Sunan "Ahlus Sunnati wal Jama'a" suna ne da yake dauke da ma'ana ta Shari'a, ba suna ne fanko maras ma'ana ba. Don haka sunan ba ya dacewa sai da wanda ma'anar sunan ta tabbata a tare da shi.
Ahlus Sunnati wal Jama'a su ne
Sahabban Manzon Allah (s.a.w), su ne "Jama'a", wadanda suke kan tafarkin Qur'ani da Sunnar
Annabi (s.a.w), sai kuma wadanda suka bi tafarkinsu cikin Tabi'ai da mabiyansu
har zuwa yau. Don haka duk wanda ba a kan tafarkin Sahabbai yake ba, to ba
Ahlus Sunna ba ne, ko da kuwa ya fi kowa ikrarin cewa; shi ne Ahlus Sunnati wal
Jama'a kawai.
Sahabban Annabi (s.a.w) sun
kasance a bisa tafarkin da Annabi (s.a.w) ya dorasu a kansa, har ya koma ga
Ubangijinsa ya barsu suna kan wannan tafarki, ba su canza ba. Haka mabiyansu
suka cigaba da tafiya a kan wannan tafarki har zuwa yau babu canji.
Tun zamanin Sahabbai aka fara
samun wadanda suka rabu da wannar Jama'a, inda aka fara samun Khawarijawa suka
fita daga al'ummar Musulmi suka dauki makami a kanta. Haka aka samu 'Yan Shi'a
suka ware, bayansu aka samu 'Yan Kadariyya, sai kuma Murji'a. Duka wadannan a
zamanin Sahabbai suka bayyana a jere. Sai kuma bayan zamanin Sahabbai aka samu
Jahamiyya, Mu'utazila.
To haka 'yan bidi'a mabiya son
rai suka cigaba da rabuwa daga tafarkin Sahabbai har zuwa lokacin da aka samu
bayyanar "Asha'ira" mabiya Abul Hassan Al- Ash'ariy (324), bayansu
kuma aka samu bayyanar "Maturidiyya", mabiya Abu Mansur Al- Maturidiy
(333).
Mazhabar "Maturidiyya"
ita ce Mazhabin da mafiya yawan 'yan Mazhabar Hanafiyya suke bi a Aqida,
kasancewarsa Dan Mazhabar Hanafiyya a Fiqhu.
Wannar Mazhaba ta Maturidiyya ita
ce: Mazhabar mafiya yawan wadanda suke gabashin Duniya; Pakistan, India, Rasha
da sauransu.
Asha'ira da Maturidiyya duka sun
saba wa tafarkin Salaf Ahlus Sunnan farko; Sahabbai da Tabi'ai da A'imma,
irinsu Imamu Abu Hanifa, Malik, Shafi'iy da Imamu Ahmad bn Hanbal, amma su suka
fi kusa da Ahlus Sunna a kan sauran 'Yan Bidi'a da son rai. Shaikhul Islami ®
ya ce:
الأشعرية
فلا يرون السيف موافقة لأهل الحديث وهم في الجملة أقرب المتكلمين إلى مذهب أهل السنة
والحديث.
مجموع
الفتاوى (6/ 55)
"Ash'ariyya ba su da Aqidar
yakar al'umma da shugabanni dacewa da Ahlul Hadees, a dunkule su ne mafi kusaci
ga Ahlus Sunnati wal Hadees a kan sauran mabiya ilmul kalam".
Dalilai da suke nuna banbanci
tsakanin Aqidun Asha'ira da Maturidiyya da Aqidar Ahlus Sunnan farko:
1- Sun saba musu a babin Daukar
Aqida, suna daukar Aqida ne daga hankali, shi ya sa suke Tawilin Nassoshin
Qur'ani da Hadisai su tankwasasu sai sun yi dadai da hankulansu. Suke cewa:
"Idan Nassi ya yi karo da
hankali to wajibi ne a tankwasa Nassin ya bi hankali, in kuma ba zai tankwasu
ba, to dole a ajiye Nassin a bi hankali, saboda hankalin shi ne asali akan
Nassi, ajiye asalin kuwa suka ne ga Nassin".
Baci da munin wannar magana a
fili yake ga dukkan wanda yake ganin girman Qur'ani da Sunna.
2- Sun saba wa Salaf a babin
Imani da Allah, saboda:
(a) Suna cewa; farkon wajibi a
kan bawa shi ne; Nazari cikin dalilan halitta don sanin Allah, alhali kowa ya
san Allah ne da fidirarsa. Kuma farkon wajibi shi ne: "Shaidawa babu abin
bauta da cancanta sai Allah, kuma Annabi Muhammad Manzon Allah ne".
(b) A babin Tauhidin Rububiyya,
suna ganin ana sanin Allah da tabbatar da samuwarsa ne da hankali (Nazari), ba
da fitira da Shari'a ba.
(c) Ba su san Tauhidin Uluhiyya
ba, (Tauhidul Ibada), shi ya sa suke fassara shi da Tauhidin Rububiyya, suke
fassara kalmar Shahada da cewa: "Babu Mahallici sai Allah", a
maimakon "Babu abin bauta da gaskiya sai Allah". Wannan ya sa suke
afkawa cikin Shirka a bauta, wajen rokon waliyyai, da dawafi a kabarbura da
yanka ma wanin Allah da makamantansu. Alhali wannan Tauhidi shi ne hakikanin
Addinin Muslunci da Annabawa suka zo da shi.
(d) Suna kore ma Allah Siffofinsa
da ya siffanta kansa da su a cikin Littafinsa, da wadanda Manzonsa (s.a.w) ya
siffanta shi da su a cikin Sunnarsa ta hanyar tawilin Nassoshin da Siffofin.
(e) Asha'ira siffofi bakwai kawai
suke tabbatarwa, Maturidiyya kuma takwas. Shi ya sa suke kore Daukakar Allah a
saman halittarsa, suke cewa: -wai- Allah yana ko'ina, alhali a fili karara
Allah ya ce: Ya daukaka a saman Al'Arshinsa.
3- A babin Imani da Littafan
Allah kuwa, hakikanin ra'ayinsu shi ne; Al- Qur'ani halitta ne, saboda
ra'ayinsu kusa yake da ra'ayin Mu'utazilawa, kawai a lafazi ne suka saba, amma
sun dace da su a ma'ana.
4- A babin Imani da Manzanni suna
ganin Annabi (s.a.w) ya san gaibi, wanda hakan zai iya kaiwa ga Shirka ma Allah
a cikin siffarsa da ya kadaita da ita ta sanin gaibi shi kadai.
5- A babin Imani da Kaddara
ra'ayinsu kusa yake da ra'ayin Jabariyya, masu cewa: Mutum ba shi da tasiri
wajen aikata aiyukansa, don haka dukkan aiyukan da yake aikatawa na alheri da
na sharri -wai- duka Allah ne yake aikatawa, har na zina da shan giya da
kafirci, -wai- duka Allah ne yake aikatawa - subhanallah-, saboda shi mutum ba
ya aikata komai da kansa, kawai yana nan ne kamar busassshen ganyen bishiya da
iska take yawo da shi duk inda take so. Sun saba wa Jabariyya a suna amma sun
dace da su a ma'ana. Wato a ra'ayinsu na "Kasab".
6- Sai kuma a babin Hakikanin
Imani da Aiki, suna tafiya ne a kan ra'ayin Murji'a, saboda imani a wajen
Asha'ira da Maturidiyya shi ne Gaskatawar zuci kawai. Ma'ana daga zarar mutum
ya gaskata Allah a zuciya to kawai ya je ya sheke ayarsa yadda yake so. Don
haka a wajensu, magana da aiki ba sa cikin hakikanin Imani.
7- Banbancin da ke tsakanin
Asha'ira da Maturidiyya dan kadan ne, saboda duka asalinsu daya ne, wato
"Kullabiyya".
Su kuma Sufaye, launinsu daban
ne, duk da cewa; Asha'ira da Maturidiyya su ne dai Sufayen ta bangaren Suluki.
Banbanci mafi muhimmanci tsakanin
Sufaye da Ahlus Sunna, suna daukan Addininsu ne ta hanyar:
(1) Hadisan karya.
(2) Ilhama.
(3) Zauqi da Wajdi.
(4) Kashafi.
Kowanne daga cikin wadannan yana
da nau'o'i.
Tauhidinsu shi ne Hululi da
Ittihadi da Guluwwi a kan Waliyyai da Shehunnai da tsarkakesu, da kuma rokonsu
da neman taimakonsu koma bayan Allah.
Hakikanin matsayin Walittaka ya
fi matsayin Annabta da Manzanci a wajensu.
A babin Imani da Kaddara su
tsantsan 'Yan Jabariyya ne, haka a babin Hakikanin Imani tsantsar Murji'a ne,
shi ya sa suke halasta sheke aya, da alfasha, da aikata dukkan ma~sha'a iya
yadda suke so.
Gwanaye ne wajen bautan
kabarburan waliyyai, da yin tawassuli na bidi'a, da zikirori na bidi'a da kuma
kide-kide da raye – raye da rawa da rangwada duka da sunan Ibada. Da kuma
sauran bidi'o'i da aiyuka na Shirka da yake bayyana wa mutane, da ma wadanda babu
wanda ya sansu sai Allah.
A dunkule, duka wadannan munanan
Aqidu ne da suka saba wa Qur'ani da Sunna, suke warware Aqidar Ahlus Sunnan
farko, wato Sahabbai da Tabi'ai da Limaman Muslunci; Imamu Abu Hanifa, Malik,
Shafi'iy da Ahmad.
SABODA HAKA, TA YAYA ZA A YI ACE:
ASHA'IRA DA MATURIDIYYA DA SUFAYE SU NE AHLUS SUNNAI WAL JAMA'A, -WAI- KUMA
MABIYA TAFARKIN SAHABBAI SU BA AHLUS SUNNA BA NE?!
KAMAR HANKALI BA ZAI YARDA DA
WANNAN BA, KUMA WAQI'I YANA KARYATASU!
Saboda haka hanyar jirgi daban da
ta mota.
Wallahu A'alam.
Dr. Aliyu Muh'd Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.