𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Ina sayar da kayan mata kamar na matsi da sauransu, sai aka ce wai ba kyau in sayar wa karuwa ko Kirista. Mene ne gaskiyar wannan?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Abin da take nufi da kayan
mata a nan shi ne ‘maganin mata.’ Wato maganin da mata suke amfani da shi domin
ƙara samun soyuwa a wurin mazajen
aurensu. Shi kuma maganin mata a fahimtarmu iri-iri ne:
1. Akwai wanda addini ya
hana kai-tsaye, kamar abin da malamai suka san shi da suna: At-Tiwalah. Shi ne
wanda Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ambata a cikin
maganarsa cewa:
إِنَّ الرُّقًى وَالتَّمَائِمَ وَالتِّوَلَةَ شِرْكٌ
Lallai Ar-Ruƙaa da At-Tamaa’im da At-Tiwalah duk
shirka ne! (Abu Daawud: 3883 da Ahmad: 3615 da Ibn Maajah: 3530 da Al-Haakim:
4/217 da Ibn Hibbaan: 1412 duk sun riwaito shi, kuma Al-Haakim da Az-Zahabiy da
Al-Albaaniy duk sun ce: Hadisi ne sahihi. Dubi Silsilah Sahihah: 1/584 a ƙarƙashin
hadisi na: 331).
Wurin fassara ma’anarsa ne
Sahabi Ibn Mas’ud (Radiyal Laahu Anhu) ya ce:
«شَيْءٌ يَصْنَعُهُ النِّسَاءُ يَتَحَبَّبْنَ إِلَى أَزْوَاجِهِنَّ»
Wani abu ne da mata suke
aikata shi, suna ƙara
soyuwa da shi a wurin mazajensu. (Sahih Ibn Hibbaan: 6090).
Shi kuma Ibn Al-Atheer (Rahimahul
Laah) cewa ya yi:
مَا يُحبّب الْمَرْأَةَ إِلَى زوْجها مِنَ السِّحْرِ وَغَيْرِهِ، جَعَلَهُ مِنَ الشِّرْكِ لِاعْتِقَادِهِمْ أَنَّ ذَلِكَ يُؤَثِّرُ ويَفْعل خِلَافَ مَا قَدَّرَهُ اللَّهُ تَعَالَى.
Abin da yake soyar da mace
ga mijinta ne, na sihiri ko waninsa. Ya sanya shi daga cikin sihiri ne domin
suna ƙudurce cewa shi ɗin
yana yin tasiri kuma yana aikata saɓanin
abin da Allaah Ta’aala ya ƙaddara.
(An-Nihaayah: 1/200).
Wannan nau’in shi ne sananne
kuma wanda ya fi yawa a cikin mata.
2. Akwai kuma wanda nau’in
kayan abinci ko abin sha ne na halal wanda mace ke ci ko sha ko shafawa ko yin
wanka da shi, domin ya gyara mata jiki ya zama mai laushi ko taushi, ba tare da
wani abu na saddabaru ko mu’amalar bokaye ko matsafa ba. Wannan halal ne, ba
laifi ba ne, in sha’al Laah.
Sai dai akwai tsoron cewa,
ta wannan hanyar ana iya bayar da maganin ‘matsi’ kamar yadda aka ambata a
wannan fatawar. Wannan kuma yana iya kai ’yan mata ga cigaba da holewa kafin
aure, tun da suna da sanin cewa akwai wannan maganin da za su yi amfani da shi
kafin tarewa da mazajensu na aure! Sai a kiyaye sosai, kar aikin ya zama
taimakawa wurin yaɗa ɓarna,
maimakon maganinta da daƙile
ta a cikin al’umma.
3. Akwai kuma waɗansu
magungunan da su ke ƙwayoyi
ne ko allurori irin na asibiti da ake yi wa mace na wani lokaci, har kuma hakan
ya kai ga sauya mata yana yi da launin fatar jiki ko kuma gashin kai, sauyawa
tabbatacce na dindindin. Wannan kai-tsaye ya saɓa wa
dokokin musulunci mai hana zaƙewa
da wuce iyaka a wurin kwalliya, domin Manzon Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa
Alihi Wa Sallam) ya ce:
«لَعَنَ اللهُ الْوَاشِمَاتِ وَالْمُسْتَوْشِمَاتِ، وَالنَّامِصَاتِ وَالْمُتَنَمِّصَاتِ، وَالْمُتَفَلِّجَاتِ لِلْحُسْنِ الْمُغَيِّرَاتِ خَلْقَ اللهِ»
Allaah ya la’anci mata masu
yin zane a fatar jiki da masu neman a yi musu zanen; da mata masu aske gashin
fuska da masu neman a aske musu; da mata masu yin wushirya, domin ƙarin kyau, masu sauya halittar Allaah. (Sahih
Al-Bukhaariy: 4886; Sahih Muslim: 2125).
Abu ne dai sananne a wurin
masana cewa, duk abin da aka cusa wa jikin ɗan’adam
alhali ba yana da buƙatarsa
ba, wannan yana haifar da matsala gare shi ko a kusa ko a nesa.
A ƙarƙashin
wannan dole mai sayar da irin wannan kayayyakin ta yi taka-tsantsan, ta bincika
ta tabbatar ba zai cutar da wadda za ta yi amfani da shi ba ko a nan kusa ko a
can nesa. Kuma a nan babu bambanci ko wacce za ta yi amfanin da shi musulma ce
ko wacce ba musulma ba. Kuma ko matar kirki ce mai kamun kai, ko kuwa dai
karuwa ce mai zaman kanta. Duk dai bai halatta musulma ta zama sanadin cutarwa
ga kowa ba.
Allaah ya ƙara mana shiriya.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad Abdullaah
Assalafiy
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.