Citation: Gambo, H. & Mohammed, S. (2025). Barkwanci a Ƙasar Hausa: Bitar Asalinsa Da Gurbinsa a Zamantakewar Hausawa. Tasambo Journal of Language, Literature, and Culture, 4(2), 46-51. www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i02.007.
BARKWANCI A ƘASAR HAUSA: BITAR ASALINSA DA GURBINSA A ZAMANTAKEWAR HAUSAWA
Hamza Gambo
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero Kano
Email: hgambo31@gmail.com
GSM: 08167309171
Da
Shu’aibu Mohammed
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero Kano
Da
Muhammad Isa Usman
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Bayero Kano
Tsakure
Wannan nazari an
aiwatar da shi ne a kan barkwanci a tsakanin al’ummar Hausawa. Nazarin an
aiwatar da shi ne ta hanyar samo bayanai daga litattafai da kundaye da kuma
kafafen sada zumunta kamar facebook da tiktok. An gudanar da wannan takarda ta
bin bayanan da masani Gusau, (2003) ya kawo na aiwatar da waƙar baka da sauran
matanin adabi, an kuma yi amfani da matakan da ra’in ya samar na nazarin waƙar baka da sauran
dabarun jawo hankali. Manufar wannan takarda shi ne gano barkwancin da Hausawa
suke yi, ta hanyar kafa hujjoji daga bayanan da aka samo daga kundaye da
kafafen sadarwa. Sannan an yi sharhin dukkannin abubuwan da nazarin ya gano. A ƙarshe dai binciken ya
gano barkwanci, ta hanyar fayyace yadda ake aiwata da shi daki-daki da misalai.
Fitilun Kalmomi: Barkwanci,
Zamantakewa, Asalin Barkwanci
1.0
Gabatarwa
Takardar tana ɗauke da bayanai ne a
kan barkwanci.
Barkwanci na ɗaya daga cikin
nau’o’in adon harshen na maganganun azanci. A takardar an yi, ƙoƙari wajen ganin an
duba ayyukan magabata kamar: Ɗangambo (2008) da Yahaya (1992) da
Gusau (2013) da Gumel (1992) da sauransu. Haka kuma, an yi tsokci kan ra’in da
aka yi amfani da bayanan ciki wajen gudanar da binciken. An kawo ma’aanar
barkwanci a mahangar masana, sannan an kawo masu yin barkwanci da dalilin da
suke sa a yi barkwanci. Haka kuma dukkanin misalai da aka kawo a kowanne ɓangare, an kafa hujja
ne daga ɗaya daga cikin
barkwancin da aka nazarta, domin a tabbatar da barkwanci a ilimance. A ƙarshe an fito da saƙonnin cikin talluka
da zantukan da suke a wasu kafafen sada zumunta.
1.1 Ra’in Bincike
An ɗora wannan bincike ne
bisa ra’in tsarin waƙar baka Bahaushiya Wanda ya ƙirƙiro wannan ra’i shi ne Farfesa Gusau
shekarar 2003 A ƙasar Nijeriya, shi wannan ra’i yana yana ƙarfafa yadda za a yi nazarin waƙar baka da hanyoyin da
ake bi wajen nazartar waƙar baka da kuma adon harshe. An sami manazarta
adabi waɗanda suka gabatar da
ayyuka a kan wannan ra’i. Wannan dalilin ne yasa aka ɗora wannan aiki na
amfanin habaici a kafafen sadarwa.
1.2 Hanyoyin Tattaro Bayanai da Sarrafa su.
A ƙoƙari gudanar da wannan
bincike an yi ƙoƙarin samo bayanan da aka nazarta daga Ɗangambo (1984) da
Umar (1986) da Tukur (1991) da Ingawa (1990) da CNHN (2006) da Bunza (2006) da
gidajen radiyo da kuma facebook da tiktok. Haka kuma an sake samo bayanai daga
littafin Ibrahim Yaro Yahaya wanda suka yi tare da wasu. An
sake samo wasu bayanan daga gidajen rediyo da kumafacebook da tit-tok a inda
aka samo waɗannan bayanai.
2.0 Ma’anar Barkwanci a Mahangar Masana
Ƙamusun Hausa (2006: 39)
ya bayar da ma’anar barkwanci da “Raha ko wasa na fatar baki don ban dariya”. Ɗangambo (1984: 36)
yana ganin barkwanci “zantuka ne na raha da wasu mutane waɗanda Allah ya hore wa
iya raha da magana da ban dariya suke yi wa mutane”.
Shi kuma Umar (1980)
cewa ya yi barkwanci “wani muhimmin rukuni na zube a adabin baka na Hausa wanda
ya danganci irin labarun nan da Bahaushe yakan ƙirƙira don kawai ya yi
dariya ya more”. Tukur (1999: 11) ya bayyana barkwanci da cewa “zantukan raha
ne da ban dariya da mafi yawan al’umma suka amintu da wanzuwarsu don adana
tarihinsu da yauƙaƙa zumunci”.
A bisa ga bayanan da
masana suka faɗa dangane da ma’anar
barkwanci. Za mu iya cewabarkwanci wata magana ce da akan shirya mai ɗauke da zantukan
hikima waɗanda suke sanyawa a
yi raha da annashuwa a tsakanin mutane biyu,,
ko a tsakanin wasu al’umma (abokan wasa) waɗanda a duk wurin da suka haɗu da juna, sai sun yi
zolaya ko kuma sun tunzura juna ba tare da an yi saurin samun wani saɓani a tsakaninsu ba.
A taƙaice dai barkwanci
wani salon magana ne da Allah kan huwace shi ga ɗaiɗaikun mutane ta inda za su kasance masu
fasaha a duk zancensu Hakan ya sa da zarar sun yi magana sai an yi raha; akalla
a yi murmushi. Barkwanci na iya zama tsararren zance na ban dariya, musamman
wanda aka shirya shi don zolaya ko tsokana. A wani ɓangaren kuma
barkwanci shi ne irin wasa da ke tsakanin ƙabilu ko al’umma, ta
dalilin aukuwar wani lamari mai girma a tsakaninsu. Haka kuma wasan da ake samu
a tsakanin taubasai (abokan wasa na dangi) ana kiran sa da barkwanci
2.1 Masu Yin Barkwanci
Dangane da masu yin
barkwanci, yawanci duk rukunin al’umma na yin barkwanci, barkwanci ba na
ya-ku-bayi ba ne kaɗai, hatta saraki da
ma’aikatan gwamnati na yin sa. Haka ma makaɗa da mawaƙa da maroƙa ma suna yin
barkwanci, samari da ‘yanmatatsofaffi da dattijai da yara ma duk suna
barkwanci. Haka ma malamai da almajirai ma suna yi barkwanci don haka ba wani
rukunin mutanen da ba sa barkwanci.
2.2 Dalilan da ke sa a yi Barkwanci
Wasan barkwanci a
tsakanin al’ummar Hausawa wani daɗaɗɗen al’amari ne wanda yake da wuyar a ce ga
lokacin da aka fara aiwatar da shi a cikin rayuwar Hausawa. Akwai dalilai da
sukan sanya a yi wasan barkwanci tsakanin al’umar Hausawa ko da wasu. Dalilan
sun kasu zuwa manyan gida uku kamar haka:
2.2.1 Zumunci
Zumunci wata
kyakkyawar dangantaka ce ta jin ko ta aure ko ta abota tsakanin mutum da mutum
(Ƙamusun
Hausa, 2006: 496). Zumunci wani babban dalili ne da yake kawo wasan barkwanci
tsakanin al’umar Hausawa. Bakura da Sani (2022: 31) sun nuna cewa, zumunci yana
ɗaya daga cikin dalilan da suke haifar da barkwanci a tsakanin
al’umma. Haka kuma, barkwanci wata hanya ce ta ƙarfafa danƙon
zumunci a tsakanin mutane.
Zumunci a
zamantakewar Hausawa ya kasu gida biyu; akwai zumunta ta ‘yan uwantaka wadda ta
ƙunshi
dangantaka ta jini. Irin wannan dangantaka ce ta haifar da wasan barkwanci
tsakanin kaka da jika da taubasi da kuma wasan ƙannen miji da mata.
Sai kuma, zumunci tsakanin masu sana’o’in gargajiya. Sana’o’in Hausawa na
gargajiya sana’o’i ne da suke dogara da junansu a koda yaushe. Don haka, wannan
ya bayar da damar yin wasa a tsakanin masu sana’o’i biyu ko fiye da ma
dangantaka wato alaƙa ta jinni. Misali, Makiyayi da Mahaucida Malami da
Maharbi da Maƙeri da Buzu da sauransu.
2.2.2 Zaman Tare
Zaman tare zana wuri ɗaya ne tsakanin wasu
mutane wanda hakan kan janyo shaƙuwa da junaA
sakamakon zama wuri ɗaya tsakanin wasu
mutane waɗanda babu alaƙa irin ta jini ga shi
kuma suna zaune a muhalli ɗaya. Misali, auratayya a sanadiyyar haka sai wasa irin na
barkwanci ya shiga tsakaninsu.
Ga wani ɗan misali:
Wai an ce zaman tare ya haɗa wani Bufulatani da ɗan ƙabilar Tibi. Da Bufulatanin nan zai yi tafiya sai ya ba wa Tibi ɗin nan amanar kadararsa suka yi ban-kwana. Ai kafin
Bufulatanin nan ya dawo Tibi ya hau kan dukiyar nan ya cinye, bai rage komai
ba. Bafulatani na dawowa ya tambayi Tibi game da ajiyarsa, sai Tibi ya ce: “Mun
ci!” Wannan dalilin ne ya sa har gobe za a ji Fulani na ƙiran Tibi da suna “Mun ci”
(D/Iya, 2/10/2016)
2.2.3 Yaƙi
Akwai yaƙe-yaƙe da dama da suka
shiga tsakanin daulolin Ƙasar Hausa da kuma maƙabtansu tun kafin
jihadin Shehu Usman Ɗanfodiyo. Kowace masarauta ta Ƙasar Hausa ta kan far
wa wata masarauta da faɗa (yaƙi) domin ta faɗaɗa ƙasarta ta kuma
mallaki tattalin arziki mafi girma. Wannan dalilin yaƙin tsakanin wata
masarauta da wata shi ne ya assasa wasan barkwanci da ake tsakanin Katsinawa da
Gobirawa, Katsinawa da Haɗejawa, da kuma
Guddirawa da Haɗejawa. (Bunza 2015)
Ga wani ɗan misali:
Haka ma a kusa-kusan nan an samu labarin barkwancin
da ya faru a fadar Sarkin Katsina. An ruwaito cewa taron aure ne ya haɗa Sarkin Katsina da wani Kwamishina da ya zo daga
jihar Nja, inda Sarki ya murtuke, ya kalli wannan Kwamishinan ya ce: “ Duk
jami’in da ya zo daga jihar Neja kar a bar shi ya fita, a ɗaure shi.” Mutane suka fara kallon-kallo. Da Mai
martaba ya lura, sai ya saki fuska ya ce: “Saboda su bayinmu ne” Nan fa raha ta
dawo sabuwa a fada, musammam ga mutanen da suka san wannan tada ta barkwanci. (Ɗan maman Alajiƙan Shata)
3.0 Rabe-Raben
Barkwanci
Ana iya karkasa
barkwanci bisa la’akari da masu yinsa. Za mu iya samun rabe-rabe kamar haka:
3.1 Barkwanci Tsakanin Rukunan Hausawa
Tarihi ya nuna cewa Ƙasahen Hausawa sun
sha fama da ƙananan yaƙe-yaƙe da aka sha gwabzawa,
sai dai abin da aka jima, amma ba sa
lissafuwa,. An fafata tsakanin Gobirawa da Katsinawa, an yi ɗauki-ba-daɗi tsakanin Kanawa da
Katsinawa, an yi artabu tsakanin Zamfarawa da Kanawa da kuma gumurzu tsakanin
Katsinawa da Haɗejawa da kuma yaƙi tsakanin Kanawa da
Zazzagawa. Daga ƙarshe dai yaƙe-yaƙen ƙasarmu su suka
fahimtar da mu cewa; dole a share jini a koma wasa. A taƙaice dai masana na
ganin yaƙe-yaƙen da al’ummomin Ƙasar Hausa suka yi da
wasu ƙasashe da kuma tsakaninsu, su suka haifar da wasannin da
ke gudana a yau. An gama yaƙi an riga an fahimci juna kowa ya san
wurin da wani ya kwana, da wanda ya yi rinjaye da wanda
aka rinjaya, don haka kowa ya miƙa wa
zaman lafiya wuya. Umar 1986)
Wasu wasannin sun faru ne sakamakon yaƙin da aka gwabza,
wasu kuma sakamakon auratayya da ta shiga tsakani, wasu kuma zamantakewa ta yau
da kullum. Daga cikin wasannin barkwancin da ke gudana tsakanin rukunan na
Husawa sun haɗa da:
3.2 Katsinawa da Gobirawa
Wasan barkwanci
tsakanin Katsinawa da Gobirawa ya ƙullu ne bayan da aka
kwashi ‘yan kallo musamman lokacin da Katsinawa suka rinjayi Gobirawa a wata
fafatawa da aka yi har Sarkin Gobir Ibrahim Babari (1737-1764) ya ce: “A mazaya
a mai da iri gida” lokacin da ya ga Katsinawa na ƙoƙarin ƙarar da mayaƙansa. Tun a wannan
lokacin kowa ya miƙa wa zaman lafiya wuya sai ‘yan abn da ba a rasa ba. A
kan wannan ne wasan barkwanci ya ƙullu tsakanin
Gobirawa da Katsinawa, Duk in da Katsinawa suka haɗu da Gobirawa sai sun
musu irin wannan wasan barkwancin suna ce musu “A mazaya a mai da iri gida”, ko
su ce “Gobirawa sun ƙare har jariransu”. Su ma Gobirawa suna da
wasu lafuzzan barkwanci da suke faɗa wa Katsinawa, sukan ce: “Katsinawa bayinsu
ne” saboda su suka fara cin Katsina da yaƙi. (Ingawa 1990)
3.2.1 Katsinawa da Kabawa da Haɗejawa
Barkwancin da ke
gudana tsakanin Katsinawa da Kabawa ba ta yaƙi ba ce, ta auratayya
ce. Wato Katsinawa ne suka ba wa Kabawa aure. An ce Sarkin Katsina Tsaga-Rana
1751-1764 ya ba sarkin Kabi Kanta auren ‘yarsa wanda ta haifi ‘ya’ya da yawan
gaske. Wannan dangantakar ce ta ƙara donƙon zumunci tsakaninsu
da kuma ɗorewar zaman lafiya
har zuwa yau. (Dano 2015)
Amma wasan barkwancin
da ke tsakanin Katsinawa da Haɗejawa yaƙi ne ya haifar da shi sakamakon an
samu yaƙe-yaƙe tsanin Katsina da Haɗeja.
3.3 Kanawa da Daurawa da sauran Ƙasar
Hausa.
Wasu sun ce wasan
barkwanci tsakanin Kanawa da Daurawa ya samu ne sakamakon gwada ƙwarin ƙashi da aka yi
tsakanin ƙasashe biyu. Wasu kuma cewa suka yi alaƙar jii ta haddasa
wasan, wato Kanawa ‘ya’yan Bagauda ne, Daurawa kuma ‘ya’yan Garori ne. A kan
wannan dangantakar ne aka ce wasan jika da kaka ne ke tsakaninsu. Sauran
wasan na barkwanci sun haɗa da tsakanin Kanawa
da Ningawa wanda ita ta samu ne sakamakon fafatawar da aka yi da juna. Sai kuma
tsakanin Kanawa da Zazzagawa da kuma Kanawa da Zamfarawa da sauransu. (Tukur
1991)
3.4 Barkwanci Tsakanin Hausawa da Wasu Ƙabilu
Tarihi ya nuna cewa
yaƙe-yaƙen da Hausawa suka gwabza
bai tsaya tsakaninsu ba kawai ba, akwai wasu artabun da aka kwasa tsakaninsu da
wasu ƙabilu musamman Nufawa da Barebari da kuma Fulani. Bayan
yaƙi
ya lafa, zuciya ta sanyi ai aka share filin gaba ya koma filin wasa. aga cikin ƙabilun da wasan
barkwanci yake
gudana tsakaninsu da Hausawa sun haɗa da:
a. Katsinawa
da Nufawa
b. Katsinawa
da Barebari
c. Hausawa
da Kambari
d. Gobirawa
da Yarabawa
e. Hausawa
da Buzaye
3.4.1 Barkwanci
Tsakanin Tobasai Na Jini
Da farko dai kalmar
Tobasai ta samo asali ne daga kalmar Taubashi wada take
nufin ɗan mace ko ɗan namiji, wato ɗan wa da ɗan ƙauwa, ko ɗan ya da ɗan ƙani (Ƙamusun Hausa 2006: 423).
Akwai wasan barkwanci na musamman da yake gudana a tsakanin
waɗannan mutanen a kusan
duk lokacin da aka haɗu da juna. Ana irin
wannan wasan sosai domin kowa yana faɗar albarka3cin bakinsa. Ana ma aka yi wasan
barkwanci sosai kowa ya faɗi albarkacin bakinsa. Irin wannan wasan yana da tasiri ƙwarai wajen tabbatar
da zama lafiya da ƙarfafa zumuntar ‘ya’ uwa na jini da ma sauran al’umma.
(Tukur 1990)
4.0 Barkwanci
Tsakanin Masu Sana’a
Akwai sana’o’in
Hausawa da dama musamman ma na gargajiya waɗanda suke da alaƙa da juna ta fuskar
amfani ko yanayin gudanarwarsu ko sarrafawa. Wasu sana’o’in sun dogara ne ga
wasu wajen samar masu kayan gudanar da sana’ar tasu, wasu kuma kamar kishiyoyin
juna ne. Irin wannan yanayi na zamantakeawar shi yake haifar da kishi da kuma gaba
tsakanin juna, wanda kuma ka iya haddasa fitina a tsakanin al’umma. A maimaikon
cigaba da irin wannan ƙazamin zaman, sai Hausawa suka ƙirƙiri wasan barkwanci
wanda zai kawar da tunanin kishi da gaba domin a zauna lafiya. A dalilin haka,
aka samu wasannin raha tsakanin masu sana’o’
daban-dabam da suka haɗa da: (Tukur 1990)
4.1 Masunta da Mahauta
A duk lokacin da
masunta da mahauta suka haɗu akan yi wasan barkwanci kowa ya yi nishaɗi har da mutanen da suke
kusa. Daga cikin kalaman barkwanci da suke faɗa wa juna shi ne, mahauta kan cewa
masunta “ga kuɗinsu a ba su fata da
kayan ciki” ko kuma su ce “masunta kuna kayan gawa, ina mahautarku take?” Su
kuma masunta sukan
mayar da martani su ce “mahautarmu tana ga Allah, turun bashi”. (Rabi’u
Abbatuwa)
4.2 Maƙera da
Wanzamai
Wannan wasan
barkwanci tsakanin maƙera da wanzamai ya ƙullu ne sakamakon
dangantakar da take
akwai a tsakanin sana’o’in biyu. Maƙera suna
ganin su ne masu gidan wanzamai, domin kuwa su ne suke
samar musu muhimmin kayan da suke amfani da shi a sana’ar tasu. Ba ma wanzamai
kawai ba maƙera na ganin su ne iyayen gidan mahauta da manoma da kuma
masassaƙa. Don haka, a duk inda aka haɗu akan taɓa wasan barkwanci
kafin a rabu. Maƙera kan yi wa wanzamai su ce musu “wanzam ba ka so a
jikinka“. Wanzamai kan mayar da martani su cewa maƙera “maƙeri sai ka ɗanɗana kuɗarka”. (D/Iya
2/10/2019
Akwai wani wasan barkwanci tsakanin Maƙera da Masassaƙa, inda Maƙera kan ganin su ne
masu gidan masassaƙa domin su suke samar musu ƙarfen da suke sassaƙa da shi. Idan an haɗu maƙera kan ce wa masassaƙa “sakke gwanin
kashin ice ba na raya ice ba”. Su kuma massaƙa su ce wa maƙera “maƙeri abokin wuta, ko a
can tare kuke”.
4.3
Mahauta da Majema
Akwai wasannin
barkwanci da ke samuwa tsakanin waɗannan al’umma. Wannan wasa yana da nasaba da ƙarfafa zumuncin
sana’arsu. Mahauta suna ganin su ne masu gidan majema tun da sai sun yanka
dabba sun cire fatarta sa’annan majema su samu fatar da za su sarrafa. Don haka
ne ma majema suke
kaɓar dukiyar shara ga
mahauta idan lokaci ya yi. Mahauta kan yi wa majema
barkwanci suna ce musu, “A ci ƙazanta, a kwana cikin ƙazanta, ai ado da ƙazanta sai majema”.
Su kuma majema sukan ce wa
mahauta, “Talle ba ta yi audi gori, jikan ma ci bashi”. Haka ma duk lokacin da
aka haɗu akan yi raha kafin
a rabu. (Shehu 2017)
4.4 Masu
Goro da Masu Gishiri
Wasannin barkwancin
da yake
gudana tsakanin waɗannan masu sana’a,
wasa ce ta kyautata zamantakewa saboda dangantakar da suke da ita na zama kamar
kishiyoyin juna. Mai sana’ar Goro a koyaushe cikin ban-ruwa goronsa yake, shi
kuma mai gishiri babu abin da ya fi tsana ya taɓa sana’arsa kamar ruwa. Don haka, a
duk lokacin da mai goro ya haɗu da mai gishiri sai wasan barkwanci ya kaure, mai goro
na faɗin Allah ya kawo
ruwan sama, shi kuma mai gishiri ya ce ba amin ba. (Lawan 2016)
Haka kuma akwai sana’o’i da dama da wasan
barkwanci ya shiga tsakanin masu yin sana’o’in kamar wasan barkwanci da yake
shiga tsakanin masu raƙuma da masu jakai, Direbobin mota da masu raƙuma, masu rake da mai
alewa da sauran su.
5.0 Sakamakon Bincike
Haƙiƙa babu shakka wannan
bincike ya gano muhimman barkwanci da yake a tsakanin al’ummar Hausawa da
makwaftansu da kuma masu sana’o’in Hausawa na gargajiya, wanda sakamakon haka
ya sa aka sami wasanni tsakanin masu sana’a da kuma sauran mutane.
Haka kuma, haƙiƙa wannan bincike ya
gano cewa, akwai barkwanci a tsakanin al’umma, domin kuwa an sami barkwanci a
cikin waƙoƙi da maroƙa kamar ‘yangambara da ‘yankama da
‘yan’adaki bzu da ‘yandamalgo da kuma ‘yangalura da sauransu. Haka kuma, wannna
bincike ya gano barkwanci a kafafen sadarwa kamar: Facebook da Tik-tok da
Gidajen Rediyo da Talabijin da sauran kafafen sadarwa.
6.0 Kammalawa
Wannan bincike ya yi ƙoƙarin kawo barkwanci a
tsakanin al’ummar Hausawa da yadda ya sami ɗaurin gindi a tsakanin al’ummar Hausawa,
wanda ya zame musu garkuwa ga jindaɗin rayuwa. Barkwanci zantuka ne na raha da
wasu mutane waɗanda Allah ya hore wa
iya raha da magana da ban dariya da suke yi wa mutane. Barkwanci ya samu ne
bayan Hausawa sun gama yaƙe-yaƙe a tsakaninsu. Wannan ya haifar da ƙirƙiran wasan barkwanci
don kawar da tashin-tashina da rigingimun da suka dabaibaye rayuwar Hausawa.
Wasan barkwanci hanya ce ta ƙulla/ƙara dnƙon zumunci da haɗin kai da ƙaunar juna da inganta
zamantakewa tsakanin Hausawa ko tsakanin Hausawa da wasu maƙwaftan ƙabilu.
arkwanci yakan sa raha ko nishaɗi da manta zogin abun da ya faru a baya. Zumunci da haɗin kai da manta abin
da ya faru a baya na artabun da aka yi tsakanin masu
wasanin barkwanci kuwa, su ne suke haɗuwa su samar da zaman
lafiya mai ɗorewa tsakanin
al’umma.
Manazarta
Bakura, A.R. & Sani, A-U. (2022). Ƙabilu a tunanin Bahaushe: Duba cikin labaran barkwanci. Sarcouncil
Journal of Humanities and Cultural Studies 1(1), 27-32.
https://zenodo.org/record/6418660.
Bunza,
A. M (2006). Gadon Feɗe Al’ada. Lagos Tiwal
Nigeria Limited.
CNHN,
(2006) Ƙamusun Hausa Ahmadu Bello University, Press
Ɗangambo, A. (1984). Rabe-Raben Adabin Hausa da
Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Triumph Publishing Company.
Gusau, S. M (2008). Adabin Hausa a Sauƙaƙe. Century
Research and Publishing Lt.
Gusau,
S. M. (2013). Jagoran Nazarin Waƙar Baka. Benchmark
Publishers Lt.
Ingawa, I. L.
(1990). Katsina Ɗakin Kara. Katsina: Arewa Printers Limited.
Lawan, N. (2023). Barkwanci mai labari a Matakin
Nazari: Cikin Journal of Contemporary Hausa Studies. Vol 5 no 1 Katsina:
Jami’ar Umaru Musa ‘Ya’aduwa.
Sanyinnawal, S. I. (2012). Cuɗeɗeniyar Sana’o’in Gargajiya a Adabin Bakan Bahaushe. [Kundin
Digiri na Biyu] Sashin Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.
Tukur, A. (1991) Wasannin Barkwanci A Ƙasar Hausa. Rukhsa Publications.
Umar, M. B. (1986). Dangantakar Adabin Baka da Al’adun Hausawa.
Kano: Triumph Publishing Company.
Yahaya, I.Y, Gusau S.M, Yar’aduwa T.M (1992)
Darussan Hausa Don Manyan Makaratun Sakandire Littafi na biyu Zaria:
Ahmadu Bello Uniɓersity, Press.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.