyara su kuma, kan iya zama ƙazanta.
Wanzami aka sani da ɗaukar wannan hidima ta
gyaran fuska da duk wasu nau’o’i na aski domin kawar da gashin da ba a buƙata a jiki, in dai bai shafi wuraren da
al’ada ba ta yarje wa wani ya
gani ba.
La’akari da wannan matsayi
na sana’ar wanzanci da matsayin wanzamai, ya sanya manazarta ke ta ƙoƙarin
nuni kan muhimmancin sana’ar
cikin al’umma. Habib da wasu (1988)
suka ce, “cikin
masu sana’o’in gargajiya na Hausa,
wanzami tamfar likita ne na fiɗa.” Lalle kuwa, domin a yau
babu wata al’umma da ba ta san muhimmancin likitan fiɗa
ba. In mutum bai yi gamo da abin da zai haɗa
shi da likitan fiɗa ba, to lalle ya ji labari
daga wajen wani ko wasu.
Malaman sun ci gaba da kawo
ire-iren ayyukan da wanzami yake yi, inda suka nuna cewa shi ke yin “aski ƙwal- kwabo ko ƙwaryar molo, da jarfa; wanzami shi yake
yin ƙaho, don fitar da mummunan jini daga
jikin mutum.”
Suka ƙara da cewa “shi yake yi wa yara kaciya.
Bayan haka wanzami ne yake fid da hakin wuya, da haƙorin shuwa, da gurya, da sauran abubuwa
irin waɗannan.”
Ba su tsaya a nan ba sai da suka nuna cewa wanzami “ke yi wa mutane tsaga da ƙyasƙyastu.
Wani lokaci sakiya ma wanzami ne yake yin ta.”
Saboda muhimmancin wanzamai
ta fuskar al’ada da kuma irin ayyukan da sana’ar tasu ta sanya suke yi, su
Habib (1988) sun ci gaba da cewa, “Sarakuna suna kusantar da wanzamai a fadarsu
saboda muhimmancin wanzanci. Kuma har suna naɗa
musu Sarkin Aska, da Ɗangaladima,
daga cikinsu.” Ba
sarakuna kawai ke ganin ƙimar
wanzamai ba, don kuwa “
jama’a suna ba wanzamai girma,
don haka ma duk wani buki da aka yi sai an ware musu nasu rabo ko ba sa nan.”
Shi ma ɗan
na-gada, wato Sallau (2010), cewa ya yi:
… sana’ar wanzanci ta taƃo aikin likita a ƙasar Hausa kafin zuwan likitan zamani.
Dalili kuwa shi ne, wani daga cikin aikin wanzanci shi ne kula da lafiya
musamman ta jarirai da ƙananan
yara, ta wani fannin ma har da lafiyar manya. Masu yin ire-iren waɗannan
ayyuka ana kiransu wanzamai waɗanda dole su kasance masu
cikakkiyar lafiya, masu hankali da natsuwa (Sallau, 2010: 34).
Idan aka yi la’akari da
yanayin aikin wanzami a tsakanin jama’a, za a iya cewa “ya fi kowa kusanta da
jama’a saboda yawan mu’amala da su kuma kasancewarsa tamfar wani maroƙi a tsakaninsu. Har ma ana yi masa
kirari da cewa:
Kalakala maganin gizo ɗan
wanzam,
Aska na cikin kube tana cin
gashi,
Ka wa Sarki rotse ka tashi
da girma!
Ɗan
wanzam na Sarkin Aski,
Ba ka so ga jikinka. (Habib
da wasu, 1988: 59).
3.2
WANZAMI CIKIN ADABI
Idan aka yi dubi da irin
kyakkyawan matsayin da wanzami yake da shi cikin al’adu daban-daban na duniya,
ciki har da Hausa, sai a ga akasin haka a cikin adabin al’ummu da dama. A cikin
adabin, akan ɗan muzanta su ta hanyar yi musu
barkwanci, ko nuna su a matsayin masu yawan surutu da shiga sharo ba shanu,
cikin harkokin jama’a. Babbar isharar da za mu yi a nan ita ce yadda aka nuna
wasu wanzamai guda bakwai cikin shahararren littafin nan mai suna Dare Dubu Da Ɗaya,
littafi na ɗaya. Waɗannan
wanzamai su ne Wanzamin Bagadaza, wato Shehu Samitu, wanda aka nuna da yawan
surutu, da kuma ayyuka irin na motsattsu. Sauran shidan su ne, Baƙaƙu,
da Haɗɗaru,
da Baƙ-baƙ, da
Kuzul Asawati, da Assharu, da kuma Saƙalilu.
Waɗannan
wanzamai duk an nuna su da wasu halaye na rashin natsuwa, musamman ma
shugabansu, wato Samitu (Malumfashi, da Haruna, da Mada, 1, 2015: 287 – 332).
Haka kuma a cikin Magana Jari Ce 2, a labarin “Ba Ruwan
Arziki Da Mugun Gashi, Wanda Allah Ya Ba Haƙuri
Ya Fi A Zage Shi”,
mun ga yadda ta kaya da wanzamin Isa Lamiri, wato Shu’aibu ɗan
wanzam, mai kayan kaifi. A farko dai ba a nuna ɗan
wanzam yana da wani taƃin
hankali ba, amma daga bisani, sai aka nuna yadda ya birkice, domin ya ga abin
da ya faru a kan idonsa, tsakanin Isa Lamiri da Buzu (Imam, 2, 1945: 9 – 13).
A littafin Yawon Duniyar Hajji Baba kuwa, ba a taƃa mutuncin wanzami ba, sai ma aka yi ƙoƙarin
nuna darajarsa a cikin al’umma:
Ubana sunansa Hassan, yana
kuwa ɗaya
daga cikin wanzamai waɗanda suka shahara a Isfahan.
… Amma gwanintarsa ta wanzanci, musamman tsakanin ‘yan kasuwa, ta sa bayan
shekara ashirin ya sake auren wata yarinya ‘yar wani mai arziki. Bai sha wata
wahala game da auren nan ba, domin ya saba da mai arzikin, kuma shi yake yi
masa aski (Tunau, 1966: 1).
A nan, sana’ar wanzancin ta
samar wa Hassan Wanzan wata daraja ce, har ya shahara a birnin Isfahan, kuma
har ya iya auren ‘yar mai arziki na birnin, kasancewarsa wanzamin mutumin.
Daga cikin rubuce-rubuce na
adabi da aka nuna wani hali na barkwanci ga wanzami, akwai na Tawfiƙ al Hakim, wato na Wanzam Azarael, wanda
wannan maƙala take aiki a kai.
4.0
BARKWANCI GA WANZAMAI
Sallau (2010: 34) ya
tabbatar mana da cewa sana’ar wanzanci ta mutane ne:
… waɗanda
dole su kasance masu cikakkiyar lafiya, masu hankali da natsuwa. Makaho ko
wanda ba ya gani sosai, ko mai hannu ɗaya,
ko kuturu ko mahaukaci ba sa iya yin ayyukan sana’ar wanzanci don tsoron kar a
fuskanci matsalar da za ta iya cuta wa waɗanda
za a yi wa ayyukan.
Idan aka yi la’akari da abin
da Sallau ya faɗi a nan a kan su waye ya
dace su yi sana’ar wanzaci, to za a ga babu makaho a ciki. Bisa ala’ada, an san
da karin maganar nan da ke cewa, ‘haushin rashi, makaho ya ce ido da ɗoyi.’
In kuwa haka ne, ashe ba abin mamaki ba ne a ji makaho yana yi wa wanzami iya
shege domin ya san sana’a ce da ta gagare shi. Wannan hanzari ba gudu ba ake
gani ya sanya Sa’in Makafin Zazzau ya yi waƙar
Idi Wanzam. Bisa al’ada,
ba a taɓa
jin cewa akwai wani dalili da ya haifar da wasan barkwanci tsakanin wanzamai da
makafi ba, kamar yadda aka sani tsakanin wasu masu sana’a kamar a ce malami da
maharbi, ko ɗan bankwai da barinde, ko maƙeri da wanzami da ire-irensu.
Wani hasashen da ake da shi
a kan wannan barkwanci da ake yi wa wanzamai shi ne la’akari da aka yi da irin
yanayin kayan aikinsa, da kuma yadda duk mai son ya yi masa aski ko gyaran
fuska, yake miƙa masa kansa gaba ɗaya.
Mutum ya miƙa kansa ga mutumin da
yake ɗauke
da makami (aska) mai kaifin tsiya, ya sanya ta a wuyansa da kunnensa da
hancinsa da tsakar kansa, ai abin dubawa ne. Wannan dalili ne kuwa ya sanya
dole mai irin wannan sana’a ya kasance mai cikakken hankali da natsuwa. Rashin ɗayan
waɗannan
zai iya zama ɓarna. Waɗannan
abubuwa biyu muhimmai, su ne Azarael Wanzam da Idi Wanzam suka rasa daga
labarin Tawfiƙ da kuma waƙar Salisu Sa’i.
5.1
WAƘAR IDI WANZAM
Karofi (1980) ya bayyana
cewa Malam Salisu ya shara sosai a ƙasar
nan a kan basirar tsara waƙar
bara. Salisu ya nuna cewa yana da yara makafi da dama da ya koya wa waƙar bara, musamman sannanun waƙoƙin
nan irin su, ‘Waƙar Wulli’ da ‘Makahon
Direba’ da ‘Waƙar Idi Wanzam’. Kaɗan
daga cikin yaran da Salisu Makaho ya koya wa waƙa su
ne, Malam Ibrahim Kunkunna da Malam Iro Ibrahim Sakkwato da Malam Audu
Sakkwato. Wannan ƙwarewa
ta Salisu Makaho ne ta kai har ya sami sarautar Sa’in Makafin Zazzau da Kaduna
(Karofi, 1980: 160 –
162).
Wannan waƙa ta ‘Idi
Wanzam’, shahararriya ce a bakin
makafi, amma an fi danganta ta da Salisu Makaho, Sa’in Makafin Zazzau, domin shi
ne aka tabbatar maƙirƙirin wannan waƙa. Baya ga yadda aka zayyana wanzami
cikin rubuce-rubuce daban-daban na adabi, a cikin adabin baka ma, musamman na
Hausa, an ga kuma yadda Salisu Makaho ya ƙirƙiri wannan waƙa, ya danganta ta da wani wanzami wai
shi Idi Wanzam, na Kwanar Gagawa. Waƙar
cike take da barkwanci domin raha ga shi wannan wanzami mai suna Idi Wanzam.
Bayan Salisu Sa’i, makafi da dama sun kwaikwaye shi, inda suke rerawa lokacin
da suke yawon bara.
Haka ma makaɗan
zamani, masu amfani da kayan kiɗa irin su fiyano, ba a bar
su a baya ba wajen kwaikwayo, tare da rera wannan shahararriyar waƙa. Fitaccen mawaƙin fiyon nan, wato Sadi Sidi Sharifai,
shi ma ya kwaikwayi wannan waƙa,
inda ya rera da muryar fitaccen ɗan
wasan kwaikwayon nan, wato Rabilu Musa ɗan
Ibro.
5.2
LABARIN AZRAEL WANZAM A TAƘAICE
Mutuwa kan iya riskar mutum
a kowane lokaci: yana sane ko ba ya sane. Akan yi wasan ƃuya da mutuwa, mutum kan iya kuƃuta, ko ya faɗa
tarkonta. Mutuwa kan ce “Na gan ka, na kuma san inda ka ƃoye.”
Rayuwarmu ta ‘yan’adam cike take da barazana,
wasu ba mu ma san da su ba: wasu sanadinsu ƙuda,
wasu cizon sauro, wasu sanadinsu hatsarin mota, ko jirgin ƙasa ko na sama. Mutum bai sani ba ma,
kila sanadin mutuwarsa tana hannun wanzaminsa da ke yi masa aski, ko gyaran
fuska, hatsarin da sam mutum ba ya zaton zai iya faruwa.
A farkon bazara na tafi
shagon wanzami domin ya yi mini gyaran fuska. Ina cike da buri na rayuwa, har
wata ‘yar waƙa na ke yi a
zuciyata. Ina tafe ina jin sautin waƙar
manoma lokacin da suke kora raƙumansu
ɗauke
da kayan kankana suna ratsa kyawawan titunan birnin Cairo. Na faɗa
cikin kujerar wanzam, na miƙa
masa kaina, na lunshe idona, kamar mai mafarkin jin daɗi,
ga fanka tana busa ni. Lokacin da wanzamin ya ɗaga
haƃata, sai na ji wata natsuwa. Daga nan ya
wasa askarsa da fatar wasa asake, har ta fara sheƙi.
Da ya dafa kaina, sai ya yi
mini magana cikin wata murya mai ban ta’ajibi, ya ce, “Ina fata ba za ka damu
ba in na ce tun ɗazu da ka shigo nake lura da
kai, kuma zuciyata ba ta yi mini ƙarya.
Ina da wata ‘yar
buƙata a gare ka.”
Ya ɗaga
askar daga goshina, amsa masa da cewa, “Ina sauraronka.”
Ya kama kaina ya fara aski,
ya ce, “Maigida, ko ka san wani a asibitin mahaukata?”
Na yi mamaki, amma sai na
daure, na ce, “Idan zuciyarka da ba ta ƙarya
ita ta raya maka haka bayan ka nazarce ni, to ba ni wata alaƙa da wannan asibitin, na gode.”
Sai ya ce, “Ka yi haƙuri, ba haka nake nufi ba. Ina nufin
cewa nazarina ya nuna mini kai mutum ne mai daraja da kila ko ka san wani
likita a asibitin.”
Na ce, “Me ya sa?”
Ya ce, “Ina da wani ɗan’uwa
mahaukaci ne a can da nake so a sake shi.”
“Mahaukaci? Ya warke ne?”
“Haukar ba mai tsanani ba
ce. Asibitin sun yi masa sharri ne. Haka suke yi a kullum sukan tsare mutune
bisa kuskure. Abin dake damunsa daga lokaci zuwa lokaci shi ne yana da wata
matsala ce da take sanya wa ya riƙa
rayawa a ransa aikata wasu abubuwa marasa hatsari. Amma bai taƃa aikata wata ƃarna ba. Bai taƃa aikata wani abu da mahaukata ke yi da
har ta kai a tsare shi a asibitin ba.
Na ce, “Abin mamaki! To me
ya sa har aka tsare shi a asibitin?”
“Ba wani dalili, yallaƃai. Matsalar mai sauƙi ce: ɗan’uwan
nan nawa shi ma wanzami ne kamar ni. Yana aiki wata rana, lafiyarsa lau, to
lokacin zafi ne, ka kuma san cewa yanayin kan sanya mutane jin ƙishi. Yana cikin yi wa wani aski, kamar
kai ɗin
nan, sai tunaninsa ya raya masa cewa kan wanda yake yi wa askin nan ya yi kama
da kankana. Yana riƙe da
aska a hannunsa, sai ya ji kamar ya tsaga kan mutumin nan.”
Ai sai nan da nan na yi
kuwwa, na ce, “Ya tsaga me?”
Cikin tattausan lafazi, ba
tare da wata damuwa ba, wanzamin nawa ya ce, “Ya tsaga kankanar ... Ina nufin
kan mutumin.”
Sai na ji lakata ta sake. A
lokacin kaina yana hannunsa, yana aske ƙasan
haƃata, can wajen wuya, ina ganin sheƙin askar tasa. Sai na ji numfashina ya ɗauke.
Nan fa sai na yi ta maza, hankalina ya dawo, cikin natsuwa, na ce “Lalle wannan
ɗan’uwa
naka ya zama zakka a cikin danginku ...”
Ya karkato da rezar kan maƙoshina, cikin natsuwa, ya ce, “Gaskiyar lamari game da
danginmu shi ne, duk haka muke. Ni kaina wani lokaci nakan raya wasu abubuwan
ban mamaki a zuciyata, musamman lokacin kakar kankana. Ina mai tabbatar maka
cewa ɗan’uwan
nan nawa ba shi da laifi.”
Sai na ga wani haske kamar
na aska ya nufi maƙoshina,
har yana haska fuskar wanzamin. Na ce shike nan na mutu, sai na fara addu’a, na roƙi Allah ya kuƃutar da ni.
Sai na sadaukar kawai, na
rufe idona – babu nishaɗi a wannan lokacin – ina
jiran mutuwata kawai. Ban sake buɗe
idona ba sai da na ji yana yayyafa mini turare a fuskata, yana cewa, “Na yi
maka barka.”
Na tashi na karkaɗe
jikina, na ji ni kamar wani sabon zuwa duniya. Na biya shi, na yi waje. Na ji
yana kira a bayana, yana tunatar da ni batun ɗan’uwan
nasa kan yadda za a sake shi. Ban ko kula shi ba. Da na fito kan layi, sai na
ja wani dogon numfashi, na rantse cewa in dai lokacin kakar kankana ne, to ni
zan yi wa kaina aski, ko kuma dai ba zan sake zuwa aski wurin wannan wanzami
ba. (al-Hakim, 2008: 221 – 223).
A wannan labari na Azrael
Wanzam, za mu ga cewa an danganta shi wannan wanzamin da ciwon hauka wanda ya
sanya mutumin da ya a je aski shagonsa shiga wani matsancin hali. Za mu iya
cewa Allah ne kawai ya cece shi daga ciwon haukar Azrael don kaɗan
ya rage ya tsaga masa kai, kamar yadda ake tsaga kankana. Wannan ya tabbatar
cewa sana’ar wanzanci ta masu cikakken hankali ce, ba ta motsattsu ko mahaukata
tuburan ba. Tawfiƙ ya
yi wa Azarael barkwanci ne ƙila
saboda yanayin kayan aikin sana’ar
wanzanci, wato asake masu kaifin tsiya waɗanda
za su iya cutarwa. Bayan haka kuma, an san yadda mutum kan miƙa kansa baki ɗaya
ga wanzami yayin aski, wanda in har rana za ta ƃaci,
to fa ba tsimi ba tanadi, sai dai gyaran Allah. A taƙaice dai, sana’ar ta masu hankali ce da
natsuwa, kamar yadda Sallau (2010) ya nuna, ba ta irin su Azrael da Idi Wanzam
ba.
6.0
“IDI WANZAM” DAGA BAKIN SALISU MAKAHO, SA’IN MAKAFIN ZAZZAU
Idi Wanzam, kamar yadda
Salisu Sa’i ya nuna mana a waƙe,
mahakaci ne tuburan. Za mu iya tabbatar da hakan daga cikin abubuwan da mawaƙin ya faɗi
daga cikin ɗiyoyin waƙar
tasa da dama. A lokacin da Makaho ya nemi ko akwai wanzami a garin:
Da na sauka garin Gagawa,
Na ce jama’ar Gagawa,
Zan yi tambaya a gare ku,
Tambayata da wanzami a garin
nan?
Sai suka ce ‘To Malam,
‘Da wanzami a garin nan’.
Sai na ce ku kai ni wurinsa,
Don kuwa ina son aski,
Sannan ai mini gyaran fuska.
Jin haka, sai jama’ar Gagawa
sai suka gargaɗi Malam Makaho da cewa:
Shi wannan wanzamin,
Mu ma da ka gan mu ‘yan
garin nan,
Muna tsoronsa.
Wannan tsoro da suke ji na
Idi Wanzam ya nuna lallai da walakin: ko dai mafaɗaci
ne, ko kuma motsattse ne. ilai kuwa, ta tabbata motsattsen ne.
Dalilai da dama suka
tabbatar mana cewa Idi Wanzam motsattse ne. Na farko shi ne sunayen asakensa:
Askarsa guda huɗu,
kowace aska ga sunanta:
Ɗaya
‘Kura kya ci da gashi’,
Ɗaya
‘Ladanki na jikinki’,
Akwai wata ‘Wa aka samu?’,
Sannan ga ‘Кare dangi’.
Amma ita ‘Кare dangi’,
Idan ta fito daga sanho,
Rannan mutum dubu sa ƙare.
Sannan amfani da sanho
maimakon zabira domin adana asaken:
Wai wanzaman kiriki,
Suna yawo da zabira,
Idi Wanzam, shi sai ya zubo
askarsa a sanho.
Sannan shi Idi Wanzam wai
yana wasa aska a dutsen niƙa
maimakon mawashi na fata ko dutsen ƙanƙara:
Haba ‘yan amshi!
Wanzaman kirki,
Kowa yana da mawashin aska,
Idi Wanzam da dutsen niƙa yake wasawa,
Na Kwanar Gagawa,
Ko kuwa ya sami bulo na
siminti.
A tsarin likitanci na
gargajiya akan yi ƙaho.
Wajen yin ƙaho, akan yi amfani
da wani gyararren ƙaho
ne na dabba domin a zuƙo
mataccen jini. Shi mataccen jini ana samunsa ne a wurin da mutum ya ƙume, ko ya yi targaɗe da
ire-irensu. To shi Idi Wanzam maimakon ya yi amfani da ƙaho bisa al’ada, yana amfani fafaffiyar
garwa ce:
Subhanallahi!
Sannan wanzaman kirki,
Suna yawo da ƙaho,
Idi Wanzam, bakin garwa aka
fafe,
Majajjawa ita ce ‘yar kamu.
Ire-iren waɗannan
halaye duk suna nuni da cewa lallai Idi Wanzam motsattse ne. Yaya za a ce
asaken da yake yi wa mutane aski a ce har suna da sunaye na musamman, kuma
sunayen ma da ji salonsu ya nuna cewa masu shirin shan jini ne.
Wani tuntuƃe gushin gaba domin a tabbatar wa Malam
Makaho cewa lallai Idi Wanzam motsattse ne, shi ne yadda ya ƙi amsa sallamar da ya yi masa. A
maimakon ma ya amsa masa sallamar, sai ya daka masa tsawa:
Aka kai ni gidan wanzami,
To da na je gidan,
Na yi sallama na ƙara,
Na sake sallama na ƙara,
Ya yi shiru ya ƙyale.
To Idi Wanzami,
To daga can da ya motsa,
Sai ya daka mini tsawa!
Ran nan da na ruɗe,
Har igiyar wandona ta
tsinke,
‘Yan amshi suka tsorata,
Kan a jima sun kai Ɗanbatta,
Suka bar mu muna ta adanja.
Mutumin da za a yi masa
sallama, kuma yana ɗan Musulmi ya ƙi amsawa, a maimakon haka ma sai ya daka
tsawa ga mai yi masa sallamar, ai an san lallai bai da lafiyar ƙwaƙwalwa
sosai.
Haka kuma wata yarinya da ta
tarar da Malam Makaho yana jira a azure, ta ƙara
tabbatar da motsuwar Idi Wanzam, inda ta shawarci Makaho da ya kama gabansa:
Ka ji ina nan zaune,
Daga nan sai ga yarinya,
Ta ce, ‘Salamu alaikum,
Albishirinka Makaho,
Zan yi tambaya a gare ka.’
Subuhanallahi!
‘Wai me kake nema a gidan
nan’?
Na ce, ‘Yarinya ai na zo ne
ai mini aski’.
Ta ce, ‘Wa zai maka aski’?
Na ce, ‘Idi Wanzami’.
Sai na ji ta yi salati,
Ta ce ‘La’ilaha Illallahu,
kai dai baƙo ne a garin nan!
In kai baƙo ne,
Tashi in sa ka a hanya kan
Idi ya fito a gidan nan.’
Wani babban lamari kuma da
ya gudana tsakanin Malam Makaho da Idi Wanzam, da yake ƙara tabbatar da nuni a kan motsuwar
hankalinsa, shi ne na irin shirin da aka yi domin yin askin:
Ya ce, ‘To, tsaya Makaho, ni
askina sai an shirya’.
Na ce, ‘Shirin me za a yi
tun da dai na ba ka kirari’?
…………………………………………………….,
Idi Wanzami, sai ya fito a
gidansa,
Ya nemi ƙato goma,
Suka je suka samo dirka,
Nan suka zo suka jibge,
Ga igiya a gabansa,
Ita ma kamu saba’in ne,
Ya sa an haƙa rami,
Rami gaba bakwai aka tona,
Na ce, ‘Wanzami, duk wannan
ramin mene ne?’
Lallai irin wannan aski na
Idi Wanzam sai an shirya. A ce za a yi aski sai an saro dirka, kamar za a kafa
rumfa? Sannan ga igiya har kamu saba’in tare da haƙa rami gaba bakwai? Wannan ai ko raƙumi za a yanka iyaka ke nan.
7.0
KWATANCI
Idan aka lura da waɗannan
wanzamai guda biyu, za mu ga shi Azrael yana da ciwon hauka ne na gado, amma ba
lalle ne a gane hakan ba domin ba koyaushe haukar take tashi ba. Ba domin
wannan irin tattaunawa da ta faru tsakaninsa da wannan da ya yi wa aski ba, da
ba za a san da haukar tasa ba ma. Amma shi Idi Wanzam haukarsa a bayyane take
ga ‘yan garinsu da kuma sauran iyalansa ma. Kowa a garin ya san shi da cewa
mahaukaci ne.
Haukar Azrael ba ta tashi
sai da kaka ko lokacin bazara, lokacin da ake fama da ƙishi saboda zafi. Kuma a daidai wannan
lokacin ne kakar kankana. Saboda haka duk wani mai jin ƙishi yakan so ya sami kankana ya sha.
Wannan yanayin yakan sa Azarael ya ji kamar ya tsaga kan wanda yake wa aski da
nufin cewa kankana ce. Amma ita haukar Idi Wanzam hauka ce da ta ƙunshi tun daga kayan aikinsa zuwa
halayyarsa da mu’amalarsa.
A taƙaice dai Idi Wanzam mahaukaci ne
tuburan.
8.0
KAMMALAWA
Wannan maƙala ta yi ƙoƙarin nuna cewa barkwanci bai tsaya a
tsakanin masu sana’a a
junasu ko tsakanin wasu ƙabilu
ba. Akan ga jama’a
suna yi wa wata nau’in
sana’a ko masu aiwatar da sana’ar saboda wani dalili, amma
ba domin suna aiwatar da sana’a
kishiyar ɗayar ba. Wannan kuwa shi ya faru a kan
wanzamai kamar yadda muka gani.
Maƙalar ta nuna cewa kila saboda mu’amala da wanzami yake yi da
kayan kaifi irin su aska da ƙaho,
ga shi kuma riƙe da kan mutum da
wuyansa da duk dai inda in har rana ta ɓaci,
zai iya kai mutum ƙiyama
lokaci ƙanƙane,
shi ya sa ake yi masa wannan irin barkwanci.
Maƙalar ta nuna cewa irin barkwancin da ake
yi wa wanzamai ba a ƙasar
Hausa kawai ake yi ba, har da ma ƙasashen
Larabawa, kamar Masar da kuma sauran wurare. Wasu suna ganin cewa in kana neman
labarin gari, to ka tambayi wanzami. Kila wannan magana ba ta zama sharri ba.
Manazarta
Habib, A, Musa, U.I, da
Zarruƙ, R.M. (1988). Zaman Hausawa, bugu na biyu. Lagos: Islamic Publications Bureau.
Ibrahim, U. (2011). “Tasirin
Haye a Sana’o’in Hausawa na Gargajiya.” Kundin Digiri na Tsakiya. Kano: Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Johnson-Daɓies,
D. (Ed.) (2008). The Essential Tawfiƙ al-Hakim, play, fiction, autobiography. Cairo: the
American University in Cairo Press.
Karofi, D.S. (1980).
“Mabarata: Nazarinsu da Gudunmuwarsu a kan Adabin Hausa.” Digirin Farko,
Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria.
Sallau, B.A.S. (2000).
“Wanzanci: Matsayinsa na Al’ada da Sana’a a Кasar Hausa.” Kundin Digiri na
Tsakiya. Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Sallau, B.A.S. (2009).
“Sana’ar Wanzanci da Sauye-sauyen Zamani Jiya da Yau.” Kundin Digiri na Кoli.
Kano: Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero.
Sallau, B.A.S. (2010). Wanzanci da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa.
Kaduna: M.A. Najiu Professional Printers.
Sallau, B.A.S. (2013). Wanzanci da Sauye-Sauyen Zamani. Zaria:
Ahmadu Bello University Press.
Sallau, B.A.S. (2009). Maganai a Sha a Yi Wanka a Buwaya. Kaduna: M.A. Najiu Professional Printers.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.