Ticker

6/recent/ticker-posts

Ba-Ga-Giji Babbar Laya: Wakar Yabon Farfesa Faruk Sarkinfada

BISMIL LAHIR RAHAMANUR RAHIM,
WA SALLALLAHU ALAL NABIYYUL KHARIM

 

1. Fa bismillahi na fara,

Bi hamdillahi nai shukura,

A farko har zuwa ƙara,

Ya Arrahamanu na yi bara,

Ka min tanyo in ko ida.


2. Wa sallallahu Ya Allah,

Alal Mukhtari wal Ala,

Ma’al Ashabi ya Allah,

Ka za ma’a Auliya’allah,

Madad dahri, bi la hadda.

 

3. Yo ga iska ta na rugi,

Ta yo laftu na ‘yan dangi,

Su na tsumuwa ta na gangi,

Hamada ba ta kai wargi,

A gare ta kai a har abada.

 

4. Begen iskar hamada yau,

Ya sa ni na barkace ha i yau,

In ta taso kamar ma yau,

In tashi in hau bisanta ayau,

 Ta kai ni Dubai wurin Sanda.

 

4. Begen iskar hamada yau,

Ya sa ni na barkace ha i yau,

In ta taso kamar ma yau,

In tashi in hau bisanta ayau,

 Ta kai ni Dubai wurin Sanda.

 

5. Da na ga fa girgije a sama,

Ya na tafiya da sawunsa,

Sai in ji kamar na hau kansa,

Ya kai ni gusun ga Farfesa,

Mu gaisa can Dubai abada.

 

6. Alalo-alalo taɓakaka,

Zumaina ‘yan uwa barka,

Yaya bazara da albarka,

Fatan hairi da albarka,

A gareku tutur a har abada.

 

7. Ina ka ke ne Professor,

A Sarkinfada Farfesa,

Fa na leƙo mu ɗan gaisa,

Alla gafarta na ce ma Sir,

 Fatan ka kwan ƙalau Sanda.

 

8. Ina tuntuntuni kanka,

A kullum zan yi hirarka,

A zuci na ɗarsa begenka,

Ƙafa ta za ta zo gunka,

Ido na yaushe zai tar da.

 

9. Nisa ga shi yai illa,

Zukata ga shi sun ƙulla,

Alaƙa mai dubun galla,

Mai dugunzuma dukka hankulla,

 Wayyo Malam Prof. Sanda.

 

10. Arwahu su na cikin shauƙi,

Zukata na hawan-na-ƙi,

Ana ta ruguntsumin yaƙi,

A fagen fama jiki yaƙi,

Zumunta za a dai sada.

 

11. Jama’a fa ku daina inkari,

A kan na yo yabon bahari,

Prof Faruku kui nazari,

Darajarsa cikin dubu da ɗari,

Kaɗan ciki ba ni kardada.

 

12. A farko ga sani gunsa,

Don yai ilimi na dininsa,

Balle fa na zamanin nasa,

Ya danganta ga Farfesa,

 Darajar ƙarshe ya kai Sanda.

 

13. Malam ya san Samarƙandi,

Isa Guji da Ɗanwardi,

Ya na raddi ga mai liddi,

Ya shirya tsaf da kyankyandi,

Ya san funfunfuni Sanda.

 

14. Ya zam bahari a gun ilmu,

Mu runtuma duk ya sashe mu,

Fagagen ilmu zai bamu,

Ƙwararren duk ƙishirwarmu,

 Yau za ta gushe a gun Sanda.

 

15. Sannan ga kyan mu’amilla,

Haƙuri jarinsa ne walla,

Bin dattawa ya mai galla,

Ga son Manzo ya na salla,

Ai dole su bar ka alfanda.

 

16. Karimi ga karimanci,

Ba ya jito da zalunci,

Ba ya sabga ta ƙasƙanci,

Ba ya son mai ƙicen zuci,

Tilas na yabe ka ai Sanda.

 

17. Malam zai ba ka mamaki,

A sabaucin ƙan da kai, kirki,

Bai girma kai da jin mulki,

Kuma ya fa fito gidan mulki,

Ɗan sarki danganen fada.

 

18. Tafi maƙasau irin kirki,

Ka fanshi dubu fa jan zaki,

Ina kura ina shaki,

Ku bar hanya ku bar tafki,

Ga zaki ya taho Sanda.

 

19. Su ‘yartsaddi a ɗau hanya,

Biri da Dila a bar hanya,

Su ɗan akuya a ɗau hanya,

Ku ce dirwa ta sau hanya,

A yau ko ran ta ta sai da.

 

20. Lafiya bango na al’uma,

Lafiya Santo a gogarma,

Lafiya mai sha da al’uma,

Lafiya mai danganen girma,

Ga garnaƙaƙi bison fada.

 

21. A min afuwa fa Farfesa,

Tabbas laifi fa na yi sa,

Ka na ta kira mu ɗan gaisa,

Ba ka samun waya ta Sir,

Ina tuba Prof. Sanda.

 

22. Da ga nan ka ƙudurce yin niyya,

Ka zo ka ishen a Zawiyya,

A tirƙashi ina kunya,

Ka zo ban zo ba ba kunya,

Ina girmanka na zubda.

 

23. Ina ta kiran waya nan ma,

Ta na kashe ba ta ko cimma,

Sai nai aniya na ɗau himma,

Ta zan zo gunka nai azama,

In sadu da kai Prof Sanda.

 

24. Fa na leƙo gidan na ka,

Mu gaisa dan in ɗan ganka,

Malam Ahmad ya ce ba ka,

Nan fa ka na Dubai hakka,

Sai nai kewar ka alfanda.

 

25. To yau na zo ni har fada,

Mu yo taɗi cikin fada,

In kurɓi dawo furar fada,

Da alkakin cikin fada,

Da funkason mutan fada.

 

26. In tauna ƙashi in ko tsotse,

In sha madara da an tatse,

In kwashi tuwo in ko gyatse,

In lashi zuma na ma katse,

Garar baƙi fa sai fada.

 

27. Da na ƙare na hau doki,

Fari fat ai kilin yaƙi,

Na yo sukuwa na ja burki,

Nai jinjini ga ɗan sarki,

 Malam kuma ginshiƙin fada.

 

28. Bararren ɗa na mai fada,

Karimin ‘yan cikin fada,

Wata ran kai ne cikin fada,

Irin ku a ke biɗa fada,

Takawa sannu alfanda.

 

29. Tafi gindigirin icen gamji,

Ana sara ya na gumji,

Ya na tofo ya na rauji,

Bahagon gulbi cike daji,

Ɗan sarki tarsashin fada.

 

30. Kasankama mai shirin yaƙi,

Kai ar ga ɗumfaman yaƙi,

Ya ɗauro janjamin yaƙi,

Ga kansakulan fita yaƙi,

Ƙi-garaje jarumin fada.

 

31. Nagarta ka ji tsaninsa,

Zumunci ka ji takensa,

Haƙuri kuma ka ji jarinsa,

Son Manzo am muradinsa,

A kullum kai a har abada.

 

32. Sannan Malam fasihi ne,

Ya na waƙa ƙwararre ne,

Lungu saƙonta ya gane,

A take yanke zai aune,

Ya tsara ba batun ganda.

 

33. Malam bai ma tsaya nan ba,

Bai ƙyale wallafofi ba,

Ba zai kuma kasa sharhi ba,

Na littafi da waƙa ba,

Manzon Adabi da al’ada.

 

34. Gogan harshe a Larabci,

Wata rana sai yai da Turanci,

In ya so yai da Hausanci,

Hirarsa gami da kakaci,

Ga taɗoɗinsa na bada.

 

35. Fa Farfesa taƙiyyi ne,

Yakana ƙana’a hali nai ne,

Tsantseni na sa mun gane,

A dattako sananne ne,

Tsabi’u ba ya alfanda.

 

36. Ya na son Annabin Allah,

Da iyalan Annabin Allah,

Da sahabban Annabin Allah,

Da sharifai Auliya’allah,

Bai inkarinsu alfanda.

 

37. Bugu-ƙari Professor,

Ya leƙa ƙasa-ƙasa ai Sir,

Ya je Landan fa Farfesa,

Ya je shi Dubai Professor,

Ya na koyar da su Sanda.

 

38.Ɗalibai nai Larabawa ne,

Da Larabci ya ke aune,

Ya koyarsu su na zaune,

Darussan Ingilishi ne,

Ya ke Tafinta alfanda.

 

39. Su na ta cika da mamaki,

Baƙar fata da mamaki,

Ya na Arabiyya ba miki,

Su kumma su na sakin baki,

Ajaban ajaban li S.Fada.

 

40. Ga ‘yar waƙar da ni nai ta,

Ta ban haƙuri a dube ta,

Ko ba wazani a karɓe ta,

Ko ba tsari a amshe ta,

Manufa haƙuri in dai bada.

 

41. Da fatan za a yafe ni,

A min afuwa a karɓe ni,

A gafarta a dube ni,

A ce lale a tarbe ni,

Ya Farfesanmu S. Fada.

 

42. In ka yafe Professor,

Ina fa jiran ka ban amsa,

Da waƙa za ka ban amsa,

Don kai ma sha’iri ne Sir,

 Na gani na faɗa a har abada.

 

43. Waƙa wa ne talalako,

Wa ne banzar gari soko,

Adabi a cikin ta lo-loko,

Duba a cikin Tabarkoko,

Da zugagen sha’iri ad da.

 

44. Kyawun waƙa da ‘yan amshi,

Jigo shi ne fa harsashi,

Sa amsa-amo ta yo ƙamshi,

Adon harshe fa ke ƙunshi,

Ga waƙa tai yi tsaf abada.

 

45. Cikar waƙa ayo ramzi,

Adon waƙa kwa ilgazi,

Mafi sauƙin ta kan rajazi,

Waƙa fa ta kan zamo kanzi,

Taskar harshe da al’ada.

 

46. Waƙa fa ta na biɗar haddi,

Lafuzanta ya zam akwai ƙaidi,

Ɗangwayenta a kan adadi,

Saƙonta tsatsaf fa ba liddi,

Ku jiya ku sha’irai abada.

 

47. Jigon waƙa ya zam siddi,

Na hawanta zuwa fagen rushdi,

Salon sha’ir ya zam lifidi,

Awo ƙaiminta kan adadi,

Na ƙafafunta a har abada.

 

48. Na kai ga sukwa fa na ƙare,

Zamiyar ma nai ta ta ƙare,

Kama-zuru na ja na tsare,

Na kai muri fa na ɗaure,

Waƙata tai cikar idda.

 

49. Ƙure doki fa ingarma,

Gano haske na bantarma,

Ga zirnaƙo da gwazarma,

Dodo na ruwa fa dangarma,

Allura ta haƙe garma,

Kafin haɗiya akwai loma,

Batun nan banda mai ganda.

 

50. Salon waƙa na ɗan tsarma,

Ga masu ƙulafucin nema,

Waƙa tamkar ya gogarma,

Basiɗine ƙure noma,

 Ku zo ku sha’irai ku gwada.

 

51. Tammat na kammale waƙa,

Yaumal Thulatha’a nai waƙa,

A Rabi lauwal ta kai matuƙa,

Kwana ashirin biyat liƙa,

Ka samu cikon fitar adada.

 

52. Af to saura batun ramzi,

Fi HAMTASHU (همتش)karɓi ga ramzi,

Hijirar Manzo Rasulu huzi,

Kai hauzi, sai ka nem hazzi,

 Buga kulkin sai ka sam adada.

 

53. A hisabin baitukan nata,

WAISUN (ويص) adadinsu to kwata,

Larabawa kui iwal nata,

Da Hausa na zo da waƙenta,

Don tai sauƙi a gun hadda.

 

54. Bagagiji ne fa sunanta,

Babbar laya kirarinta,

Ga Farfesa na tsaro ta,

Yan Hausa ku ɗau nazar nata,

 Ku rabe ƙaura da kau tsada.

 

55. A batun waye ya tsaro ta,

Usman Nagado ya shiryo ta,

Ɗalibin Shehu Ƙani yai ta,

Gusawi gun zuciya likita,

A Gwale ya yi ta ba ganda.

 

56. In ka so sai ka sa harufa,

Kai babbaƙu farfaru ka ɗafa,

Inu (ع) da Ca (ث) da Mim (م) ka ɗafa,

Alu-ja (ا) Nun (ن) haɗa ka rufa,

To ce Usman aje ganda.

 

57. Ana kwana ana tashi,

Ana ta ragar mu numfashi,

Mu na daɗa ƙara alwashi,

Kwatsam rai zai halin na shi,

 Mutuwa ta ishe mu har fada.

 

58. Mu yo saunar biɗar tuba,

Gaban mutuwa ta zo arba,

Mu riski bukin dakan gumba,

Mu hanzarta gurin Rabba,

 Mu tuba a nan mu bar ganda.

 

59. Salati zan a ƙarshenta,

Ga Ɗahe mai hana ni ɓata,

Da Alayensa sun kuɓuta,

Da Sahabbai kunzumi kwata,

Da salami ban bari abada.

 

60. Allah na roƙi fatana,

Nunan Manzo Ma’aikina,

Shahada ran fitar raina,

Ta zam furuci na bakina,

Ka min tanyo in ko ida.

TAMAT

(M) Usman Nagado (II)
Bulangu86@gmail.com
Talata, 25- Rabi al-auwal, 1445 (H).
10 Oktoba, 2023. (M)

Post a Comment

0 Comments