Citation: Musa Muhammad CHIROMARI (2020). Sigogin Adon Harshe a Wasu Waƙoƙin Siyasa Na Kamilu Hussaini Nguru. Yobe Journal of Language, Literature and Culture (YOJOLLAC), Ɓol. .8 Department of African Languages and Linguistics, Yobe State Uniɓersity, Damaturu, Nigeria. ISSN 2449-0660
SIGOGIN ADON HARSHE A WASU WAƘOƘIN
SIYASA NA KAMILU HUSSAINI NGURU
Musa
Muhammad CHIROMARI
Tsakure
Wannan takarda ta yi nazari ne a kan amfani da adon harshe a waƙoƙin siyasa na Kamilu Hussaini Nguru. Saboda haka, maƙasudin gudanar da bincike shi ne nazari a kan waɗannan waƙoƙi don gano hikimar da ke tattare da amfani da adon harshen da kuma amfanin yin hakan a cikin waƙoƙinsa. Domin gano hakan ne muka yi amfani da ra’in Gusau (2003). A hanyoyin tattara bayanai kuwa an yi amfani da hira da sauraron waƙoƙin tare da juyarsu, an kuma yi zaiyarce-ziyarce. Sannan a yayin binciken an gano cewa wannan mawaƙi lallai ya yi amfani da adon harshe sosai, waɗanda suka haɗa da kamantawa, siffantawa, jinsintarwa, alamtarwa, ƙarangiya da kuma kinaya. Har wayau na daga cikin dalilan amfani da wannan salo ga mawaƙin, kamar yadda muka gano, shi ne bayyana hoto, ƙiyasi, ba da haushi, kambamawa da ƙara wa waƙa armashi da karsashi wajen masu sauraro.
1.0 Gabatarwa
Masana irin su; Gusau
(2008) da Yahaya da wasu (2007) da Ɗangambo (2007) da
Abba da Zulyadaini (2000) da ma wasu masana sun bayyana cewa waƙoƙin baka na Hausa sun
daɗe da faruwa, tun kafin
zuwan addinin Musulunci ƙasar Hausa. Kuma har ya zuwa yanzu ana aiwatar da wannan
fasaha ta baka. Duk da canje-canje da zamani kan haifar, waƙa a wajen al’ummar
Hausawa bunƙasa da inganta da sha’awa ta samu a ƙasar Hausa. Shi kuma
adon harshe masana irinsu; Gusau (2003) da Yahaya (1995) da Dija (1997) sun
bayyana cewa wata dabara ce da ake yi wa harshen waƙa ko furuci kwalliya
domin ƙara mata armashi da daɗi. Wani lokaci kuma yakan zama ma’auni da
gwada hikimar zance da balagar da Ɗan-adam yake da ita
domin burge mai sauraro. Ita wannan takarda an gabatar da ita ne a kan Sigogin
Adon Harshe a wasu Waƙoƙin Siyasa na Kamilu Hussaini Nguru.
An haifi Kamilu a
wani ƙauye da ake kira Beta, da ke ƙaramar hukumar
Sumaila ta jihar Kano a shekarar 1980. An kai shi karatun Allo wajen malaminsa
mai suna Sani Dogon Kwari a garin Nguru na Jihar Yobe tun yana ɗan shekara huɗu da haifuwa, kana
daga bisani iyayensa suka ƙauro garin na Nguru. Yanzu yana zaune
a unguwar Hausari Zangon Kanwa a garin Nguru. Ya fara waƙa a shekara ta 2008,
ya shahara a fannin waƙoƙin da suka shafi siyasa a Jihar Yobe da ma wasu jihohi na
Arewacin Nijeriya. Mawaƙin ya yi waƙoƙi da dama kuma waƙoƙinsa na siyasa ne
Chiromari (2013).
2.0 Ra’in Bincike
A wannan takarda an
yi amfani da ra’in Gusau (2003); wannan ra’i ya yi bayani a kan irin hanyoyin
da za a bi don gudanar da nazarin waƙar baka ta Hausa.
Masanin ya yi bayani ne a kan yadda adon harshe yake tare da kawo sassansa da
kuma yadda za a nazarce su. Wannan kuma shi ne abin da za a binciko a wannan
takarda.
3.0 Adon Harshe a Waƙoƙin
Kamilu Hussaini Nguru
Harshen Hausa ma,
kamar sauran harsuna yana cike da adonta harshe. Saboda haka, waƙoƙin mawaƙa da makaɗan baka na Hausa,
cike suke da irin wannan dabara domin isar da saƙontsu cikin salo mai
armashi da burgewa tare da ƙawatarwa. Sannan adon harshe yana da
sassa da dama waɗanda suka haɗa da: kamantawa da
siffantawa da jinsintarwa da kinaya da ƙarangiya da kuma
alamtarwa, ga misalansu daga cikin waƙoƙin. Dangane da haka
Kamilu Hussaini Nguru ma ba a bar shi a baya ba wajen amfani da adon harshe don
ƙawata
waƙoƙinsa ga masu sauraro
da waɗanda yake yi domin
su. kamar yadda za mu gani a bayanan da ke biye:
3.1 Kamantawa
Gusau (2003, sh.55),
ya bayyana kamantawa da cewa “Dabara ce wadda ake kwatanta abubuwa biyu dangane
da wasu darajoji da za su iya zama na daidaito ko na fifiko ko kuma na kashi”.
Ana amfani da wasu kalmomi da ke nuna kamance a fili da ake kira kalmomin
kamantawa ko kalmomin tsakani. Misali, kamar da ca kake da tamkar da awa da
kama da sai ka ce da daidai da bai kai da wadda ya wuce da I kaza da gaza da
wane da fi da makamantan waɗannan kalmomi da yawa. Kamantawa tana iya zama kamantawar
daidaito ko fifiko ko kuma ta kashi.
3.1.1 Kamantawa Ta Daidaito
A kamantawar
daidaito, kamar yadda sunan ya nuna, mizanin kan bayyana daidaituwar abu da ta
wani abu daban. Wato kamanta abubuwa masu daraja iri guda. Misali waƙarsa ta Ali Idris
Diginsa yana cewa:
Jagora :Shi rowan
shayin ga akwai zafi mu mun ƙyale shi ya ɗau sanyi,
:Ahmad burgun dutse
gwamna mu mun gode maka sai mun yi,
:Wancan Difitin ba ya
ƙyauta
mu ya ƙyale mu kamar bayi,
(Nguru, K. H; Waƙar. Ali Idris
Diginsa).
A wannan gunduwa da
ta gabata ya yi kamantawa ta daidaito a inda ya kamanta kansu da bayi sanadiyar
rashin kulawa da yake cewa Difiti ya musu. Kamar yadda mawaƙin ya nuna da su da
bayi daidai suke a wajen Difiti.
3.1.2 Kamantawa Ta Kashi
Mawaƙa suna amfani da
wannan dabara ce ta hanyar kwatanta abubuwa biyu sai a ƙasƙantar da guda, ta
yadda kowa ya saurara ya san cewa kaza ya gaza kaza. Misali:
Jagora Jirgin ruwa
komai linƙaya nina san bai
yi ya kifi ba
:Gaskiya a siyasa ba ƙarya Dan Idi ba su yi
kamar kai ba
:- - - - - - - - - - - - -
(Nguru, K. H; Waƙar, Ali Idris
Diginsa)
A wannan gunduwa mawaƙin ya ƙasƙantar da jirgin ruwa
ne yana nuna cewa komai iya linƙayarsa a ruwa bai kai kifi ba, a gaba
kuma yake ƙasƙantar da abokanan hamaiyar gwarzonsa da cewa a wajen yin
gaskiya ba su yi kamar shi ba.
Jagora :- - -
:Ahmad mun yadda batun tsere ɗan zomo bai yi barewa
ba.
(Nguru, K. H; Waƙar Ali Idris Diginsa)
A nan ma ya ƙasƙantar da ɗan zomo ne yana mai
nuna cewa idan batun gudu ake yi to bai kai barewa ba.
Amshi : Jaki bai fi
rago ba
: Ai idan daraja ake
nema
: Ali Ɗan Idirisa ke godiya
a wajen Allah maso bayi
(Nguru, K. H; Waƙar Ali Idris Diginsa)
A wannan waje da ya
gabatar ya ƙasƙantar da jaki ne inda yake nuna idan magana ta daraja ake
yi to rago ya fi jaki. Za mu gane haka ne yayin da muka duba matsayin rago na
daraja da yake da ita misali ta fuskar halaccin namansa da kuma matsayinsa a
layya ba kamar jaki ba.
3.1.3 Kamantawa Ta Fifiko
A wannan hanya a kan
kwatanta abubuwa biyu ne ta hanyar ɗora ɗaya bisa ɗaya. Wato a nuna abu kaza ya fi abu kaza.
Misali;
Jagora : Riɗi da gyaɗa akwai garɗi
: Soyayya ma akwai daɗi
: Shi mutunci wadda
ya fi kuɗi
-
- - -
(Nguru, K H; Waƙar Ali Idris
Diginsa).
A wannan gunduwa da
ta gabata mawaƙin yana nuna fifiko tsakanin mutunci da kuɗi.
Jagora :- - - - -
:Magana ta zumunci mai ƙarfi mata fannin haka
sun fi maza
:Ƙere-ƙere marar adadi
wannan sai an koma gun Turawa
(Nguru, K. H; Waƙar Ali Idri Diginsa)
A wannan waje mawaƙin yana nuna irin
fifikon da mata suka yi wa maza a ɓangaren sada zumunci, wato riƙo da zumunta a
tsakanin mutane.
3.2 Siffantawa
Ɗangambo (2007, sh.
43), ya bayyana siffantawa da cewa, “Siffantawa kamar kwatantawa ce, sai dai
ita kwatance ne na kai tsaye. A kan ɗauki darajar wani abu ko halayyarsa, a ɗora wa wani kai
tsaye, wato a ce ‘kaza’ ko kaza, kaza ne, shi ne kaza”. Siffantawa ta kasu
kashi biyu, wato gajeriya da doguwar siffantawa.
3.2.1 Gajeriyar Siffantawa
Gajeriyar siffantawa
kwatance ce ta falan ɗaya, wato sau ɗaya ake kwatanci. Ɗangambo (2007, sh.
44). Misali;
Jagora :- - - -
:Waƙar zan haɗa mahauta bangaru sai
aminan asali
:Indai mutum mahauci ne shi kara gare shi ba
shakku ba.
(Nguru, K. H; Waƙar Baba Machina)
A wannan waje mawaƙin ya siffanta
mahauta da halinsu na rashin jin tsoro ko shakkar mutum, idan abu ya haɗa ku sai dai idan
suna jin kunyarka su maka kara, ba wai don tsoro ba.
Jagora :Kun san tashi
sama sai tsuntsu,
: A ci zali ai dawa
sai kura
: A faɗa a cika ɗan Diginsa ya Ali mun
gode maka talakawa
(Nguru, K. H. waƙar Ali Idriss Diginsa).
A nan mawaƙin yana siffanta
tsuntsu ne da cewa tashi sama yake yi ba kamar dabba ba, ya kuma siffanta kura
da halinta na cin zali da kuma tsoro.
3.2.2 Doguwar Siffantawa
Ɗangambo (2007, sh.
44), ya bayyana doguwar siffantawa da cewa kwatantawa ce mai rassa mai yaɗo. Za a iya kiran ta
da hoto cikin bayani, wato idan aka siffanta abu tamkar ana nuna shi a hoto ne,
wani lokaci wadda ya ƙunshi kwatantawa. Misali:
Jagora :Masu Babura na acaɓa ku taso ku matsa
babur ku ma,
:Samu awa kashe wa minti sai ɗan acaɓa ƙarshen nema,
:Shi ɗan acaɓa babu ruwansa wajen tsegumi da zancen gulma,
:Laifinsa guda ɗai ya kai yara makaranta su tashi bai ɗauko ba.
(Nguru, K. H; Waƙar Baba Machina)
Mawaƙin yana siffanta ‘yan
acaɓa da halayyarsu na
matsa Babura da ƙoƙarin neman kuɗi, idan an samu kuma a kashe su a lokaci
guda. sannan ga halayensu na rashin tsegumi sakamakon koyaushe suna kan nema ga
kuma rashin zuwa ɗaukan yaran makaranta
a kan lokaci.
Jagora : Wani mai waƙarsu mai roƙo,
: Ka gano shi ciki
kamar baƙo,
: Jangwam-jangwam ya
miƙo,
: Wai nan mota yake
roƙo,
: Ko riga bai yi
canji ba.
(Nguru, K. H; Waƙar Malam Sani)
A wannan gunduwa mawaƙin yana bayyana
siffofin makaɗin jam’iyar da take
hamayya da jam’iyar da yake yi wa waƙa, yana nuna cewa ga
shi jangwam-jangwam wato a rame da yunwa a jikinsa, ta yaya wanda ba a ba shi
abinci ya ƙoshi ba har za a ba shi mota.
3.3 Jinsintarwa
Kamar yadda Gusau
(2003, sh. 59), ya bayyana jinsintarwa da cewa, “Dabara ce ta ɗaukar daraja ko sifa
ko hali ko yanayi ko aiki na wani jinsi a ba wa wani jinsi na daban”. Misali a ɗauki wata halayya da
jinsin da mutum kawai aka san shi da ita a ɗora wa jinsin dabba ko tsuntsu, kuma
jinsintarwa ta kasu zuwa; mutuntarwa da dabbantarwa da abutarwa.
3.3.1 Mutuntarwa
Abba da Zulyadaini
(2000, sh.122), sun bayyana mutuntarwa da cewa “Mawaƙa kan yi amfani da
wannan dabara ce ta hanyar ɗaukar wasu halaye ko siffofi ko wasu abu masu kama da
haka na Bil-Adam, sa’annan sai a lanƙaya su ga wani wanda
ba mutum ba”. Misali:
Jagora :Yau ga wawan kare za shi kwartanci har shimfiɗar kura,
:Amma da zuwansa sai na ga ya riƙe bindi yana ƙara,
:Kare cewa yake ni fa kwarto ne magana yake ƙarara,
:A tsugunne yana ta kuka yana ihunsa yana
kiran tuba.
(Nguru, K. H; Waƙar Adam Dala Dogo)
A wannan gunduwa mawaƙin yana ɗaukar siffar ɗan Adam ta magana da
kuma kwartanci yana danganta su da kare.
Jagora : In za ka ji gobe aboki na ka tuno dai gobe
akwai saura,
: Wai kare aka ba alƙalanci ai ƙaryar mage ta kai ƙara,
: Kuliya ta lalubi
lauyoyi a ciki na hangi akwai kura,
: Wannan shari’a za
ai rigima don na gane haka ɗan baiwa.
(Nguru, K. H. waƙar. Ali Idiss
Diginsa)
Idan aka duba wannan
gunduwa za a ga yadda mawaƙin ya ɗauki wasu ɗabi’u na ɗan Adam kamar alƙalanci da ɗaukar lauyoyi da ma
shari’ar kanta yana ɗaukan ɗabi’un yana nuna cewa
dabbobi sun yi.
3.3.2 Dabbantarwa
Abba da Zulyadaini
(2000, sh. 124), sun bayyana ma’anar dabbantarwa da cewa “Hanya ce da mawaƙa kan mayar da mutum
ko wani abu dabba. A irin wannan dabara akan kwatanta Bil-Adama da wasu halaye
ko siffofi irin na dabba”. Misali;
Jagora : - - - -
:Ga haziƙin gwamna ba mu yadda
da tinkiya ko jaki ba,
:Jaki uban gardama ka
fito ka ga haziƙin gwamna kai ma.
(Nguru, K. H; Waƙar Ɗan Tumba)
Mawaƙin ya dabbantar da
abokin takarar gwamnan jam’iyarsa, inda ya kira shi da jaki da tunkiya.
Jagora :Amadu Mirwa
wanda ake yayin sa a ko’ina sha nema
:Damo ne shi uban haƙuri Allah ya nufe shi
ba ya gulma
:Ya Amadu Jalla shi
ya naɗa ka muna bayanka
koyaushe ma
:Duk jama’a ku zo ga
mai ƙaunarmu ba za mu ɗau jaki ba.
(Nguru, K. H. waƙar Malam Sani)
Idan muka duba za mu
ga yadda mawaƙin ya dabbantar da gwaninsa ya lira shi da damo, domin
yta nuna cewa mutum ne mai haƙuri. Sannan ya dabbatar da wanda yake
yi wa habaici inda ya kira shi da jaki.
3.3.3 Abuntarwa
Abba da Zulyadaini
(2000, sh. 125), sun bayyana abutarwa da cewa “wata hikima ce da ake mayar da
mutum ko dabba ko tsuntsu ya zuwa wani abu marar rai”. Misali:
Jagora: : - - - -
:Jama’a duk sun faɗa ga Amadu Mirwa a
daina taɗin kowa,
:Ga naman saniya su ba za su ci naman kulɓa ko jaki ba.
(Nguru, K.H; Waƙar Amadu Mirwa)
A wannan waje ya
abutar da wanda yake zuga ya ce shi naman saniya ne domin ya nuna darajarsa a ɓangare guda kuma ya
abutar da abokan hamayyar gwaninsa da naman kulɓa da na jaki domin ya nuna ba abin so
ba ne ga jama’a.
Jagora : Allah ka ƙara salatin Annabi
Mustafa kogin adalci,
: Allah haɗa da Umar Usmanu
Aliyu ƙusa gatan benci,
: - - - -
(Nguru, K. H; waƙar Kun Ji Kunya ‘Yan
PDP)
Mawaƙin ya abutar da Aliyu
ne don ya nuna irin matsayinsa a wurin Manzon Allah (SWT) da kuma Musulunci,
domin ƙusa a benci aba ce mai matuƙar daraja da
muhimmanci.
3.4 Alamtarwa
Gusau (2003, sh. 60),
ya bayyana alamtarwa da cewa “Wata hanya ce da ake bayyana wani abu ta ba shi
wata alama da ta yi kama da shi dangane da shi ko yanayi ko ɗabi’a ko hali ko
jarunta ko ƙasaita da sauransu”. Wata alama ce da take wakiltar wata
manufa, musammam takan zamo madadin sunan abu. Misali;
Jagora :- - - - -
:Kafin na ce komai kowanku ya dakata ga farkon
shafi,
:Kun tabbata lokacin sanatan Ɗan Tumba dai ba mu
sha daɗi ba.
(Nguru, K. H; Waƙar Kun Ji Kunya ‘Yan
PDP)
Mawaƙin ya alamta kalmar
dan Tumba a matsayin alama da ke wakiltar sunan ɗan takarar jam’iyyar da take adawa da
tasu, wanda kuma tsohon sanata ne.
Jagora : Ina so na
lallaɓo na gaya muku ɓera gare ku masu
awaki,
: Ina da tambaya ina
fadawa ga wani can da shi da matar sarki,
: Buri yake yah au
ref don ya ci mu ya ba mu garin kwaki,
: ƙaryarka ta riga ta ƙare tun wuri ka zo da
ragon tuba,
(Nguru, K. H. waƙar Baba na Machina)
Mawaƙin ya alanta kalmar ƙwai a matsayin arziƙi, wato zama cikin
wadata da jin daɗi, sai kalmar garin
kwaki wacce take alama ta nuna talauci da yunwa.
3.5 Ƙarangiya
Gusau (2003, sh. 61),
ya bayyana ƙarangiya kamar haka “Dabara ce ta luguden harrufa ko
kalmomi ko wasa da harshe cikin baƙaƙe da kalmomi. Haka
kuma akan iya maimaita wata gaɓa ko ƙwayar sauti, sautinsu ya dinga tafiya
bai ɗaya a cikin kalmomi”.
Misali:
Jagora :Turmi ka ture kura ke kura ki tashi ture
turmi,
:Ƙarƙaballu kai da mulki
fam-fam-fam sai ka tada babban ƙaimi,
:- - - - -
(Nguru, K. H; Waƙar Baba Machina)
Jagora : Faɗar falala filin
Fulani farilla ban haka dan faɗa ba,
: Cire ciwo a cikin
cikin mai ciki cikas yake ka ji babba,
: Tunanin zancen
tuntuɓar tafiya ta ban taɓa tuntuɓe ba,
: Sayan sa don sarasi
sukuni sahihi sa a ce babba.
(Nguru; K. H. waƙar PDP rigar Ƙaya)
A waɗannan gunduwowi an ga
yadda mawaƙin ya nuna iya ƙwarewa a harshe, wato
yadda yake luguden kalmomi da haruffa masu sauti iri guda, inda a gunduwa ta farko
ya kawo kalmomin ‘turmi ture kura, kura ture turmi’, a gunduwa ta biyu kuma ya
kawo kalmomi masu sauti iri ɗaya waɗanda suka haɗa dal faɗar falala filin fulani farilla faɗa da kuma kalmomin
cire ciwo a cikin ciki mai ciki cikas da sayan sa sarari sukuni sahihi sa’a,
Wannan ya nuna fasaha da ƙwarewarsa a harshe.
3.6 Kinaya
Gusau (2003, sh. 60),
ya bayyana kinaya da cewa “Wata dabara ce ta sakaya zance wadda take juyar da
abu daga asalinsa wato ma’anarsa ta farko zuwa ga wata ma’ana ta biyu wato
sakayawa”.
Jagora :Ku ‘yan uwana
zan shiga waƙa kowa ya ji ba wai ba,
:Kuma gaskiya ce za ni faɗi ba wai gyara miya
ta ba,
:- - - - -
(Nguru, K. H; Waƙar Musa Gamcho)
A wannan gunduwa za a
ga yadda mawaƙin ya sakaya ma’anar kalmar gyara-miya wacce take nashe
da ma’anar fadanci ko faɗin son rai domin a so
mutum.
Jagora :Kai su o-o da
o-o ‘yan cuta,
: Bara fa jirgi za ya
ɗauka ta,
: Na zamo cikin
mahajjata,
: Ga suna na da lamba
ta,
:‘Yan uba ba su bar
ni tashi ba.
(Nguru, K.H Waƙar Malam Sani)
A wannan gunduwa da
ta gabata mawaƙin ya yi kinayar kalmar ‘yan uba wacce tana ɗauke da ma’anar maƙiya ko mahassada.
4.0 Kammalawa
Binciken ya nuna cewa
adon harshe yana da muhimmanci wajen kwatantawa da bayyana hoto cikin bayani da
ƙiyasi
da bayar da haushi da kuma kambamawa da sauransu. Adon harshe yana iya zama
tamkar gishiri a miya a cikin waƙoƙin baka na Hausa
domin yana ƙara wa waƙa zaƙi. Sannan adon harshe
yana tasiri wajen nazarin waƙar baka ta Hausa domin yana iya sa a
fahimci salo da kuma saƙon da mawaƙi yake son isarwa
cikin sauƙi. An kawo taƙaitaccen bayani akan
waƙar
baka da adon harshe tare da kawo tarihin Kamilu Hussaini Nguru da kuma ra’in da
aka yi amfani da shi a wannan takarda. Sannan an gabatar da misalai na adon
harshe tare da yin ƙarin bayani a kan su, a cikin waƙoƙin siyasa na Kamilu
Hussaini Nguru sannan an gabatar da bayanai a kan kowane ɓangare na adon harshe
da aka kawo a matsayin misali, waɗanda su ne aka gudanar da wannan takarda a
kansu.
Manazarta
Abba, M. da
Zulyadaini, B (2000), Nazari kan waƙar baka
ta Hausa.
Gaskiya Cooporation.
Chiromari, M. M
(2013), Adon Harshe a Waƙoƙin Baka na Hausa: Nazari a Wasu Waƙoƙin Siyasa na Kamilu
Hussaini Nguru. [Kundin Digiri na ɗaya]. Sashen Koyar da Hausa, Jami’ar Jihar
Yobe, Damaturu.
Dija, Ɗ. (1997), Nazarin
Adon Harshe a Cikin Wasu Ƙagaggun Labarai na Hausa. [Kundin Digiri na Biyu]. Sashen
Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano.
Ɗangambo, A (2007), Ɗaurayar gadon feɗe waƙa (Sabon Tsari).
Triumph
Gusau, S. M. (2003). Jagoran nazarin waƙar
baka.
Benchmark Publishers.
Gusau, S. M. (2008). Dabarun nazarin adabin Hausa. Benchmark
Publishers.
Yahaya, A. B. (1995).
Siffantawa bazar mawaƙa: Wani saƙo cikin waƙa. A cikin A. U.
Kafin Husa, A. Y. Bichi & L. D. Yalwa (edc.). Studies in Hausa Language, Literature and Culture. The Fifth Hausa
International Conference. Benchmark Publishers
Yahaya, da wasu
(2007). Darrussan Hausa 1 don manyan
makarantun sakadare. Uniɓersity Press.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.