Hukuncin Wanda Ke Leƙen Tsaraicin Mutane
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalam alaykum malam tambaya ta shi ne mene ne hukuncin wanda yake leqa mutane (musamman ma 'yan mata) yayin da suka shiga bayan gida domin wanka ko kama ruwa? Na gode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Babu shakka wannan haramun ne. Kuma duk wanda ya
aikata haka tabbas ya cika azzalumi kuma fasiqi ta hanyoyi kamar haka :
1. Yin haka, leken tsaraicin jama'a, Qetare
iyakokin Allah ne kuma Allah ya ce : "Wanda ya saɓa wa Allah da ManzonSa kuma ya Qetare iyakokinsa, Zamu
shigar dashi cikin wata wuta wacce zai dawwama acikinta, kuma azaba mai
wulakantarwa ta tabbata gareshi". Awani wajen kuma Allah ya ce "Wanda
ya qetare iyakokin Allah, hakika ya zalunci kansa".
2. Yin haka yana daga keta alfarmar musulmi da
kuma mutuncinsa. Gashi kuma Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce :
"Dukkan musulmi akan musulmi, haramun jininsa da dukiyarsa da mutuncinsa.
3. Wannan laifin ya shafi kallon al'aura da
tsiraicin mutane. Kuma Imamuz Zahaby acikin kitabul Kaba'ir ya kawo hadisin
dake nuna Allah ya tsine wa mai kallo da wanda ake kallon (Wato Allah ya tsine
wa mai kallon tsaraici, da kuma wanda ke bayyanar da tsaraicinsa domin arika
kallo). To kaga anan su waɗanda ake kallo ɗin, ba da son ransu ake kallon nasu ba. Hasali ma basu
bayyanar da tsaraicin ba. Don haka tsinuwar ta tattaru ne akan wannan dake
kallon nasu aɓoye.
4. Leqen tsaraicin Muminai cutarwa ce garesu kuma
Allah ya ce : "wadannan dake cutar da muminai maza da muminai mata sannan
basu tuba ba, to azabar jahannama ta tabbata garesu, kuma azabar quna ta
tabbata garesu".
Amma idan ya zamanto akwai makobtaka atsakaninsu,
to anan ne laifin kuma yafi girma domin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam
ya ce : "Duk wanda Makobcinsa bai tsira daga sharrinsa ba, bazai samu
shiga Aljannah ba" (imamu muslim ne ya ruwaitoshi).
Sannan daga karshe idan an kama irin Waɗannan mutane wajibi ne akaisu ga hukuma mafi kusa domin ɗaukar matakin da ya dace akansu.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.