ALLAH YA JIƘAN "TARA GARI ƊAN MAMMAN ", AMIN.
An haifi Alh. Sa'idu Muhammad Baƙo a garin Kwantagora ta
Jihar Neja a shekarar 1934.
Mahaifinsa shi ne Malam Muhammadu Sarkin Zagin Kwantagora.
Ya yi karatun addinin musulunci mai zurfi ya kuma yi karatun zamani a matakin firamare. Tun ya na ƙaraminsa ya ke da ƙwazon neman nakai ta hanyar sarrafa taro sisin dake shigo shi. Wannan ne silar azama da nasibinsa a fuskar kasuwanci.
Ya yi sana'o'i daban daban ciki kuwa har da siye da siyar da
kayan abinci irin su Hatsi da Wake da sauransu kafin daga baya ya tsunduma a
cikin sha'anin kwangilar ciyar da Sojoji a Barikinsu daban daban.
Irin wannan zirga-zirga ce ta sanya shi barin Kwantagora
zuwa yankin kudu maso gabascin Nijeriya kamar su Inugu da Aba da Umma'ahiya
inda ya haɗu da sojoji 'yan asalin Jihar Arewa tun suna ƙananan hafsoshi kamar
su Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Janar Aliyu Muhammad Gusau suka ƙulla
abotar da bata yanke ba har bayan wafatinsa.
Kamar yadda muka ambata a sama ya samu shiga sosai a
sha'anin kwangilar gidan Soja dalilin waɗannan aminai da yayi musamman a
lokacin yaƙin basasa na Nijeriya (1967-1970).
Bayan kammala wannan yaƙi Alhaji Sa'idu Baƙo Muhammad ya ci
gaba da kasuwancinsa da kuma ayyukan kwangila a matakin Gwamnatin Tarayya da Gwamnatotan
wasu Jihohi cikin iyawar Allah SWT ya zama hamshaƙin mai kuɗi ba wai a Jihar
Neja ba kawai har ma a Nijeriya gaba ɗaya.
Bahaushe ya na cewa "A bayar a rasa ta hanawa raggo
suna". Allah ya yi Alhaji Sa'idu Baƙo Muhammad jarumi kuma karimin
dattijo. Nan take alherinsa ya game kowane sashe na arewacin Nijeriya.
Tun daga Adamawa da Taraba zuwa Borno Gombe da Yobe da
Bauchi da Jigawa da Kano da Katsina da Kaduna da Zamfara da Sokoto da Kebbi da
Plateau da Nasarawa da Kogi da Kwara da Benue babu Jihar da wannan bawan Allah
bai ƙulla zumunci da muhimman mutanensu ba.
Alheri da aikin tawali'unsa musamman wajen ci gaban addinin
Musulunci da fitar da al'umma daga cikin ƙangin fatara ya sanya sunansa ya yi
amo sosai musamman a lokacin siyasar Jamhuriya ta biyu.
Ya zama jigon Jam'iyyar NPN da ta kafa Gwamnatin farar hula
ta farko a Jihar Neja da kuma samun nasararta a zaɓen 1979 da kuma zaɓen 1983 a
matakin Tarayyar Nijeriya.
A matsayin godiya da tukuici akan irin kyawawan ayyukansa,
Masarautar Kwantagora a ƙarƙashin jagorancin Marigayi Mai Martaba Sarkin Sudan
na Kwantagora, Alhaji Sa'idu Namaska Allah ya jaddada masa rahama ta naɗa shi
GARKUWAN KWANTAGORA a ranar Asabar 22 ga watan Maris na shekarar 1980 inda aka
gudanar da ƙasaitaccen bikin da ya tara jinsin al'umma a garin Kwantagora.
ALLAHU AKBAR! WANI AIKI SAI TARA GARI ƊAN MAMMAN.
Allah SWT ya karɓi rayuwar Alhaji Sa'idu Baƙo Muhammad
Garkuwan Kwantagora a ranar 21/8/1989.Ya bar iyali (matan aure da 'ya'ya).
Daga cikin ya'yansa akwai Alhaji Ibrahim Baƙo dake zaune a
Kaduna da Alhaji Aminu Baƙo dake Abuja da Alhaji Falalu Baƙo wanda a halin
yanzu Kwamishina ne a Gwamnatin Jihar Neja da kuma Hajiya Hauwa'u Baƙo, Dakrata
- Janar a Gwamnatin Jihar Neja.
Allah ya jaddada masa rahama shi da sauran magabatanmu ya sa
mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani, amin.
Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji,
Jihar Zamfara,
Nijeriya.
Litinin 26/05/2025.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.