GWANI A ALƘUR'ANI || SHA'IRI || ƊAN GWAGWARMAYAR SIYASA || ƊAN KISHIN HAUSA
KAI HIDIMA KAN GYARA ƘASATA.
(AMSHI)
In dai kana shaƙa
numfashi,
Ka ci ka sha
har ma kai kashi,
Muddin mutum na
kwana ya tashi,
To wataran dole
ba ya tashi,
Ko ba—daɗe zai je maƙabarta.
Da ta iso rai
ne za ta karɓe,
Kan-mai-jawabi
ai ba ta zaɓe,
Ai ba a zille
wa ko a saɓe,
Riƙo na
tarna take ba—raɓe,
Dangi abokai
har ma maƙota.
Ta gangaro kan
Garba sadauki,
Ɗan
Gashuwa sha'iri fa gwanki,
Fannin fusaha
cene shi zaki,
Labarin tamkar
fa a mafarki,
Fesbuk rubuce
na ko karanta.
Waƙar
"Mutum wanda ba a i mai",
"Sannu da
Himma" ka bi da mai-mai,
"Allah
kiyaye" waƙar da yai mai,
IBB ya tabbatar
da komai,
Fannin ƙasida
ya jinjina mai,
Dukkan fasihai
ya ba su rata.
Gwagwarmayatai
har ƙoƙari
nai,
Ya ɓata dukkan nin shekarunai,
A ƴanta
kowa yayye da ƙannai,
Dan mu ji daɗi ya sai da rainai,
Sannu da himma
ka so ƙasata.
Barden mawaƙa an
sallama ma,
Maƙogaran
P.R.P bale ma,
In kun haɗe da Isah Bunguɗu ma,
Sauran Fasihai
ba mai fa toma,
Idon su dan dai
zai raina fata.
Dare da rana
sanyi da zafi,
Duk mun wuya ya
tsaya a kaifi,
Guda fa shi bai
da wani haufi,
A kanmu ya jure
duka yarfi,
Allah ya saka
Barden Ƙasata.
Shin me ya
saura a duniyar nan,
Ya ku fasihai
ku san da wannan,
Ba Sambo Wali
ba Garba wannan,
Ba ɗan Magoga a shekarar nan,
Mun yo rashin
Sha'iranmu kwata.
To yanzu
aikinsu ne ya wanzu,
Kamar suna nan ƙasar a
yanzu,
Dan sun fa
jajirce ne a ɗazu,
Me zai hana mu
ma mui gumurzu,
Dan gyara
addini na ƙasata.
Yau Garba
Gashuwa ya je makwanci,
Ya za mu kwanta
wai mui ta barci,
Bayan ƙasar
ta zurfafa ƙunci,
Da ba ta kai
hakka ba a ɓaci,
Su Garba sun
kai tsaye mu huta.
An tafka
jibgegiyar asara,
Kan ilimi yau ƙasa a
tura,
Ga hikima ba
dama a shura,
Ahir Fasihai mu
bar gadara,
Cikinmu wai zai
tsaya ku furta.
Kai Jalla ya
mai baiwar fusaha,
Wajen yabo gun
Manzanmu Ɗaha,
Ka duba
littafinai Fusaha,
Tsantsar basira
ya mai Ilaha,
Da kwaikwayon
ma murya ta Shata.
Na yo kira to
gurbin Hukuma,
Kar dai a mance
sunansa shi ma,
Da hidimarsa ga
ƴan
ƙasa
ma,
A SANYA SUNANSA
JAMI'A MA,
Wannan fa shi
ne to manufata.
Kan Sambo Wali
muna tuni ma,
Malam Kabiru
Magoga shi ma,
Da Dr. Yusuf ɗan Ali shi ma,
Ga Sheikh Muhd Ƙani fa
shi ma,
Sun hidima gun
gyara ƙasata.
Barden mawaƙa ga ƙi—garaje,
Zaki fashe
ayarin mazaje,
In yai amo kai
tamkar ya gwarje,
Sai nan-da-nan
sun karkaɗe buje,
Sun gudu ba sa ƙaunar ƙasata.
Kiran da zan yi
aboka dangi,
Ku dangana ba
ihu da zagi,
Dan kar mu faɗa cikin fa ƙangi,
Rai na wurin
Jalla babu zargi,
Shi ya ara mai
ya kuma ƙwata.
Me zan yi wai
ne yau rai ya huta,
Wai in yi kuka
ko in fusata,
Ko na yi ma bai
biyan buƙata,
To zai fi ma in
yi addu'ata,
Ga malami Garba
na ƙasata.
Allah kai ne
Rabbi Ganiyyu,
Me sama Allah
ya Alhayyu,
Dan darajar
Manzonka Nabiyyu,
Gun Garba yo
rahmarka Ganiyyu,
Ka haskaka mai
inda ya kwanta.
Allah dai kai
ne da sarauta,
Don haka kai ne
ka yi halitta,
Don haka kai
kab bani fahimta,
In shirya waƙa har
in rubuta,
Kan ta'aziyyar
Garba na yi ta.
Ka ƙara
salati gun Manzo,
Ahmadu Ahmadu
mai ƙwazo,
Alu Sahabbainai
Manzo,
Ka sa su ciki
maƙurar
ƙwazo,
Ka ban ladar
ta'aziyyata.
(m) Usman Nagado (II)
1 ga Satumba, 2025.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.