KO ME NE NE DALILIN KIRAN MAI SUNA IBRAHIM DA ALKUNYAR
"MAIGANDI" A YANKIN SAKKWATO, NA GURAGURI A YANKIN ZAMFARA, MAI KAITA
A YANKIN KATSINA?
A Ƙaramar Hukumar Mulkin Raɓah ta Jihar Sakkwato akwai garin da ake kira Gandi wanda a nan ne hedikwatar gundumar Gandi.
Wannan gari ya samo
asali ne daga zaman Ribaɗi na masu Jihadin jaddada addinin Musulunci da
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio tagammadahullah birahamatihi ya jagoranta a
farko farkon ƙarni na 19 har aka samar da Daular Usmaniya.
A lokacin mulkin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio(1817-1837) ne
aka naɗa ɗansa Malam Ibrahim a matsayin Sarki a wannan gari na Gandi.
Zamansa a Gandi ne ya haifar da kiransa "Maigandi"
/ "Mai Gandi" a matsayin alkunya wanda tun daga lokacin ne wannan
suna ya zama alkunyar /laƙabin duk mai suna Ibrahim musamman a yankin Tsohuwar
Jihar Sakkwato (Sokoto da Kebbi da Zamfara na yau).
A shekarar 1950 Ɗangaladiman Shinkafi Ibrahim ya zama
Dagacin Shinkafi da laƙabin Sarautar Magaji, wato Magajin Shinkafi, ya yi mulki
har zuwa rasuwarsa a shekarar 1990( Shinkafi a halin yanzu hedikwatar Masarauta
ce mai daraja ta biyu kuma ita ce hedikwatar Ƙaramar Hukumar Mulkin Shinkafi a
Jihar Zamfara).
Yana da amini /ɗan uwa da ake kira Malam Jibril dake da
Sarautar da ake kira "Guraguri" anan Shinkafi.
Shi Guragurin Shinkafi Malam Jibril ya fito daga tsatson
wani Mujahidi ne da ya taka rawar gani a jihadin jaddada addinin Musulunci na
Daular Usmaniya da ake kira Malam Muhammadu Tukur da aka fi sani da Malam Tukur
Ɗan Binta ko Malam Tukur na Matuzgi.
A farko farkon mulkin Magajin Shinkafi Ibrahim sai Makaɗa
Alhaji (Dr.) Ibrahim Buhari Abdulƙadir Mai Dangwale Narambaɗa Tubali ya yi masa
Waƙoƙi da dama cikin su kuwa har da wadda yake danganta sa da Guraguri Jibril
ko Jibril Guraguri inda yake cewa "Ibrahimu na Guraguri, mai Shinkahi
bajinin Zagi, mu dai Allah ya bam muna kayaa".
Sanadiyar yaɗuwar wannan Waƙa a yankin Zamfara sai aka samu alkunyar
"Na Guraguri" ga duk mai suna Ibrahim musamman a yankin.
Marigayi Mai Martaba Sarkin Katsina Malam Ibrahim ɗan Sarkin
Katsina Malam Muhammadu Bello ɗan Sarkin Katsina Malam Umarun Dallaje wanda ya
yi Sarauta daga shekarar 1870 zuwa 1882 ne sanadiyar samar da alkunyar
"Mai Kaita" ga mai suna Ibrahim a yankin Katsina.
Marigayi Mai Martaba Sarkin Katsina Malam Muhammadu Bello ɗan
Sarkin Katsina Malam Umarun Dallaje ya auro Mahaifiyar Marigayi Mai Martaba
Sarkin Katsina Malam Ibrahim wato Malama Habi/Habiba(Ɗiyalle) yar Malam Muhammadu Mai Gyaza daga garin
Kaita.
A lokacin da Malam Ibrahim ɗan Sarkin Katsina Malam Bello ɗan
Sarkin Katsina Malam Umarun Dallaje ya zama Sarkin Katsina sai ya dinga
ziyartar garin Kaita akai akai har ma ya
gina gida a can inda yake zama idan ya je irin wannan ziyara.
A ƙarshe ma a garin na Kaita ne ya yi wafati kuma a cikin
wannan gida da ya gina aka yi masa hubbare (makwanci).
Sanadiyar nuna irin wannan ƙauna zuwa ga wannan gari na
Kaita da jama'ar Ƙasar da Mai Martaba Sarki Ibrahim ɗan Bello ɗan Malam Umarun
Dallaje ya nuna sai al'ummar yankin suka dinga raɗawa akasarin 'ya'yansu maza
suna Ibrahim da alkunyar "Mai Kaita" domin girmamawa.
Allah ya jiƙan magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da
kyau da imani, amin.
Malam Ibrahim Muhammad Ɗanmadamin Birnin Magaji,
Jihar Zamfara, Nijeriya.
Laraba, 28/05/2025.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.