Citation: Akilu Suleiman Bashir (2017). Gudummuwar Waƙoƙin Siyasa Wajen Tallata ‘Yan Takara A Jihar Taraba: Misalai Daga Waƙoƙin Shu’aibu Ibrahim Muhammad Aska. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Vol. 5. Department of African Languages and Linguistics, Yobe State University, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
GUDUMMUWAR
WAƘOƘIN
SIYASA WAJEN TALLATA ‘YAN TAKARA A JIHAR TARABA: MISALAI DAGA WAƘOƘIN
SHU’AIBU IBRAHIM MUHAMMAD ASKA
Akilu
Suleiman Bashir
TSAƘURE
Siyasa
wata aba ce da ta jiɓinci rayuwar al’umma ta duniya, kuma ta
yi tasirin gaske cikin jininsu. Don haka, marubuta waƙoƙin
Hausa suke dubin irin wannan tasirin da siyasa take ɗarsawa
cikin al’umma ga rayuwarsu ta yau da kullum musamman a Jihar Taraba. Ganin
haka, ya sa mawaƙan
suka duƙufa wajen yin rubutattun waƙoƙin
da nufin tallata ‘yan takara da jam’iyyun siyasa ga jama’ar da suke cikinsu
dangane da muhimmancin shiga jam’iyya da kuma zaɓen shugabanni nagari. Takardar za ta zaƙulo gudummuwar da marubuta waƙoƙin
siyasa suke badawa wajen tallata ‘yan takara da kuma jam’iyya.
ABSTRACT
Politics
is an issue that affects people’s life with profound impact. Because of this,
Hausa poet therefore relate the impact of this politics on society in their ɓarious
songs. In doing this, lots of them compose song to popularize politicians and
their parties because of its importance in electing better leaders. The aim of
this paper is to eɗamine the role of political poetry
during election campaigns with particular reference to Taraba State: Eɗamples
from poems of Shu’aibu Ibrahim Muhammad Aska.
KEYWORDS: Gudummuwa, Siyasa,
Tallata, ‘Yan takara, Taraba
1.0
GABATARWA
Waƙoƙin siyasa waƙoƙi ne da suka sha nazari a hannun malamai da ɗalibai masu
nazarin adabin Hausa.An sami ayyuka da dama ta wannan ɓangaren. Daga
cikin waɗannan ayyuka
akwai Hiskett (1977), da Birniwa (1987), da Funtua (2003), da Ɗangulbi (2003), da Yahaya (2010), da Ɗan ‘illela (2010), da Adamu (2012), da Dunfawa
(2013) da ma wasu. Malamai sun kawo ma’anar siyasa a cikin ayyukan da tarihin
kafuwar jam’iyyun siyasa da nazarin waƙoƙin siyasa dangane sa jigoginsu da salonsu da irin
gudummuwarsu ga kafuwar dimokuraɗiya. A wannan takarda za a dubi wani muhimmin salo
ne a wasu waƙoƙin Shu’aibu Ibrahim Muhammad Aska. Wannan salon kuwa
shi ne yadda mawaƙin ya yi amfani da kwantar da harshe ko mu ce daɗin baki wajen
tallata wasu ‘yan takara ga talakawan jihar Taraba wajen ganin sun zaɓe su.
Akwai dabaru da salailai
masu yawa da mawaƙan
siyasakan yi amfani da su waɗanda suke ba da gagarumar
gudummuwa wajen tallata ‘yan takara a lokacin yaƙin
neman zaɓen
waɗanda
suke yi wa waƙa Dunfawa (2013)
Wannan takarda an ɗora
ta ne kan ra’in Dunfawa (2013) wanda ya gabatar a kan waƙoƙin
siyasa tare da duba salailan cikinsu. Wannan ne aka yi amfani da shi wajen fito
da dabarun tallata ‘yan takara kamar yadda za a gani, amma misalai daga wasu waƙoƙin
siyasa na Shu’aibu Ibrahim Muhammad Aska.
1.1
TAƘAITACCEN TARIHIN RAYUWAR SHU’AIBU
IBRAHIM MUHAMMAD ASKA
An haifi Shu’aibu Ibrahim
Muhammad Aska a ranar 16/10/1972, a ƙaramar
hukumar Lau da ke jihar Taraba. Ya yi karatun allo a wurin mahaifinsa Malam
Muhammad a cikin garin Lau dake ƙaramar
hukumar Lau.Ya yi Makarantar Firamare a Central
Primary School Lau daga shekara ta 1980-1986.Shu’aibu bai yi ƙasa a guiwa ba, ya halarci Makarantar
koyon sana’a (Ɓocational
Training Centre) dakeƙaramar
hukumar Ganye da ke jihar Adamawa daga 1986 zuwa 1991.
Ya shiga harkar rubuta waƙoƙin
Hausa a shekara ta 2000 har zuwa yau 2017.Ya yi waƙoƙi da
dama da suka danganci faɗakarwa, da ilmantarwa. Bai
tsaya a nan ba, ya yi waƙoƙin nishaɗantarwa,
kamar soyayya. Har ila yau ya yi wa kamfanoni da ma’aikatu, da ƙungiyoyi na gwamnati da hukumomi da ba
na gwamnati ba (NGO) waƙa.
Bai tsaya a nan ba ya yi waƙoƙin siyasa da dama waɗanda
jimilarsu a taƙaice za su kai ɗari
da hamsin (150).
Ya yi waƙoƙi
masu yawa da suka haɗa da: na sarauta da kafofin
yaɗa
labarai (Media) kamar su Muryar Amurka (ƁOA)
da Rediyo Faransa da wasu da dama a nan gida Najeriya. Shu’aibu na da mata biyu
da ‘ya’ya bakwai.
1.2 MA’ANAR TALLATAWA/TALLA
CNHN,
(2006) ya bayyana ma’anar talla ta lugga ta fuskoki uku kamar haka:
Yawo
da kaya don sayarwa.
Rubuta
bayanin wani abu a jaridu, ko maƙala takardu a
bango ko jikin wani abu, don neman mai saye.
Bayyana
sirrin wani.
Ɗangulbi (2003)
Tallatawa na nufin wayar wa jama’akai a kan wani abu da ake buƙatar su saye ko su aminta da shi. Watau talla a
cikin waƙoƙin siyasa ita ce a fitar da jam’iyya fili da
kyawawan manufofinta don mutane su so ta.
Dunfawa
(2013) ya bayyana ma’anar tallatawa da dabara ce ta fito da kyawawan manufofi
da zummar wayar wa al’umma kai akan abin da ake buƙata su aminta da shi.
Saboda
haka marubuta waƙoƙin siyasa suna taka gagarumar rawa wajen cusa wa
mutane son jam’iyyunsu baki-rai-baki-fama. A cikin wannan tallarce suke kawo
sunayen wasu mashahuran mutane da aka san su da adalci da riƙon amana da kuma yin tsaye ga ƙwato wa talakan ƙasa yancinsa
da haƙƙinsa a duk lokacin da aka ba su dama ta hanyar zaɓensu a muƙaman siyasa. Ambaton sunayen irin waɗannan
shugabanni a cikin waƙa yana sa talakawa ko jama’a su rungumi jam’iyya.
Mawaƙan siyasa sukan dubi irin alheri ko kyauta da mutane
ke yi wa talakawa da maƙwabtansu sai su ambace su cikin masu kyawawan ɗabi’u da
halaye na kirki da ake son kowane ɗan siyasa ya kasance yana da su. Don haka da waɗannan ɗabi’u na kirki
ne mawaƙan za su tallata waɗannan mutane har jama’a su zaɓe su a
majalisu daban-daban.
Har
ila yau marubata waƙoƙin siyasa na tallata jam’iyyu da ‘ya’yan jam’iyunsu
dangane da ƙwarewarsu ga aikin hukuma ko wajen hulɗa da ƙasashen waje da sauran harkoki na kasuwanci. Ta
hanyar wannan tallar ɗabi’u da ƙwarewa ga
sha’anin mulki na wasu shugabanni da ‘ya’yan jam’iyyu ke sa mutane su shiga
jam’iyyu daban-daban.
1.3 DAƊIN BAKI
Daɗin
baki na nufin a faɗa wa wani magana mai faranta
masa rai domin samun wata biyan buƙata
daga gare shi koda kuwa maganar ba gaskiya ce ake faɗa
masa ba. Shu’aibuya yi amfani da irin waɗannan
salailan a cikin waƙoƙinsa don tallata wasu ‘yan takara ga
talakawan jihar Taraba. Daga cikin irin waɗannan
salailan da ya yi amfani da su akwai:kyaun hali dakyauta da iya mulki da
farin-jini da kawar da tsoro da buri/manufa. A kan waɗannan
ne wannan takarda za ta yi sharhi kamar yadda ya yi amfani da su cikin waƙoƙinsa
na siyasa.
1.3.1 KYAUN HALI
Kyaun hali shi ne kasancewar
mutum managarci.Da yawa mawaƙan
siyasa ke danganta kyaun hali ga wanda da suke yi wa waƙa ko da kuwa sun san baya da kyaun halin
domin su yi wa masu jefa ƙuri’a
daɗin
bakisu so shi kuma su zaɓe shi.
(Dunfawa,2013: 2)
Shu’aibu ya yi amfani da
wannan salon don tallata wata ‘yar takara a waƙarsa
mai taken “Maman Taraba Ta Iso”.Ga abin da ya cea wannan baiti:-
Adalci
sanin haƙƙin
jama’a sune ta sa a gaba,
Sannan
kuma da kare mutuncin kowa ba batun gaba,
Aisha
Alhassan da shiri ta taho domin ta kai mu gaba,
Mu
yunƙura duk mu ɗau
ƙuri’u musaka mata zata goya mu.
(bt, 8)
A wannan baitin mawallafin
na tallata ‘yar takarar ce dangane da kyawawan halayenta inda ya bayyana kaɗan
daga cikin halayen nata da suka haɗa da
baiwa talakawa haƙƙinsu,
da kare mutuncin kowa.
Mawallafin ya tallata wani ɗan
takarar a waƙarsa mai taken
“Taraba 2015 Gwamna Kai Muke Ƙauna”.Ga
abin da yake cewa danganeda kyawawan halayenɗan
takarar:-
Mai
farin-jinin Jama’a zuciyarsa farau ne,
Ga
al’umma shi ya ƙara
burge ni,
Taimako
da sada zumuncinsa ne ya ratsa ni,
Zuciyarsa
ba hassada dukkaninmu shaida ne.
(bt, 6)
A wannan baitin mawallafin
ya bayyana wasu kyawawan halayen wani ɗan
takarar kamar haka:mutum ne mai taimako da sada zumunci marar hassada.
Don haka duk wanda ya ji an
ambaci waɗannan kyawawan halaye ga wani zai ji
yana son sa. Mawaƙin
kan cusa irin wannan so ne a cikin zukatan mutane game da wanda yake yi wa waƙar. Abin na iya zama akasin abin da aka
faɗa,
shi dai burinsa kawai ɗan takarar ya sami karɓuwa
ga talakawa.
A baitukan da suka gabata an
ga yadda mawaƙin ya jingine waɗannan
kyawawan halayen ga waɗannan ‘yan takara da nufin
tallata su ga al’ummar jihar Taraba, don ganin sun sami karɓuwa.
Jingine waɗannan kyawawan halaye kan samar wa ‘yan
takaran soyayya da farin-jini gun talakawa, har ya kai ga su zaɓe su
a kujerun da suke takaran, haka kuma kyakkyawar dabara ce wajen tallata ‘yan
takaran ga talakawa.
1.3.2 KYAUTA
CNHN,
(2006) ya bayyana kyauta ta fuskoki guda biyu:
-Kyauta
bai wa mutum wani abu don ra’ayi ba tare da ya yi wani aiki ba.
-Kyauta
yin abin kirki ga wani.
Mawaƙan siyasakan yabi wani jigo ko ɗan takara ta
hanyar amfani da irin kyautar da yake yi wa jama’a, don su amince da shi kuma
su zaɓe shi.
Shu’aibu
yayi amfani da wannan dabarar ya tallata wani ɗan takara dangane da irin kyautar da yake yia waƙarsa mai taken “GwamnaTu O Sabin Taraba”. Ga abin da yake cewa a waɗannan
baitocin:-
Ga kyauta da son jama’a baba,
Zuciyarsa ba ta ɗagawa ba,
Sannan Baido bai gaji rowa ba,
Tausayinsa ke daɗa burge ni.
Mai kyauta ya sake ƙarawa,
Alkhairinsa bashi yankewa,
Ƙofofi yake ta
buɗewa,
Na arziƙi wajen
Ibadullah.
A Taraba martabarka ta ƙaru,
Kyautarka ta haɓaka ta ruru,
A zuciyarka talaka ta ƙaru,
Ai dole ‘yan uba su ƙyale ka.
(bt,
5,7,9)
A
waɗannan baitocin
mawallafin ya yi amfani da kyautar da wannan ɗan takara yake yi wa mutane ya tallata shi, ga ma
abin da yake cewa mai kyauta, da son jama’a, bai gaji rowa ba, mai kyauta ya
sake ƙarawa, alherinsa bai yankewa,kyautarsa ta haɓaka ta ruru,
son ka a wajen talakawa sai ƙaruwa yake yi.
Mawallafin
ya yi amfani da irin kyautar da Aisha Jummai take yi, ya tallata ta. Ga abin da
ya ce a waƙarsa mai taken “Twenty
Fifteen A Taraba ZaMu Ga Canji Sabo”
Mai haƙuri da tausayi
mai ƙaunar al’umma,
Ga fara’a da kyauta Aisha har da karama,
Akwai ta da ilimi na mulki a cikin al’umma,
Ga adalci ga tawakkaligun Allah mai girma.
(bt,
18)
A
wannan baiti mawallafin na ya bayyana ‘yar takarar ce dangane da halinta na haƙuri da ƙaunar al’umma
ga fara’a da kyauta.
Ambaton
waɗannan halayen
ga ɗan takara kan
sa ya sami tagomashi a wajen talakawa kuma ya dishe hasken abokan adawarsa.
1.3.3 FARIN -JINi
CNHN,
(2006) Farin-jini ƙaunar da mutum ko wani abu yakan samu a wurin
mutane.
Mawallafin
ya yi amfani da farin-jinin wata‘yar takara,ya tallata ta a waƙarsa mai taken “Twenty
FifteenA Taraba ZaMu Ga Canji Sabo” Ga abin da yake cewa a waɗannan baitoci:
Dukkan al’umman Taraba muna bayan ki,
Babu taraddadi ko shakka mune naki,
2015 randa zamu zo tarban ki,
Ƙoyinmu da
kwarkwata zamu fito domin ki Aisha.
Sarakai al’umma kowa ka ji sai zancen ki,
Har da ma’aikatanmu nagwamnati na ƙaunar ki,
Har yaranmu ‘yan makaranta sai begen ki,
Aisha Alhassan girgije inuwar alheriJummai.
(bt,
12, 13)
A
waɗannan baitocin
mawallafin na tallata ta ne dangane irin farin-jini da take da shi a wurin
talakawan jihar Taraba. Ga ma abin da yake cewa; dukkan al’ummar Taraba muna
bayan ki, babu shakka mune naki, ƙwanmu da
kwarkwata zamu fito domin ki.
Ya
ƙara da cewa sarakai, al’umma kowa sai zancen ki,
ma’aikatan gwamnati, da ‘yan makaranta na ƙaunar ki, yara
da ‘yan makaranta na begen ki.
Mawallafin
ya yi amfani da farin-jinin da wani ɗan takara yake da shi a wajen talakawa a ya tallata
shi a waƙarsa mai taken “GwamnaTu O Sabin Taraba”. Ga abin da mawallafin ke cewa a wannan baiti:-
Yau
dai Baido sai ka ƙara
godewa,
Ga
Allah ka ƙara
dagewa,
Masoyanka
basu ƙarewa,
Kullum
safiya akwai sabbi.
(bt, 11)
A
wannan baiti mawallafin na shaidawa ɗan takarar da ya godewa Allah ganin irin yadda
masoyansa kullum sai ƙaruwa suke yi.
Farin-jini
da ɗan takara ke
da shi a wajen al’umma kantaka muhimmiyar rawa wajen samar masa da tagomashi,
kuma ya sami karɓuwa na sosai da sosai, har ma ya kai ga ya sami ƙuri’un talakawan a lokacin zaɓe.
1.3.4 IYA MULKI
CNHN,
(2006) Mulki gudanar da harkokin hukuma kan jama’a. Mawallafa waƙoƙin siyasa kan tallata ɗan takara da suke yi wa waƙa ta fuskar iya mulki a wasu lokutan ma sukan nuna
babu wanda ya fi shi iya gudanar da mulki.
Shu’aibu
ya yi amfani da wannnan dabarar a waƙarsa mai taken
“Twenty FifteenA Taraba ZaMu Ga Canji
Sabo” wajen tallata wata ‘yar takarar. Ga abin da yake cewa a wannan baiti:-
Mu duba al’ummanmu Taraba mu yo talifi,
Aisha Alhassan mun san ta ba wani haufi,
A fannin mulki da siyasa ta riƙi kofi,
Zaku yi shaida lambar girma aka bata da yabawa.
(bt,
10)
A
wannan baiti mawallafin na bayyana iya mulkin ‘yar takarar ce wadda ya kai ga
ta sami lambar yabo. Ga abin da yake cewa Aisha Alhassan mun san ta ba wani
haufi, a fannin mulki na siyasa ta riƙi kofi, zaku
yi shaida lambar girma aka ba ta da yabawa.
Iya
mulki kyakkyawar hanya ce ta tallata ‘yan takara da mawaƙan siyasa kan yi amfani da shi wajen cusa wa
talakawa so, da ƙaunar wadda suke yi wa waƙa. Har ila yau wannan dabara kan sa ɗan takara ya
sami ƙima a wajen talakawa.
1.3.5 KAWARDA TSORO
Kawar da tsoro na nufin bawa
mutum tabbacin abu da yake tababa acikin zuciyarsa game da shi, idan wani yana
kifi-ido-kifi-bado game da yadda wani abu zai kasance, to akan kawar masa da
tsoro ta hanyar faɗa masa wasu batutuwa masu ba
shi tabbacin abin da yake tsoro da dukkan alama bazai faru ba.(Dunfawa 2013)
Mawallafin ya yi amfani da
wannan dabarar a waƙarsa
mai taken “Twenty FifteenATaraba Za
Mu Ga Canji Sabo”. Ga abin da yake cewa a wannan baiti:-
Ba
bambanci na ƙabila
ko addini,
Kowa
nasa ne a Taraba kowani fanni,
Hausawa,
Fulani da Mummuye kowani ƙarni,
Wurkum
har da Jenjo ga Junkun, Tiɓ kuma har ma Yarbawa.
(bt, 8)
Mawallafin yana kawar da
fargabanda talakawa jihar Taraba suke ji na ƙila
‘yar takarar zata nuna musu bambancin addini daƙabila.
Ya ci gaba da bayyana wa talakawan cewar bata da bambancin ƙabila, ko na addini, kowa nata ne a
jihar Taraba a kowani fanni yake.
An samimisalin kawar da
tsoro a waƙar mawallafin mai
taken “Maman Taraba Ta Iso”. Ga abin da yake cewa a waɗannan
baitoci:-
Na
ji ma’aikatanmu nagwamnati na wasu zantuka a gari,
Bayan
gwamnatin nan ta kau za su shige cikin haɗari,
Wa
zai ƙarfafa musu albashi balle kuɗin
garari,
Ai
ko na ce musu ga albishir Aisha hero ce.
Aisha
Alhassan ta ɗaura shiri domin kare haƙƙinku,
Zata
kula da ku tamkar ƙoyi
da biyan buƙatunku,
Albashinku
har da kuɗin hutu da sauran muradunku,
Ku
ɗunguma duk mu ɗauƙuri’u ku fito mu saka yaudara illa ce.
(bt, 13, 14)
A waɗannan
baitocin mawallafin ya kawar da tsoro da ma’aikatan gwamnati ke ji na faɗawa
cikin haɗari
na rashin ƙarfafa musu albashi,
da kuɗin
garari bayan shuɗewar wannan gwamnati.Don
haka mawallafin yakekawar musu wannan tsoron inda ya ce musu ga albishir Aisha
hero ce.
Mawallafin ƙara dacewa ‘yar takarar a shirye take
domin ta kare haƙƙinsu,da
kula da biyan buƙatunsuna
biyan albashi da zata yi har da basu kuɗinsu
na hutu.
Jin waɗannan
zantuttukakanƙarfafa wa talakawa
gwiwa da sakin jiki wajen zaɓen wacce aka tallata musu.
Kawar da tsoro makami ne na kare dange da ke taka muhimmiyar rawa wajen janyo
hankalin talakawa a lokacin neman zaɓe.
1.3.6 BURI/MANUFA
Buri
shi ne fatan da mutum yakan sa a ransa don cimma biyan buƙata a rayuwarsa. CNHN,(2006). Mawaƙan siyasa kan yi amfani da kyawawan burace-buracen
‘yan takaran da suke yi wa waƙa don tallata su a wajen talakawa don samun ƙuri’unsu a lokacin zaɓe.
Mawallafin
ya yi amfani da burin wata ‘yar takara ya tallata ta da shi a waƙarsa mai taken “Maman Taraba Ta Iso”. Ga abin da
yake cewa a waƙar:
Noma har da ruwa hanyar mota wannan muhimmi ne,
Ilimi, lafiya, haske na wuta wannan farilla ce,
Inganta harkar masana’antu wannan sahihi ne,
Wannan ɓangaren manufa neda ta fara shiryawa.
(bt,
12)
A
wannan baitin mawallafin ya bayyana kyawawan buri/manufofin ‘yar takarar ceidan
aka zaɓe ta ya ce
zata yi na inganta harkar noma, da samar da ruwan sha, da gina hanyoyin mota,
da samar da ilimi, da magunguna a asibitoci, da hasken wuta, da inganta
masana’antu. Duk wanda ya ji waɗannan kyawawan manufofi ko buri da aka zayyana zai
ji yana son wannan ‘yar takara.
Mawallafin
ya yi amfani da buri don tallata wani ɗan takara a waƙarsa mai taken
“U.T.C Muke So A Taraba 2015”. Ga abin da yake cewa a waɗannan baitocin
guda biyu:-
Alhaji Garba shi ne mutum mai kishinmu,
Shi burinsa shi ne mu kwana da ‘yancinmu,
Yai mana ayyuka ko’ina a Taraba,
Bai ware addininmu ko ko ƙabila ba.
Burinsa kullum Taraba mu zauna ƙalau,
Baya son ya ɗau tsegumin mabiya Jatau,
Baya zama da mai yaɗa gulma faufaufau,
Sabon Gwamna ba ya alaƙarsa da miyagu.
(bt,
5, 6)
A
waɗannan baitocin
mawallafin ya kawo kyawawan burin ɗan takaran na ganin talakawa sun zaɓe shi inda
yake cewa mutum ne mai kishinsu, wanda burinsa shi ne talakawa su kwana da
‘yancinsu, haka kuma zai yi ayyuka a ko’ina a jihar Taraba, bai ware wani
addini ko ƙabila ba. Zai samar da zaman lafiya a jihar Taraba
wanda Hausawa ke cewa ya fi zama ɗan Sarki. Babu ruwansa da sauraron tsegumi, baya
zama da magulmata da miyagu.
Mawallafin
ya yi amfani da wannan dabara na kyawawan buri ya tallata wata ‘yar takara a waƙarsa mai taken “Twenty
Fifteen A Taraba Za Mu Ga Canji Sabo”. Ga abin da yake cewa a wannan
baiti:-
Ba sauran zaman kashe wando gun al’umma,
Zamu zama kamar a ƙasar Turai don
ƙima,
Domin dogaro da ƙafafu babu
nadama,
Aisha Alhassan burinta ya zama lalaci ya ƙaura.
(bt,
20)
A
wannan baitin mawallafin ya shimfiɗo kyawawan ƙudurori da
wata ‘yar takara take da shi idan har an zaɓe ta.Inda yake cewa burinta shi ne, tasamar da
ayyukan yi ga matasa, ta gyara jihar Taraba ya zama kamar ƙasar Turai, zata samar wa jihar ƙima.Har ila yau yana daga cikin burin ‘yar takara ta
kau da lalaci a jihar Taraba.
Jin
waɗannan kyawawan
burace-burancenko manufofin ‘yan takara kan sa talakawa su so su, su zaɓe su idan
lokacin zaɓe ya zo. A nan ma za mu iya cewa buri/manufofin ‘yan
takara kyakkyawar hanya ce ta tallata ‘yan takaran.
1.4 KAMMALAWA
Bisa bayanan da suka gabata
an bayyana tallar ‘yan takara dabara ce da Shu’aibu ya yi amfani da ita wajen
fito da ƙimar ‘yan takara. An ga yadda ya yi
amfani da kyaun hali da kyauta da farin jini da iya mulki da kawar da tsoro da
buri/manufa, aka yi bayaninsu ta fuskar kwarzonta ‘yan takara a jam’iyya da
jama’arta.
Takardar ta fahimci mawaƙan siyasa sukan ja hankalin masu jefa ƙuri’a su zaɓi
‘yan takararsu da jam’iyyoyinsu. Don haka, abin da duk mawaƙin ya ambata a cikin waƙarsa dabara ce ta jawo hankalin talakawa
zuwa ga ɗan
takara ko jam’iyya. Dangane da haka dabarun nan da aka kawo suna da muhimmanci ƙwarai da gaske wajen tallata ‘yan takara
a lokacin yaƙin zaɓe a
jihar Taraba.
MANAZARTA
Adamu, A.I. (2012). “Salo da
Sarrafa Harshe A Cikin Wasu Waƙoƙin Jam’iyyun ANPP da P.D.P A Jihohin
Kano da Jigawa”. Kundin Digiri na Uku, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya da
Kimiyyar Harsuna Kano: Jami’ar Bayero.
Birniwa, H.A. (1987):
“Conserɓatismand
Dissent: A Comparatiɓe Study of NPC/NPN and
NEPU/PRP Hausa Politcal Ɓerse
From Circa 1946-1983” Ph.D Thesis, Department of Nigerian Languages. Sokoto:
Usmanu Ɗanfodiyo Uniɓersity.
Birniwa, H.A.(2004):
“Siffantawa a Cikin Waƙoƙin Siyasa”Ɗunɗaye
Journal of Hausa StudiesƁol.1.No.1
Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Birniwa, H.A.
(2005):“Tsintar Dami A Kala: Matsayin Karin Magana A Cikin Waƙoƙin
Siyasa” Maƙala da ta fito a
cikin Ɗunɗaye Journal of HausaStudies. Ɓol.1No.2 Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
CNHN, (2006):Ƙamusun Hausa.Kano:
Jami’ar Bayero.
Ɗan’ilela,
A. (2010). “Rubutattun Waƙoƙin Siyasa: Nazari A Kan Jihohin Sakkwato
da Kebbi da Zamfara”. Kundin Digiri Na Biyu Sashen Nazarin Harsunan Najeriya,
Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Ɗangulbi,
A.R (1996):“Habaici da Zambo a Cikin Waƙoƙin Baka na Hausa”. Makalar da aka
Gabatar a Taron Ƙara
wa Juna Sani, Kwalejin Ilimi ta Sakkwato.
Ɗangulbi,
A.R. (2003): “Siyasar Nijeriya: Gudummuwar Marubuta Waƙoƙin
Siyasa na Hausa Ga Kafa Dimokuraɗiyya
A Jumhuriya ta Huɗu, Zango na Farko”.Kundin
Digiri Na Biyu. Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.
Diso, A.H. (1997): “Zambo da
Yabo a Matsayin Dabarun Jawo Hankali a Cikin Rubutattun Waƙoƙin
Siyasa na Hausa”. Kundin Digiri Na Biyu, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya,
Kano: Jami’ar Bayero.
Diso, A.H. (2009):“Tsokaci Kan Rubutattun Waƙoƙin
Hausa”. Kano: Annuri Printing Press.
Dunfawa, A.A. (2013):
“Balmar Baka:Dabarun Jawo Hankalin Masu Jefa Ƙuri’a
A Cikin ‘Gaskiya Ba Ta Neman Ado’Ta Ibrahim Aminu Ɗandago”. A cikin Studies in Hausa Languages, Literature and Culture.Maƙala ce da aka Gabatar a 1st
National Conference, Center for the Study of Nigerian Languages, Kano:Bayero
Uniɓersity.
Funtua, A.I. (2003): “Waƙoƙin
Siyasa Na Hausa a Jamhuriya ta Uku: Yanaye-Yanayensu da Sigoginsu”. Kundin
Digiri na Biyu, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero..
Hiskett, M. (1977):“An Anthology of Hausa Political Ɓerse Teɗts” Edited And Annoted,
London: Uniɓersity of London SOAS.
Idris, Y. (2016):“Bijirewa a
Waƙoƙin
Siyasa: Bincike kan Waƙoƙin 1903-2015”. Kundin Digiri na Uku
Department of African Languages and Culture, Zaria: Ahmadu Bello Uniɓersity.
Yahaya, A. B. da Dunfawa,
A.A (2010): “Waƙar
Motar Siyasa:Saƙon
Talakawa Zuwa Ga ‘Yan Siyasar Zamani”Ɗunɗaye
Journal of Hausa Studies Ɓol.
1 no. 3 Dec Published and Printed in Nigeria by The Department of Nigerian
Languages, Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo
Uniɓersity.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.