Citation: Bunza, A.M. (2025). Gurɓacewar Al’adun Hausawa, Ɗabi’unsu Da Halayensu a Ƙarninmu. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 4(1), 14-23. www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i01.002.
GURƁACEWAR AL’ADUN HAUSAWA, ƊABI’UNSU DA
HALAYENSU A ƘARNINMU
Daga
Aliyu
Muhammadu Bunza
Department of Nigerian Languages
Usmanu
Danfodiyo University
Sokoto, Nigeria
mabunza@yahoo.com
08034316508
Tsakure
Al’ada Balarabar kalma ce da a
sakamakon zamantakewa ko saduwar Balarabe da Bahaushe ta samu a harshen Hausa. Al’adunmu sun samu sauyi daga addinan da suka riski ƙasarmu guda biyu (Kiristanci da Musulunci). Haka kuma, sun gurɓace sanaddiyar Mulkin Mallaka da
karatun Boko. Wayewar kan zamani na hanyoyin sadarwa na baka da rubutattu sun sa
masassara ga al’adunmu. Cigaban mai ginar
rijiya na hanyoyin sadarwa na ga-ni-ga-ka na rediyo mai hoto da finafinai, da
wasannin kece raini da batsa sun yi wa al’adunmu rauni babba. Shirye-shirye da
tsare-tsaren wayoyin hannu sun mayar da gaba baya; sun gurɓatar da kyawawan al’adunmu, muka
koma gaba kallo baya da mamaki. Babban abin da ya kyautata al’adunmu na gado
shi ne “gaskiya” abin da ya gurɓatar da su shi ne “ƙarya”. Ga alama, dabarar da muka
fara yi ta leƙon al’adunmu na shekaranjiya, da shekaranjiya ban da
jiya, domin gyara su a yau domin amfaninmu jibi da gata, su ne kaɗai dabarun gyaran gurɓatacciyar al’ada da inganta ta.
Gabatarwa
Hausawa mutane ne da suka mamaye
duniyar ɗan Adam ga harshensu, sana’o’insu, zamantakewarsu, sarautunsu, da fasahohinsu. Daga cikin abubuwan da suka ɗaukaka Hausawa nan duniya akwai: Harshensu,
da ɗabi’unsu, da ƙwazonsu na kare kansu da al’adunsu. Yadda ƙwazonsu ya ɗaukakar da su, aka san su a duniyar kowane zamani shi ya sa har yanzu ana
koyi da su wajen neman cigaba ga kowane abu ake fuskanta a duniyar zamaninmu. Wannan
ya sa duk abin da ya gurɓata duk wata hanyar ɗaukakar Bahaushe Hausawa na damuwa da shi, da ƙoƙarin jawo hankalin Hausawa a tabbata musu daga na gaba ake gano zurfin ruwa. Duk al’ummar da ba ta kula da sakarkacewar kyawawan al’adunta saboda sauyawar lokaci da
zamani ba, ta taimaki kanta ga cigabanta da gudunmuwar magabatanta
ba, tana cikin ƙalubale. Bisa ga irin wannan misali halayyar da al’adun Hausawa
suke ciki a yanzu sun cancanci a nazarce su, a ga yadda za a fuskance su domin
a ci ribar abubuwan da aka gada kaka da kakani.
Ma’anar
Al’ada
Na so in ɗan taɓo ita kanta kalmar “al’ada”. Abin
sani shi ne, kalmar ba ta Hausa ba ce, ta Larabci ce. Abokan zama da dama, da
manazarta, idan an tattauna da su kan ma’anar “al’ada” za a ji sun ce:
a.
Halayyar rayuwa
b.
Ɗabi’un mutane
c.
Ayyukansu na al’ada da sauransu
Ga alama, kalmar da Hausawa suka fara amfani da ita
a kan “al’ada” ita ce “gado”. Wataƙila saboda tsoron fassarar da waɗanda ake yi wa ita rashin fahimta shi ne ya sa aka fassara ta da “al’ada”.
Gabanin Hausawa da baƙin al’ummomi da addinai da harsuna daban-daban za mu ji
Hausawa na faɗar:
a.
Ƙira ya yi gado
b.
Masunci ne ga gado
c.
Bakano ne ga askar gado
d.
Ai gadon Musulunci ya yi
e.
Hausawa ba su gaji ƙarya ba gaskiya suka gada.
A taƙaice, za mu iya cewa:
Al’ada ita ce wasu abubuwa da muka
gada kaka da kakanni. Sukan iya kasancewa dabarun zamantakewa, ko ayyukan aure,
suna, da mutuwa. Haka kuma, yakan kasance abubuwan da aka gaji dokokin yin su,
ko ƙaurace musu, ko jin kunya ga aikata su, ko samun godiya
ga aikata su. Ana gano al’ada daga bakin masu ita ko ayyukansu.
Wane
ne Bahaushe?
Gabanin mu leƙo al’adun mai al’adu, a al’adance ya fi dacewa mu san shi da bayyana yadda
za a gane shi ko ga wanda bai san shi ba ne. Fitattun masana Hausa, da Tarihi,
da Addini, da Ilmin Harsuna, da sauransu sun yi ƙoƙari a fannonin ƙwarewarsu su fayyace wane ne Bahaushe? Ƙoƙarin da suka yi shi ya ba da damar
samun shafukan sake bitar ayyukansu da hanyoyin da ba su faɗaɗa ba a nazarce-nazarcensu. A taƙaice, za mu ce, duk wani ilmin gano wane ne Bahaushe? Dole sai ga Bahaushe
za a iya gano shi a kuma tambaye shi tushensa da asalinsa. Zancen da zai fito daga bakin mai abu ya fi na kowa dacewa. Dr.
Ibrahim Narambaɗa ya tabbatar da cewa:
Jagora: Ko an so ko da ba a so ba,
: Mai abu dai shi adda abinai.
Gindi: Shiri bajinin Mamuda,
:
Abu na Namoda tsararre.
Bisa ga bitar binciken da masananmu
suka yi za mu iya cewa:
a.
Bahaushe shi ne wanda ya yarda da Bahaushe ne kuma yana bugun gaba da zama Bahaushe
b.
A samu ga iyaye da kakani duk Hausawa ne
c.
Ba ya bugun gaba da wata ƙasa in ba ƙasar Hausa ba
d.
Yana da karin harshe daga cikin karuruwan harshen Hausawa
e.
Idan an same shi da askar fuskar Hausawa ya tabbatar da iƙirarinsa
f.
Samun sa baƙar fata dole ne, kasancewarsa farar fata ya ɓata dukkanin matakai (v) da suka
gabata.
Ina
ne Ƙasar Hausa?
Ƙoƙarin gano ƙasar Hausa zai taimake mu gano ina
al’adun Hausawa da ɗabi’unsu suka mamaye da kuma yadda gurɓacewar wasu daga ciki ya kasance. A
taƙaice, ƙasar Hausa ƙasa ce da take da ƙasashe manya da suka tabbatar da
zamanta babbar farfajiya bisa ga kasancewar:
a.
Kano ƙasar Kanawa mai cibiya Kano
b.
Gobir ƙasar Gobirawa mai cibiya Sabon Birni
c.
Kabi ƙasar Kabawa mai cibiya Argungu
d.
Katsina ƙasar Zagezagi mai cibiya Zariya
e.
Zamfara ƙasar Zamfarawa mai cibiya Anka/Gummi/Gusau
f.
Yawuri ƙasar Yawurawa mai cibiya Yawuri (daga Birnin Yawuri)
g.
Daura ƙasar Daurawa mai cibiya Daura
h.
Maraɗi ƙasar Maraɗawa/Arawa mai cibiya Maraɗi
i.
Damagaran (akwai maganganu da yawa a kanta)
Waɗannan su ne ƙasar Hausa wurin da Hausawa suka kafa garuruwan da suke cibiyi ko su
Hausawan ke sarauta ko harshensu ya mamaye harsunan da aka tarar a nan. To, mun
ga Bahaushe da ƙasarsa sauran harshensa domin mu san yadda ake furta shi, ya aka gado shi, wannan kaɗai ya isa gano harshen Hausawa na asali.
Yaya
Harshen Hausa Yake?
Bahaushe ga al’adarsa shi ya sa wa
Hausa sunan harshen “Hausa”. Mai gadon harshe ya kira shi “Bahaushe”. Furucin
magana da harshen a ce mishi “Hausa”. Fassarar wani harshe zuwa harshensa ya ce
masa “Hausantawa”. Farfajiyar da sarakunan Hausa suke sarauta a ce mata “ƙasar Hausa”. Wanda ya zauni ƙasar Hausa ba ya jin harshen Hausa a kira shi da sunan “Ba Hausa”. Hausa
harshe ne mai gajerun kalmomi da jimloli da keɓaɓɓun kalmomi ga sana’o’i da wasanni.
Ga alama ya fi sauran harsuna da ke kusa da shi ƙirar wasali da baƙaƙe. Ga ɗan misali kamar haka:
a.
Wasula: a, i, o, u, e.
b.
Wasula biyu: ai, au, ui, iu (da wuya a same su ga wasu harsuna)
c.
Tagwayen baƙaƙe: kw, gw, gy, ts, ky, sh, fy
d.
Tagwaye masu ƙugiya: ƙy, ƙw
e.
Baƙaƙe masu ƙugiya: ɓ, ɗ, ƙ, ‘y
f.
Baƙaƙen karin harshe: ɗw, tc, tw, dw, rw, lw, hy, nw, sw
Kaɗan ke nan daga cikin haruffan da Hausa take da su da masana harshe na gado sai ‘yan harshen na asali ke iya furta
su sosai. Haka kuma, daga cikinsu ake iya rarrabe karuruwan harshen Hausa.
Zamunan
Ƙasar Hausa
Masana tarihi, da Hausa, da sauran ilmuka suna da irin kallon da suke yi wa zamunan ƙasar Hausa domin yin ƙoƙarin rarrabe yadda al’adu da ɗabi’un Hausawa suke juyawa daga wani zuwa wani wuri na cigaba ko faɗuwa, ko gurɓacewa. Yadda ƙasar Hausa take, za a ga zamunan da ta shimfiɗu ciki su ne:
1.
Zamanin farko: ɓullarsa, bayyanarsa da kafuwarsa
2.
Zamani na biyu: hulɗa da wasu ƙabilu makusanta
3.
Zamani na uku: haɗuwa da ƙabilu manisanta
4.
Zamani na huɗu: zamanin addinin Annabi Isa (AS)
5.
Zamani na biyar: zamanin addinin Musulunci
6.
Zamani na shida: zamanin mulkin mallaka
7.
Zamani na bakwai: Boko da wayewar kai
Kowanne daga cikin waɗannan zamuna bakwai da ƙasar Hausa ta ratsa ko suka ratse su akwai wasu al’adu da suka ci gaba
da rayuwa, ko rage ƙarfi, ko masassara, ko rugujewa, ko taɓarɓarewa ba da sani ba, ko da sanin da
ba a hango makircin da yake ciki ba. Zamanin farko fari ne fes daga Bahaushe
sai Bahaushe. Zamani na biyu an sadu da Fulani, Dakarkari, Zabarmawa, Kyangawa,
Adarawa, da sauransu. Zamani na uku, saduwa da Larabawa, Kanuri, Yoruba,
Nufawa, Bambara da Shonghai (Mali), Asanti (Ghana) da sauransu. Zamanin addinin
Annabi Isa (AS) an sadu da Arawa da Kyangawa. A zamanin da addinin Musulunci a ko’ina ya shiga ƙasar Hausa. Idan muka dubi zamani
na shida na mulkin mallaka da zamani na bakwai na Boko da wayewar kai, nan
maganganun da muke son mu faɗaɗa bincike suke.
Makarantun
Ilmin Hausawa na Farko
Duk wani bincike, da karatu, da
rubuce-rubucen da za a yi kan gurɓacewar al’adun Hausawa, da ɗabi’unsu, jiya da yau dole sai sun leƙo waɗannan makarantu za a tabbatar da su, ga makarantun:
1.
Tatsuniya
2.
Karin magana
3.
Salon magana
4.
Kirari
5.
Baƙar magana
6.
Waƙoƙin yara na baka
7.
Waƙoƙin zanga-zanga (na yara)
8.
Waƙoƙin yaƙe-yaƙe (na gari)
9.
Waƙoƙin aure (na yara)
10.
Waƙoƙin bukukuwa (yara da manya)
11.
Waƙoƙin mutuwa (na manya)
12.
Waƙoƙin daka (na mata)
13.
Waƙoƙin kishi (na mata)
14.
Waƙoƙin talla (na masu sana’a)
15.
Waƙoƙin baka (na manyan maza da manyan mata)
Waɗannan waƙoƙin da wasu nassoshin magana na Hausawa tun gabanin
zamani na biyu Hausawa ke da su, kuma a nan aka ɓoye kyawawan ɗabi’u da ake hardacewa domin ganin
an yi nasarar ɗabi’u na kirki da aka gada kaka da
kakani.
Kyawawan
Ɗabi’uƘyawawan
Ɗabi’u na Kirki da Aka Gada Kaka da
Kakanni
Manyan littattafan da aka karanta
ko aka hardace a makarantunmu na gado sun haɗa da:
1.
Goyon bayan gaskiya da aiki da ita
2.
Nisantar ƙarya da faɗa da ita
3.
Rowa da nisantar tanisantarta
4.
Kyauta da kusantar ta
5.
Ɓanna da illolinta
6.
Tsaro da dabarar yin sa
7.
Haɗin kai da hidimarsa
8.
Girmamar da gabaci da magabata
9.
Kawar da laifukan sata da ƙazantu
10.
Kyautata ƙwazo da rushe ragganci
11.
Zumunci da muhimmancinsa
12.
Inganta harshe da adabinsa
13.
Tattalin arziki da muhimmancinsa.
Kaɗan ke nan daga ƙunshiyar abubuwan da muka tarar ga magabata, a yau suna batun ɓata mun kasa mu tsaya mu yi gyara.
Magabatanmu sun san wannan gurɓacewa tun gabanin bayyanar ta a wannan zamani namu na
cigaban ginin rujiya. Ji wannan saƙo ga Dr. Makaɗa Ibrahim Narambaɗa:
Jagora: Na hore ki gaskiya bari tsohon ƙarya,
Yara: Mai ƙarya munahuki Allah su yaƙ ƙi,
Jagora: Har yau ba mu ga in da an ka bi mai ƙarya ba,
Yara: Amma ita gaskiya gari da mutane tay yi,
Gindi: Gwarzon Shamaki na Malam toron giwa,Toron Giwa
:
Baban Dodo ba a tamma da batun banza.
A Bahaushiyar al’ada, babu abin da kan gyara mutane da al’adunsu, da
addininsu, da zamantakewarsu, da tsaronsu, da cigabansu, da cin nasararsu, da ɗaukakarsu, sai gaskiya. Tunanin
Bahaushe ya yi canjas da na sauran al’ummar duniya. Wanda duk ya ɗaukaka a duniya za a ga gaskiya ce
ta ɗaukaka shi. Babu abin da ya gurɓata muna al’adunmu na gargajiya a
yau illa ƙin ba gaskiya goyon baya. Dubi yadda karuruwan maganarmu
na gyara muna al’adun zamantakewa da irinsu:
-
Gaskiya ina laifinki
-
Gaskiya mai korar ƙarya
-
Gaskiyar faɗa harsashe
-
Gaskiya dokin ƙarfe
-
Gaskiya sunan ta gaskiya
-
Gaskiya a ƙi ki, a so ki
Bin gaksiya ya ɗaukaka sarakunan da suka gina ƙasar nan, da gwarazanmu, da
jagororinmu. Yau saɓa mata ya ɓata shugabancinmu na sarauta, da addini, da ilmi, da siyasa.
Ƙarya
Al’adunmu sun ƙi ƙarya, sun ƙi masu yin ta, ba su yarda hulɗa da ita da masu yin ta ba. A al’adance, duk wurin da ƙarya ta kutsa taɓarɓarewarsa ta tabbata. Ai don haka ne magabatanmu ke cewa:
-
Ƙarya fure take ba ta ɗiya (‘ya’ya)
-
Ramin ƙarya ba ya da zurfi
-
Gaskiya mai korar ƙarya
-
Ƙarya aka yi wa rijiya, ruwa na gulbi
Makaɗa Aliyu Ɗandawo ya jawo hankalinmu ga matsalar ƙarya a faɗarsa da yake cewa:
Jagora: Mai kurin biɗan faɗa
Yara: Bana an ba shi kashi
Jagora: Har na zaburo rabo
Yara: Sai naj ja da baya
Jagora: Nat tuna ƙaryar da yay yi min
Yara : Gara a ba shi kashi.
Gindi: Bai ɗau wargi ba Audu,
: Mu je mu ga Madawaki.
Makaɗa Dr. Ibrahim Narambaɗa ya tabbatar mana damuna cewa ƙarya tana gurɓata komai na rayuwa, da addini, da iko, da sarauta, da
siyasa, balle al’adunmu na gargajiya, ji yadda saƙonsa yake:
Jagora: Na bar ƙarya ko ina kiɗi,
: Na wuce ƙarya ko ina kiɗi,
: Nai sittin saba’in nika hwaɗa,
: Mai saba’in yai ƙarya,
: Ana ta zunɗe nai,
Yara : Ko yaran da ag garai,
: Duk wawwatce mishi sukai,
: Shina yawo shi ɗai ɓarau-ɓarau.
Gindi: Ya ci maza ya kwan yana shire,
: Gamda’aren Sarkin Tudu Alu.
Koyon gaskiya da nisantar ƙarya su ne al’adun da Hausawa suke
koyar da yara su, a girma cikin saninsu sai a ɗaukaka a ɗaukakar da al’ada. A
kula, al’adar gaskiya, tana cikin tatsuniya, karin magana,
salon magana, waƙe-waƙen yara da manya. Duk wani cigaba
da aka samu na rayuwar al’ada gaskiya ta taimaka aka yi, cikas da aka gani
cikin gurɓacewar al’adunmu a yau ƙarya ta cutar da mu.
Kyauta da Rowa
Gaskiya ta taimaka wajen inganta kyauta har Hausawa da al’adunsu suka
rinjayi wasu al’ummomin da ke tare da su. Ai gaskiya ta koyar da kyauta ga ‘yan
uwa, da iyalai, da abokan zama gaba ɗaya. Kyauta tana
inganta tsaro da tattalin arziki, da haɗin kai, da cigaban al’umma. Dubi
yadda Alhaji Gambo Fagada mijin Kulu ya kalli kyauta:
Jagora: Kyautar mai kuɗi yar taƙi ta,
: In an yi bukin dangi yanai ma,
: In an yi bukin salla yanai ma,
: Amma a ba ka yau, a ba ka gobe,
: Kuma jiɓi a ƙara ba a gaza ba,
: Wallahi ɓarawo ɗai ka yin haka,
: Ba da abinai na shi kai ba.
Ya tabbatar da cewa, Hausawa suna da al’adar kyauta ta fitar da ‘yan’uwa da abokan hulɗa ga wahala da rashi. Almubazzaranci
kuwa ƙarya ta haddasa shi, domin ta kore kyautar da gaskiya ta
turo. Tsofaffin taskokin adabi na baka da ƙasar Hausa ta fara amfani da su, su
suka bai wa mawaƙan kowane fanni kayan aiki da suke amfani da su ga aiwatar da waƙoƙinsu kuma da abubuwa biyu aka yi amfani da su, “gaskiya” da
“ƙarya”. Duk wata hanyar rayuwa su ne manya a ciki.
Dangantakar
Al’adu da Addinai
Ga ƙolin binciken addinan da suka rayu ƙasar Hausa akwai na gargajiya da na Kirista da kuma addinin Musulunci da yake kan gaba. Na gargajiya babu takamaiman lokacin faruwarsa, sai dai a ce lokacin da ƙasar Hausa ta bayyana a bangon ƙasa. Addinin Kiristanci daga Masar ya fara kutso kai tun zamanin kasuwanci
da sarautar Gobir da wasu sassan Gobir da Maraɗi. Addinin Musulunci kuwa ya yi shekaru da yawa da
bayyana tun wajajen ƙarni na sha uku (13ƙn), wasu na ganin tun bayyanar
Manzo (SAW). Duk yadda waɗannan abubuwa suka kasance sun yi ɗan tasiri cikin al’adun Hausawa, har wasu al’adu suka gurɓace. Babban abin nufi sun yi tasiri ga:
1.
Matakan rayuwa uku: aure, haihuwa da mutuwa
2.
Tasiri a rayuwar bauta musamman a kan bori da tsafi
3.
Sun yi tasiri a tsarin abubuwan ci da sutura
4.
Sun yi tasiri a rayuwar ladabi da biyayya na gargajiya wasu sun rushe wasu
an yi gyara
5.
Sun yi tasiri a kan tsaro da ƙirƙiro dokokin zaman lafiya
6.
Sun yi canjaras ga gurbin gaskiya
7.
Sun haɗu tangam a kan gano ƙarya da ƙin ta.
Saukakkun addinai da suka sauƙa a ƙasar Hausa sun tsawatar a kan sata,
da yaudara, da zina, da shaye-shaye, da cunkoson mata da maza, da kisan kai, da
yaƙe-yaƙe. Addinan sun yi tasiri a kan
al’adun tsage-tsagen fuska,
da tsiraici da yin kaciya ga maza da mata, da barin gemu da saje, da auratayya
musamman mata fiye da ɗaya. Tabbas! Al’adun da suka saɓa wa aƙidar addinin Musulunci, addinin Musulunci ya hana su yaɗuwa ga masu addinin sai aka kawar
da su.
Al’adun
Kyautata Zamantakewa
Ƙasar Hausa tana da tarihin yaƙe-yaƙe da yawa musamman in an dubi daular Kabi, da Gobir, da
Kano, da Katsina, da dai sauransu. Ƙulla yaƙi da aiwatar da shi lalata tsaro ne da zaman lafiya. Don haka al’ada ta zo
da wasar kore yaƙi da gaba mai suna “Tobasantaka”. Dubi wasan Katsinawa
da Zagezagi, da ta Gobirawa da Fulani, da ta Kabawa da Fulani da dai sauransu.
Da wasar tobasantakan jini, da ta ‘yan masu sana’ar da suka yi takin saƙa kamar mahauta da masunta. Yau tobasantakar dogo da gajere, takwaranci,
kaka da jika, malamai da bokaye, auren zumunta da ire-irensu sun fara rafashewa
saboda wayon cewa, wai an waye sai ɗabi’unmu na haɗin kai suke lalacewa. Dubi satar ‘yan’uwa ada ɗora kuɗin fansa, sanya da sa makamai a halaka abokan zama, ya haifar da wata
sabuwar musiba da ta haifar da gaba tsakanin al’umma, musamman a arewacin Nijeriya.
Kafofin
da Suke Gurɓata Al’adunmu da Lalata
Su
Kafofin da suka fara yi wa
al’adunmu ɓarna da gurɓatar da mu, ba mu kaɗai suka shafa ba; har sauran ƙabilunmu na Nijeriya sun shafa. Wasu abubuwa kamar don cigaba aka tarbe
su, suka haifar da koma baya kamar:
1.
Karatun boko
2.
Kafofin yaɗa labaranmu na waje
3.
Kafofin yaɗa labarai na cikin gida
4.
Ƙungiyoyin wasannin kwaikwayo
5.
Ƙungiyoyin rawa da waƙe-waƙe
6.
Cibiyoyi finafinai
7.
Litttafai da mujallunmujallu na wasannin da ba
al’adunmu ba, amma ana gudanar da su da harshenmu
8.
Ƙungiyoyin waƙe-waƙe da raye-rayen jam’iyun siyasoshi
Haɗa al’ummomi da yawa tare da gudanar da wasanni cikin harshenmu da al’adunmu
Waɗannan abubuwa (9) su suka fara taɓa al’adunmu aka fara gurɓata su sannu-sannu, har muka wayi
gari yau cikin injimomin kwamfuta da wayoyin hannu da suka game duniya aka fito
da hanyoyin sadarwa na:
1-
Facebook
2-
Instagram
3-
Whatsapp
4-
Tiktok
5-
Tik-tok
6-
Snap chat
7-
You tube
8-
Twitter
Babu wani hoto, da aiki, da labari,
da tattaunawa, da kiɗa, da rawa, da waƙoƙi, da hulɗoɗin mutane, da yaudare-yaudare, da
babu a cikinsu. Sun gurɓatar da ingantattun al’adunmu sun
sa mu koyon miyagun al’adu. A cikin waɗannan hanyoyin an koyar da yaranmu
maza da mata:
1.
Shaye-shaye
2.
Tsiraici
3.
Ƙarya da yaudara
4.
Kisan kai na gayya
5.
Koyar da sace-sace
6.
Rashin ladabi da biyayya ga ma’aurata
7.
Keta haddodin addinanmu
8.
Koyar da yara bore da zanga-zanga
9.
Gina ƙiyayyar ƙabilanci
10.
Cire ɗa’ar yara ga iyayensu
11.
Mayar da ƙarya wata makarantar kanta.
A cikin waɗannan shirye-shirye aka raunanar da
ɗa’a tsakanin ma’aurata a fito da ‘yancin mace fiye da na miji. A sakamakon
haka, a Kaduna sarakuwa ta sayar da kanta ga ‘yan ta’adda don a yi wa mijin ɗiyarta tara ya tsiyace a sake
kishiyarta. A Katsina, an nuna yaron da ya sayar wa ‘yan ta’adda mahaifiyarsa.
Haka aka nuna yaron da ya kashe mahaifinsa a Bauchi ya ce, ya yi haka ne domin
mahaifinsa ya samu shahada. A Neja yaro ɗan shekara (25) Abubakar Muhammad
ya biya abokinsa (N110,000) su kashe mahaifinsa domin ya gaji dukiyar mahaifin
mai yawa. Mahaifin ɗan shekaru hamsin da biyu (52) ne, kai tsaye aka kashe shi. Haka
yaro ɗan shekara (23) ya kashe mahaifinsa a jihar Delta. Waɗannan bala’o’in duk cigaban zamani da waɗancan shirye-shirye ya haifar da
su.
Shirye-shiryen sun ci nasarar cire
wa matanmu al’adun jin kunya. Neman aure, da son aure, da ɗaura aure, da bukin aure, da kai
amarya, da sada ta da ango, da hanyoyin ciyarwa, da shayarwa, an ɗebe al’adunmu. Ga al’adar Bahaushe, mata ba su sa
wando a matsayin suturar ƙasa, ba su sa hula, ba su sa
riga bale tagguwa, ba su ƙawata fuska, ba su ƙawata yatsu da zobba. Yau sun koma kamar matan Indiyawa da Romawa. Mace da
miji ba sa faɗan sa-in-sa gaban mutane, yau finafinanmu sun rusa wannan al’ada. Ladabin
gaisuwa, da barka, da ban kwana, na matan Hausawa iri ɗaya na girmama maza. A yau, TikTok da
Istagram da Feacebook sun gurɓace muna al’ada. Da za mu yi nazarin waɗannan labarai za mu tabbatar da zamani ya illantar da al’adunmu:
-
Rufin kan uwar daɗi
-
Gaba kallo baya da mamaki
-
Gwamma a bakin Ɗangambara
Rusar da kunya ga idanunmu musamman
matanmu shi ne babbar yaudarar zamani ga ɓata kyawawan al’adunmu. Abin ban
tsoro shi ne, da maƙiya sun ci nasarar kore kunya ga matanmu tarbiyar yaran
da za a haifa ta taɓarɓare, al’umma kuwa ba ta san ƙarshen makomarta ba. Yaudarar da
muka yi wa ma’abota al’ada managarciya ita ce, a tura musu al’adar da ba tasu ba wadda ta keta dokokin al’adunsu a ce, ita ce wayewa sai a rungume ta hannu biyu.
Musabbabin
Gurɓacewar Al’adunmu
Babu al’ummar da masassarar al’ada
bai shafa ba, hatta masu iƙirarin su ne wayo kuma gare su wayo
ya fito. Duk da haka a wajenmu Hausawa manya abubuwan da suka gurɓace al’aunmu su ne:
1.
Mulkin mallaka
2.
Ilmin boko
3.
Ƙungiyoyin siyasa
4.
Finafinan da, da na yanzu
5.
Kafofin yaɗa labarai na baka da rubutattu
Turawan mulkin mallaka a ko’ina
suke al’adunsu ne halartacciya wadda ta yi taƙin saƙa da ita haramtaciya ce matuƙar ba ta yi maraba da su ba. Ilmin Boko na ‘yan mulkin mallaka ne, ai da
shi aka tsara tsarin mulkinmu da al’adunsu ya mamaye. Ɗan boko Hausawa sun ce, mai ganin uba nai wawa. Na bar masu karatu da
fassara, siyasar ƙasarmu ta game dukkanin ƙabilar da ke cikin ƙasa. Kowane ɗan ƙabila ya samu shugabantar ƙasa da al’adunsa yake mulki
talakawa su fara aron su. Finafinai tun fitowarsu ya zuwa yau, al’adun wasu ake
talla don su shiga zuciyar al’adun waje suke talla. Na cikin gida kowa takansa
yake yi kuma sun rinjaye Hausawa yawa. Dalilai na sama biyar duka, daga na
(2-5) na (1) ne ya haddasa su. Gaskiyar yaran ƙasar Hausa da ke waƙar:
Jagora: Kai ku ɗaga ga ɗan doka,
‘Yan Wasa: Ba mu gudu sai mun ga Nasara.
Jagora: Jar hula ba iko ce ba,
‘Yan Wasa: Ko rawani ba iko na ba.
A taƙaice sun tabbatar da mu cewa,
mulkin mallaka ya karɓe komai ga hannun sarakunanmu da ‘yan dokarsu (masu jar hula) da su masu rawuna. Ashe tushen suturarmu na iko su ne hula
da rawani da riga don rusa wannan al’ada Turawa suka ƙago kayan aiki na mata da maza iri ɗaya da ‘yan sanda, da soja, da duk
masu aikin tsaron ƙasarmu. Wane Bahaushen asali zai yarda da ɗiyarsa, ko matarsa, ko uwarsa, su
sa wandon aiki, da ‘yar riga, ɗuwawu da nonna suna jijjiga gaba suna fassarar taho na
shirya?
Hanyoyin
da Za a Farfaɗo da Al’adunmu
Babu Bahaushen da zai musanta cewa, ba a zalunci Hausa a al’adance ba. A tarihance yau 2025 muna da
shekara 65 daga samun mulkin kai da aka ba mu 1960. Kasancewarmu shekaru 65 ƙarƙashin maƙiyanmu ba mu san iya cutuwar da aka
yi muna ga al’adunmu ba. Haka kuma, ba mu iya fayyace irin gurɓacewar da al’adun suka yi ba. A
al’adance, Hausawa ba su da gajeren wondo, sai dai kirshe da yaba ko warki da
zai rufe jiki zuwa guiwa tun gabanin kowane addini a ƙasarmu. Turawa suka kawo gajeren wando da Hausawa suka ƙi. Dubi waƙar mayaƙan Satiru 1906, a ƙasar Boɗinga, Ɗancaɗi da Satiru suna waƙa:
: Waziri ya daɗe bai zaka ba,
: Marafa ya daɗe bai zaka ba,
: Balle Nasara mai ɗan wando,
: Babban mutum da wandon yara,
: Ku sa kiɗi mazaizai mu gani,
: Ko can gida faɗa munka sani,
: Ba mu san gudu ba sai dai a mutu.
Don haka babbar hanyar kare
al’adunmu da farfaɗo da su da ɗaukaka su ita ce inganta karatun Hausa. Na biyu, kiran taron ƙara wa juna sani. Na uku, shi ne, inganta al’adunmu musamman na sana’o’i.
Na huɗu, a sa dokokin haramta shigo da finafinan batsa da ta’addanci kamar yadda
Russia da Saudiyya suka yi. A nan Nijeriya, jihar Kano ta fara kafa irin wannan
doka.
Sakamakon
Bincike
Bincikenmu ya tabbatar da cewa,
al’ada wata babbar ɗabi’ar rayuwa ce ta kowace al’umma. Duk da kasancewar sunan “al’ada” Larabci
ne da ya taushe na Hausa “gado” za mu ce:
a.
Mulkin mallaka ya haddasa duk wani abu da ya taɓi al’adunmu, kuma ba a daina ba har
yau (2025).
b.
Taɓarɓarewar al’adunmu matasa ya fi mamayewa tsofaffin da suke rage da sun wuce an gama da mu.
c.
Ƙabilancin ƙabilun da Hausa ta haɗe harshensu, da waɗanda ta fi yawa, da wanzuwa, na daga cikin abubuwan da
suka janyo gurɓacewar al’adunmu.
Naɗewa
Hausawa sun ce, ba a san maci tuwo
ba sai miya ta ƙare. Al’adunmu su ne, harshenmu, halayyarmu, ayyukanmu
da muka gada kaka da kakani, tunaninmu da hangenmu da suka bayyana a adabinmu.
Babu shakka, duk al’ummar da take bangon ƙasa yau, al’adunsu na gado masu yawa sun ɓata, wasu sun gurɓace, wasu ko suna nan suna kai da
kawo. Abin da ya kyautu shi ne, mu yi tunanin gina harshenmu da koyar da ilmi
cikinsa kamar yadda ake yi a ko’ina duniya ba aron harshen Ingilishi da
Faransanci a makarantunmu ba. Su me ya hana su aron wani harshe su koyar
da yaransu? Ai cikin harsunansu ne suka turo muna abubuwan da suka yi wa
al’adunmu alaƙaƙai. Wani fitacen mawaƙin tashe a ƙauyenmu yana cewa:
Jagora: Sai dai a hi mu kalangu da kurkutu,
Yara: Amma ba a hi mu daɗin baki,
Gindi: Bori goje kana da borin
tashe.
Manazarta
Adam, Y. M. (Ed.). (2021). Hausa prose-fiction: A reader.
Kano: Bayero University Press.
Adamu, A. U., Yusuf, M. A., &
Umar, F. J. (Eds.). (2004). Hausa
home videos: Technology, economy and society. Kano: Centre for
Hausa Cultural Studies.
Adamu, M. (1975). Hausa factor in West African history.
Zaria: Ahmadu Bello University.
Adamu, M. (1980). The Hausa and other
peoples of Northern Nigeria, 1200-1600 A.H. Seminar
paper. Zaria: Ahmadu Bello University.
Adamu, M. U. (2011). Sabon tarihin asalin Hausawa.
Kaduna: Espee Printing and Advertising.
Ajayi, A. S., & Fabarebo, I.
(2009). Oral traditions in
Black and African culture. Lagos: Centre for Black and African Arts
and Civilization (CBAAC).
Alao, A. (Ed.). (2011). Politics, culture and development in
Nigeria: A Festschrift for Gabriel Olatunde Babawala. Lagos: Centre
for Black and African Arts and Civilization (CBAAC).
Al-Hajj, M. (1968). A
seventeenth-century chronicle on the origins and missionary activities of the
Wangarawa. Kano Studies, 4.
Alkali, B. (1968). Hausa community in crisis: Kebbi in
the 19th century (Master’s thesis). Ahmadu Bello University, Zaria.
Augi, A. R. (2021). The Gobir factor in the social and
political history of Rima Basin (c. 1650 to 1808 A.D.). Makurdi:
Aboki Publishers.
Bello, A. (1992). The dialects of Hausa.
Fourth Dimension Publishers.
Bunguɗu, H. U. (2022). Waƙoƙin Amali Sububu. Zaria: Ahmadu Bello University
(Supported by Tetfund).
Bunza, A. M. (2002). Yaƙi da rashin tarbiyya, lalaci, cin
hanci da karɓar
rashawa cikin waƙoƙin Alhaji Muhammadu Sambo Wali
Basakkwace. Lagos:
Ibrash Publishers.
Bunza, A. M. (2005). The place of
culture in national development. Paper
presented at the First Convocation Ceremony, Adamu Augi College of Education,
Argungu.
Bunza, A. M. (2006). Gidan Gadon Feɗe Al’ada. Lagos: Tiwal Publishers.
Bunza, A. M. (2009). Narambaɗa. Lagos: Ibrash
Publishers.
Bunza, A. M. (2010). In ba ka san gari ba saurari daka:
Muryar nazari cikin tafashen gambo. Cairo: Elkods Printing House.
Bunza, A. M. (2023). Hausa a matsayin
harshen uwa a farfajiyar karatun boko. Biram
Journal of Contemporary Research in Hausa Studies, Maiden Edition.
Kafin Hausa: Jami’ar Sule Lamiɗo.
Bunza, A. M., Ibrahim, S. S., &
Usman, B. B. (Trans.). (2007). Daular
Sakkwato (M. Last, Author). Lagos: Ibrash Publishing Company.
Dokaji, A. A. (1978). Kano ta Dabo Ci Gari.
Zaria: NNPC.
East, R. M. (1932). Labaran Hausawa da maƙwabtansu. Zaria: NNPC.
Farguson, D. E. (1973). Nineteenth-century Hausaland: Being a
description by Imam Imoru of land, economy, and society of his people
(PhD thesis). University of California.
Haroun, K., & Nasiru, A. (Eds.).
(2022). Women and their
contribution to Hausa society. Katsina: Alqalam University.
Ibrahim, M. S. (1982). Dangantakar al’ada da addini
(Master’s thesis). Bayero University, Kano.
Igwe, S. (2010). How Africa underdeveloped Africa.
Port Harcourt: Prime Print Technologies.
Isa, M. A., Ibrahim, A. K., Junaidu,
M., & Isma’ila, B. (Eds.). (2017). Kano:
The state, society, and economy (1967–2017), 50th anniversary of the creation
of Kano State. Kano: Century Research and Publishing Limited.
Koko, H. S., & Fatima, A. (Eds.).
(2018). Taskar adabin mata.
Sokoto: Annoor Multimedia Limited.
Labbo, U. M. (2015). Diplomacy and war in the Sokoto
Caliphate. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Madauci, I. (1968). Al’adun Hausawa. Zaria:
NNPC.
Maishanu, I. M., Jafar, M. K., &
Nazir, I. B. (Eds.). (2020). Zamfara
and the challenges of socio-political transformation (1764–2019).
Sokoto: Faculty of Arts and Islamic Studies.
Maishanu, I. M., Usman, M. T., &
Gobir, Y. A. (Eds.). (2021). Transformation
in Gobir Kingdom: Past and present. Sokoto: FAIS, International
Conference Proceedings.
Mani, A. M. (1956). Zuwan Turawa a Nijeriya Arewa.
Zaria: NNPC.
Nadama, G. (1977). The rise and collapse of Hausa states:
A social and political history of Zamfara (PhD thesis). Ahmadu
Bello University, Zaria.
Nasidi, Y., & Iyortange, I.
(Eds.). (1997). Culture and
democracy. Zaria: Ahmadu Bello University Press.
Nedel, F. J. (1970). Hausawa da maƙwabtansu. Zaria: Gaskiya Corporation.
Safana, M. S. (2003). Gurbin gaskiya cikin adabin Hausa
(Master’s thesis). Usmanu Danfodiyo University, Sokoto.
Sani, A.-U., & Bakura, A. R.
(2023, December). Al’adun Hausawa a duniyar intanet: A san matsayin yau don a
kyautata gobe. Zamfara
International Journal of Humanities, 2(3), 82–92. https://doi.org/10.36349/zamijoh.2023.v02i03.010
Sani, A.-U., & Maikwari, H. U.
(2019). Cuɗanyar al’adu a Sabon Garin Kano: Wani misali na
“mun zo garinku mun fi ku rawa.” EAS
Journal of Humanities and Cultural Studies, 1(4), 240–245. https://www.easpublisher.com/get-articles/359
Sani, A.-U., Shehu, M., & Rambo,
R. A. (2023). Bitar tasirin Musulunci a kan al’adun Hausawa na mutuwa. Scholars International Journal of
Linguistics and Literature, 6(12), 498–502. https://doi.org/10.36348/sijll.2023.v06i12.007
Sani, A-U. & Maikwari, H.U.
(2019). Cuɗanyar al’adu a Sabon Garin Kano: Wani misali na
“mun zo garinku mun fi ku rawa.” EAS Journal of Humanities and
Cultural Studies, 1(4), 240-245.
https://www.easpublisher.com/get-articles/359.
Sarkin Sudan, I. A., Yahya, I., &
Muhammad, M. U. (Eds.). (2021). Matsalar
tsaro a Arewacin Nijeriya: Matanin rubutattun waƙoƙin gasar (2021). Sokoto: UDUS Press Ltd.
Shehu, M. & Sani, A-U. (2018).
Zamantakewar Hausawa jiya da yau. Yobe Journal of Language, Literature and
Culture (YOJOLLAC), 6. 274-284. ISSN 2449-0660.
Usman, B. B., & Sani, A.-U.
(2019). Gargaɗi ga
kyautata zamantakewa: Faɗakarwa
daga alƙalamin Isan
Kware Ɗan Shehu. East African Scholars Journal of
Education, Humanities and Literature, 2(10), 621–632. https://www.easpublisher.com/get-articles/950
William, S. I. (2007). Can our culture
and traditions overcome corruption? Inhaus
Services Limited.
Yahaya, I. Y. (1979). Oral arts and the socialization
process (PhD thesis). Ahmadu Bello University, Zaria.
Yanɗaki, A. I., Jumare, I. M., & Usman, M. T. (Eds.).
(2018). Mahdi Adamu in the
practice of history: Hausaland and beyond. Zaria: Ahmadu Bello
University Press.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.