Duka karerayin 'Yan Shi'a a kan imamancin Imamansu 12 sun kitsa su ne a kan Hadisin "Muwalati", wanda Annabi (saw) ya fade shi a rana mai kamar ta yau, wato ranar 18 ga Zul-Hijja, a Ghadeer Khum, a kan hanyarsa ta komawa Madina daga Aikin Hajji.
Wannan Hadisin ya tabbata, Imamu
Tirmiziy ya fitar da shi, amma sai dai 'Yan Shi'a sun juya ma'anarsa kamar
yadda Yahudawa suke juya ma'anonin maganar Allah.
Shi ya sa Imamul Baihaqiy ya
ruwaito da Isnadinsa daga Rabee'i Almajirin Imamu Shafi'iy ya ce:
"سمعت الشافعي يقول في معنى قول النبي صلى الله
عليه وسلم لعلي بن أبي طالب رضي الله عنه: «من كنت مولاه فعلى مولاه» يعني بذلك ولاء
الإسلام. وذلك قول الله تعالى: {ذلك بأن الله مولى الذين آمنوا وأن الكافرين لا مولى
لهم}.
وأما
قول عمر بن الخطاب لعلي: «أصبحت مولى كل مؤمن» يقول: ولى كل مسلم".
مناقب
الشافعي للبيهقي (1/ 337)، الاعتقاد للبيهقي (ص: 355)، تاريخ دمشق لابن عساكر
(42/ 238)
"Na ji Shafi'iy yana cewa;
ma'anar fadin Annabi (saw) ga Aliyu bn Abi Dalib (ra) {Duk wanda na kasance Maulansa
to Aliyu ma Maulansa ne}, yana nufin jibinta ce ta Muslunci. Wannan kuwa shi ne
ke cikin fadin Allah Madaukaki:
{ذلك بأن
الله مولى الذين آمنوا وأن الكافرين لا مولى لهم}
"Hakan saboda Allah shi ne
majibincin wadanda suka yi imani, kafirai kam ba su da majibinci".
Amma fadin Umar bn Khaddab (ra)
ga Aliyu: "Ka wayi gari Maulan kowane Mumini", yana nufin Majibincin
kowane Mumini, (wato masoyi mai taimako)".
Haka Ibnu Asakir ya ruwaito
ma'anar wannar kalma daga babban Malamin Harshen Larabci Ibnul A'arabiy inda ya
ce:
"المولى المالك وهو الله والمولى ابن العم والمولى
المعتق والمولى المعتق والمولى الجار والمولى الشريك والمولى الحليف والمولى المحب
والمولى اللوي والمولى الولي ومنه قول النبي (صلى الله عليه وسلم) (من كنت مولاه فعلي
مولاه) معناه من تولاني فليتول عليا.
قال ثعلب:
...ولكنه من باب المحبة والطاعة ويدل على أن المولى والولي المحب".
تاريخ
دمشق لابن عساكر (42/ 238)
"Maula shi ne mamallaki,
kuma shi ne Allah. Kuma Maula shi ne Dan Baffa, kuma wanda ya 'yanta bawa, kuma
bawan da aka 'yanta, kuma makobci, kuma abokin tarayya, kuma halifi, kuma
Masoyi, kuma Majibinci, daga haka akwai fadin Annabi (saw): {Duk wanda na
kasance Maulansa to Aliyu ma Maulansa ne}, ma'ana; duk wanda ya jibince ni to
ya jibinci Aliyu.
Tha'alab ya ce:.... Wannan a
babin soyayya da da'a ne, yana nuni ga cewa; Maula da Waliyyi shi ne
Masoyi".
Saboda haka, Bidi'ar Rafidha 'Yan
Shi'a ta ginu ne a kan juya maganar Allah da Manzonsa (saw) da canza ma'anar
abin da suka fada, kamar yadda Yahudawa suke yi. Da ma Malam Bahaushe ya ce:
Barewa ba za ta yi gudu danta ya yi rarrafe ba!
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.