𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Tambayata Ita ce: Yaya Sunnah ta koyar ga wanda jinnu ke damu, da kuma kariya daga su ko da ba suna jikin Ɗan Adam ba ne?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salam, ƴar uwa game da wanda ke fama da jinnu, ya tabbata
za a iya yi masa ruƙ'ya wadda ba ta saɓa wa Shari'a ba,
saboda hadisin Aufu bin Malik Al'ashja'iy da ya ce: Mun kasance muna yin ruƙa a zamanin jahiliyya,
sai muka ce; ya Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam mene kake gani game da
hakan? Sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce: " Ku nuna min ruƙan naku, babu laifi ga
ruƙa matuƙar babu shirka a
cikinta". (Sahihu Muslim 2200).
Wannan ya zama dalili a kan yin ruƙ'ya matuƙar an kaucewa shirka a
cikinsa. Ibn Hajar ya ce: "Haƙiƙa malamai sun yi ijma'i
a kan halascin yin ruƙ'ya idan an kiyaye sharuɗɗa guda uku, ya
zama da maganar Allah SWT za a yi, ko da sunayensa da siffofinsa, ya zama da
harshen Larabci za a yi, ko kuma wani harshen da aka san ma'anarsa, ya zama an ƙudurce a zuci cewa ita
ruƙ'ya ba ita ce take
tasiri da kanta ba, tana yin tasiri ne da nufin Allah SWT. (Duba FAT'HUL BÁRIY
(10/227).
Shi ma Shaikhul Islam Ibn Taimiyya ya faɗa cewa: "Malaman Musulunci sun hana yin ruƙ'yar da ba a fahimtar
ma'anarta, saboda ita ce matattarar shirka, ko da kuwa mai yin ruƙ'ya ɗin bai san ita shirka ba ce". (Duba littafin
AKHBÁRUL JINNI WASSHAYAƊEEN shafi na 21, na Ibn Taimiyya).
Wato dai dole mai son yin ruƙ'ya ya yi ta da maganganun Allah, da sunayensa da
siffofinsa, kuma ba a so a yi ruƙ'ya da kalmomin da ba a san ma'anarsu ba, haka kuma ba a son mutum ya riƙa tunanin cewa ita ruƙ'yar ce za ta samar da
waraka da kanta, wato a ƙudurce cewa Allah ne zai ba da lafiya.
Yana daga cikin hanyar samun kariya daga jinnu:
kiyaye farillai da wajibai, da nisantar haramtattun al'amura, da yawan tuba
daga dukkan munanan ayyuka, da yawan kyautata yin zikirori da addu'o'i, da
isti'azozi da shari'a ta yarda da su.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.