Ba yau aka fara samun masu sukar Hadisan Annabi (saw) ba, a'a, tun zamanin magabata an samu masu yakar Hadisan Annabi (saw) bisa manufofi daban-daban, ta bangaren Munafukai masu yakar Muslunci, haka kuma ta bangaren wasu Musulmai gafalallu da aka yaudara da sunan ba da kariya ga Sunna, da sunan ware Hadisan da suka saba hankali ko suka saba waqi'i ko suka saba Alkur'ani, da sauran munanan manufofi da aka yi musu ado da kyawawan sunaye.
Don haka aka samu masu yakar
Sunnar ta hanyar jefa shakku a zakutan Musulmai game da Hadisan Annabi, da kira
ga riko da Alkur'ani kadai ban da Sunna.
Da kuma masu sukar maruwaitan
Hadisan -har Sahabbai- da sukar hanyar da aka ruwaito su.
Da masu gindaya wasu sharuda da
ba su da asali, kamar cewa; ba a daukar Aqida daga Hadisi "Ahaad"
saboda zato ne, ko ba a kafa hujja da Hadisi in ya saba hankali, ko ya saba
Alkur'ani, d.s.
Tun zamanin Sahabbai aka samu
irin wadannan mutane, shi ya sa a lokacin da wani ya zo wajen Sahabin Annabi
(saw) Imrana bn Huswain (ra) ya ce masa:
"Ya kai Baban Nujaid, kuna
karantar da mu wasu Hadisan da ba su da asali a cikin Alkur'ani. Sai Imran ya
fusata ya ce masa:
{Shin ka karanta Alkur'ani?} Sai
ya ce: Eh.
{Shin a cikin Alkur'ani ka ga
inda aka ce Sallar Isha'i raka'a hudu ce, Magriba uku, Asubah biyu, Azahar da
La'asar hudu?}. Sai ya ce: A'ah.
Sai ya ce: {To a wajen wa kuka
samu hakan, shin ba daga gare mu kuka samu ba, mu kuma mun samo daga Annabi
(saw)?".
To kun ga kenan, idan ka ce za ka
jefar da wani Hadisi da ya tabbata daga Annabi (saw) to sai ka watsar da
Sallolin da kake yi, saboda babu bayanin adadin raka'o'insu a Alkur'ani Mai
girma.
Haka aka samu wani mutum ya ce wa
Mudarrif bn Abdillah: Kar ku karanta mana komai sai abin da ke cikin Alkur'ani
kadai. Sai Mudarrif ya ce masa:
{Mu ma ba ma bukatar canjin
Alkur'ani, amma muna bukatar bayanin wanda ya fi mu sanin Alkur'anin (wato
Manzon Allah)".
Haka nan aka yi ta samun masu
inkarin Hadisan Manzon Allah (saw), da sunan bin Alkur'ani, ko da sunan ya saba
ma hankali da sauransu. Aka samu 'Yan Jahamiyya da Mu'utazila da sauran
kungiyoyi masu yakar Sunna, suka yi ta inkarin Hadisan da suka saba munanan
Aqidunsu da son zuciyoyinsu.
Malaman Muslunci kuwa ba su gushe
ba suna yi musu raddi suna tona musu asiri, irin su Imamu Shafi'iy cikin
littafinsa "Jima'ul Ilm", da Imam Ibnu Qutaiba cikin littafinsa
"Ta'awilu Mukhtalafil Hadeeth".
Haka abin ya cigaba da tafiya har
ya iso wannan zamani, ta yadda ya zama duk wani Dan Bidi'a ko Mai son zuciya za
ka samu yana yakar Hadisan da suka saba ma Bidi'arsa da son zuciyarsa, yana
sukarsu yana karyata su, kawai don sun saba son zuciyarsa.
A takaice, bacin wannan mummunan
tafarki a fili yake, saboda in har da gaske ka yi imani da Alkur'ani, to a
cikinsa Allah ya yi umurni da bin Allah da bin Manzonsa (saw), alhali babu
yadda za ka bi Allah sai ta hanyar bin Alkur'ani, kamar yadda babu yadda za ka
bi Annabi sai ta hanyar bin Hadisansa tabbatattu.
Kuma babu tabbataccen Hadisin da
yake cin karo da Alkur'ani ko lafiyayyen hankali. Matukar Hadisi ya tabbata,
amma sai ka ga ya saba hankalinka, to ka tuhumi hankalin naka, hankalin naka ne
ya samu tabuwa ba Hadisin ne bai tabbata ba.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.