𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Mal. Barka da yau da fatan kana lafiya. Tambayata ita ce shin idan mutum ya rabu da matarshi sannan akwai 'ya'ya tsakaninsu shin wa keda hakkin rike yaran domin kula da tarbiyarsu? Bayan haka ita matar ta yi aure sannan shi miji bai gamsu da yana yin natsuwarta ba. Na gode. a huta lfy.
HAƘƘIN
RIƘON YARO BAYAN RABUWAR AURE
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa
rahmatullah.
Shi hakkin rikon yaro bayan
rabuwar aure yana wuyan mahaifiyar yaron ne, mutukar dai ba'a samu wata
matsalar da za ta hana ita uwar ɗaukar
dawainiyar kulawa da yaron ba.
Dalilin da yasa ake fara
gabatar da uwa fiye da uban yaro awannan matakin saboda ita uwa tafi uban yaro
sanin halayensa da kuma hanyar da za ta bi wajen tarbiyyantar da yaron bisa
kyawawar dabi'a.
Kuma ita uwa tafi uban yaro
nuna tausayi da tausasawa da soyayya da haƙuri
da juriya wajen ɗaukar wahalhalun kulawa da
rayuwar yaro. Misali kamar irinsu wanka da wanki da ɗaukar
yaro zuwa duk inda zataje.
Sayyiduna Abdullahi bn Amr
bn Al aas (Allah ya yarda dasu) ya ruwaito cewa "Wata mata tazo wajen
Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam sai ta ce masa "Ya Rasulallahi
wannan yarona ne. Cikina ya kasance shi ne wajen ɗaukarsa
(Madaukinsa) Kan cinyata ya kasance shi ne matattarinsa, kuma nonona ya kasance
shi ne abin shansa, amma yanzu kuma mahaifinsa (wato mijina wanda muka rabu) ya
zo yana raya cewar zai kwaceshi daga gareni". Sai Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam ya ce mata "ke kika fi chanchanta da rikeshi, mutukar
bakiyi aure ba". Imamu Ahmad da Abu Dawud da Baihaƙiy da Hakim ne suka ruwaitoshi.
Amma akwai sharudan da
shari'a ta shimfida kafin ita kanta uwar ta chanchanta da rikon yaron. Daga
cikin sharudan nan akwai:
1. HANKALI: Matar da ta samu
taɓuwar
hankali bata chanchanta a bar mata rikon yaro ko yara ba.
2. IKON BAYAR DA TARBIYYAH:
Idan uwar ta kasance ita kanta bata da tarbiyyah, to bata chanchanta da rikon
yaro ba, domin ita kanta bata da tarbiyyah ballantana har ta bayar.
3. RIKON AMANA DA KYAWUN
HALAYE: Idan ta kasance fasiƙa ko
barauniya, ko mai bayyanar da ayyukan saɓon
Allah, to bata chanchanta abar mata rikon yaro ba.
4. MUSULUNCI: mafiya
rinjayen maluman musulunci sun tafi akan cewa bai halatta abar wa mace kafira
tarbiyyar yaro Ƙarami
ba.
5. 'YANCI: Bai halatta ga
mace baiwa ta rike yaro Ƙarami
ba, saboda rashin isassun lokutan kulawa da rayuwar yaron.
6. RASHIN YIN AURE: Idan ta
yi aure to shikenan hakkin kulawa da yaron ya faɗi
daga kanta.
Idan ta kasance kamar yadda
ka faɗa
cewar baka gamsu da yana yin tatbiyyarta ba, to abin da ya fi dacewa shi ne
abar yaron akarkashin kulawar kakarsa ta ɓangaren
uwa, ko 'yar uwar mahaifiyar yaron.
WALLAHU A'ALAM.
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta
Links ɗin
mu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
HAƘƘIN RIƘON YARO BAYAN RABUWAR AURE
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh.
Asalin hukuncin shari’a shi ne:
1. UWA ce ke da haƙƙin riƙon yaro bayan saki
Idan an rabu da aure, uwar yaro ita ce tafi cancanta ta riƙe
shi domin kula da shi, saboda:
• ita ce tafi sanin halayen yaron,
• ita ce tafi tausayi, haƙuri, juriya da iya tarbiyya,
• ita ce tafi jiran wahala da hidimar yaro.
Manzon Allah ﷺ
ya yi hukunci ga wata mata cewa:
“Ke kika fi cancantar rikeshi muddin baki yi aure ba.”
(Imam Ahmad, Abu Dawud)
2. Amma akwai sharuɗɗan da dole uwa ta cika kafin ta samu
wannan haƙƙi
(a) Ta kasance mai cikakken hankali
Idan akwai tabin hankali ko rashin daidaito, ba a ba ta
riƙon yaro.
(b) Ta kasance mai tarbiyya da kiyaye addini
Wadda ba ta da tarbiyya ko mai bayyanar da fiskanci ba ta
cancanta.
(c) Ta kasance amintacciya ce
Ba mai barna, sata, lalata da sauransu.
(d) Ta kasance Musulma ce
Malamai da dama sun ce ba a barin yaro ƙarami a hannun
kafira idan uban Musulmi ne.
(e) Ba ta yi aure ba
Idan ta sake aure – kamar yadda ka ambata – da wannan haƙƙin
riƙon yaro ya fice daga hannunta, sai dai in mijin da ta aura ba zai cutar da
yaron ba ko zai yarda ya zauna da ita da yaron.
Yawancin malamai suna cewa aure na biyu yana ɗauke wa mace
haƙƙin riƙon yaro, saboda:
• sabon miji yawanci ba ya ƙaunar ɗaukar dawainiyar yaro ba
nasa ba,
• hakan yana iya haifar da cutuwa ga yaron ko rashin
tarbiyya.
3. To idan uwa ta yi aure kuma uban yaro bai yarda da
tarbiyyarta ba?
A irin wannan yanayi:
• uban yaro shi ya fi cancanta, idan yana iya tarbiyya da
kula da shi.
• Idan uban yana aiki ko ba shi da lokacin tarbiyya, to
kakarsa ta ɓangaren uwa ko ’yar uwar mahaifiyar yaron su ne suka fi cancanta.
Saboda su sun fi kusa da yaron, kuma basa cutar da halinsa.
KARSHEN HUKUNCI
A matsayinka na uba:
• idan matar ka ta sake aure ta rasa haƙƙin riƙo,
• idan kuma kai baka yarda da tarbiyyar sabon mijinta ba, to
yana cikin haƙƙinka ka karɓi riƙon yaron, bisa shari’a.
Amma dole ka tabbata:
• zaka iya kula da yaron,
• zaka bayar da tarbiyya ta gari,
• za ka ba shi kulawa, soyayya da nusarwa.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.