𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Malam, mahaifiya ce ta ce za ta tsine ma ɗanta in bai saki matarsa ba. To, idan ya sake ta a kan haka sakin ya yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
W Alkm Slm W Rhmtul Laah.
Malamai sun yarda cewa sakin
wanda aka tilasta shi a kan sakin ba ya aukuwa, saboda hadisin Annabi (Sallal
Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) wanda Al-Imaam Ibn Maajah (2045) ya riwaito
kuma Al-Albaaniy a cikin Sahih Al-Jaami’ (1836) ya inganta shi cewa:
« إِنَّ اللَّهَ تَجَاوَزَ عَنْ أُمَّتِى الْخَطَأَ ، وَالنِّسْيَانَ ، وَمَا اسْتُكْرِهُوا عَلَيْهِ »
Haƙiƙa
Allaah ya yafe wa al’ummata
kuskure da mantuwa da abin da aka tilasta su a kan sa.
Wannan maganar kuma ita ce
gaskiya in shaa’al Laah, domin ko ba komai wanda aka takura wa ba sakin ya yi
nufi ba. Ya dai yi nufin kauce wa cutar kisa ko salwantar wata gaɓa ko
asarar dukiya ko ɗauri ne kawai.
Amma kuma malamai sun sanya
sharuɗɗan
da sai an cika su kafin a ce saki ya zama na wanda aka tilasta masa:
1. Ya zama tilascin ta
fuskar zalunci ne a gare shi, amma ba kamar wanda yake cutar da matarsa kuma
don haka alƙali ya tilasta masa
ya sake ta ba.
2. Ban da kamar wanda matar
take hana shi sauke haƙƙoƙin addini kamar sallah da azumi, idan
iyaye suka tilasta shi ya sake ta. Wannan ma ba tilasci ba ne.
3. Ya zama tilascin daga
wani mai ikon sarauta ko wani azzalumi ne a kansa, kamar wani ɗan
fashi ko mai garkuwa da mutane.
4. Ya zama shi yana da
marinjayin zato a kan cewa mai sarautan ko azzalumin zai zartar da barazanar da
ya yi masa idan bai saki matar ba.
5. Ya zama abin da za a
zarta masa wani abu ne da zai cutu da shi cutarwa mai girma, kamar kisa ko duka
mai tsanani ko ɗauri ko tsarewa na tsawon
lokaci.
6. Amma zagi ko tsinuwa ko ƙwace wani abu kaɗan
na dukiyarsa, da sauran makamantansu duk ba tilasci ba ne. (Tamaamul Minnah:
3/146-7)
Don haka, barazanar tsinuwa
daga mahaifiya bai isa ya zama tilasci ba a gare shi. Kuma ko da ya saki
matarsa a kan haka, sakin bai tabbata ba.
Sai dai ko in ta kafa hujja
a kan hakan ne da cewa: Matar tana hana mijin nata tsai da addini ne kamar zuwa
sallah a kan lokaci saɓanin yadda yake kafin ya
aure ta, kuma an rasa hanyar hana ta hakan sai ta hanyar sakin. A nan idan ta
tilasta shi ya sake ta daidai ne, kuma sakin ya tabbata, saboda shahararriyar
nan ta ƙissar Ibn Umar (Radiyal Laahu Anhumaa).
Allaah ya ƙara mana fahimta.
WALLAHU A'ALAM
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.