MAGANIN YAWAN FITAN RUWA MAI ƘAIƘAYI DAGA FARJI
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum. Malam ina yawan samun fitar ruwa a farji kuma yana ƙaiƙayi dan ALLAH mene ne, kuma mene ne maganin ?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Walaikumussalam........ Lalai wannan shine
infection dan haka kibi wayannan hanyoyin dan maganceshi. Ki gwada ɗaya daga cikin wadannan:-
1. Ki samu Saiwar Garafuni da Sassaken Magarya,
sai a tafasa, idan ya ɗan huce sai mace
ta dinga kama ruwa da shi. Kullum sau ɗaya. Yana
maganin budewa da kaikayi.
2. Ki samu Garafuni da Sassaken Sanya sai a
tafasa, mace ta dinga shan rabin kofi da safe, rabi da yamma. Yana fitar da
dattin mara da maganin farin ruwa mai wari.
3. Ki samu Furen Tumfafiya, sai a shanya ya bushe,
a daka a dinga zubawa a cikin Nono ana sha. Yana magance matsalar ruwan
infection.
4. Ki samu Lalle da Ganyen Magarya da Kanumfari, a
haɗa waje ɗaya a daka
sannan a tafasa a zuba farin miski a ciki. Idan ya ɗan huce sai ta shiga ciki ta zauna tsawon kamar minti
goma. Yin haka yana maganin kaikayi da kuraje da budewa da dadewar gaba.
5. Ki samu Kabewa a dafa ta, bayan an dafa sai a
tsame daga ruwa a jajjagata ko a birga, a zuba Madara ko Nono sannan a sa Zuma
a sha. Wannan yana mganin rashin sha'awa da bushewa da rashin gamsuwa.
6. Ki dafa Zogale, idan ya dahu sai a murje shi ko
a dama, a ta ce, a yi lemon juice da shi. Yana maganin fitar farin ruwa mai
wari da cushewar mara kuma yana kara ni'ima.
7. Ki samu `Dan-Tamburawa da Albabunaj a tafasa a
zuba Man Hulba a ciki. Sai ta dan tsuguna tururin ya dinga shigarta. Idan ya
dan huce kuma sai ta shiga ciki ta zauna. Zai magance mata kaikayi da kuraje
kuma yana sa matsewa.
8. Ki samu Farar Albasa da Kanumfari da Citta da
Malmo da Barkono da Raihatul Hubbi, sai ta dake su tayi Yaji ta dinga cin
abinci da shi. Yana saukar da ni'ima da magance duk
matasalolin sanyi.
9. Ki samu Sabulun Zaitun da Sabulun Habba sai a
daka su. A samu ganyen Magarya da Garin Bagaruwa a daka a tankade. Sai a zuba
akan sabulan da aka daka sannan a kwaba da Ma'ul Khal, a zuba Man Tafarnuwa da
Farin Almiski. Sai mace ta dinga kama ruwa da shi kullum sau ɗaya. Da ruwan dumi amma ake tsarki da shi. Wannan Sabulu
yana maganin kuraje da kaikayi da fitar wari.
19. Ki samu Man Zaitun da Man Habba da Man
Tafarnuwa da Man Kanumfari sai a hadesu waje ɗaya. Mace ta dinga shan cokali ɗaya kullum kafin ta karya. Yana wanke dattin mara kuma
yana samar da ni'ima.
11. Ki samu Ciyawar Kashe-Zaƙi da Farin Magani sai ta haɗa waje ɗaya ta dinga
jika rabin karamin cokali tana sha. Sannan ta dinga shan Man Zaitun Cokali ɗaya kullum kafin ta karya. Wannan yana maganin dattin
mara da wanke daudar mahaifa.
12. Ki samu garin saiwar Zogale se a debi cokali ɗaya adafashi da 'yar jan kanwa se adinga sha. Yana
maganin fitar Ruwa ta gaba in sha Allahu.
Allah Yasa Adace.
✍Jamila Dahiru Muhammad
(Muhsinat Datti)
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.