𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum Malam ygd ya kokari. Malam dan Allah ina neman shawara akan wannan matsalar. Mahaifina ne Allah ya baiwa mahaifiyata miji ta yi aure mu biyu ta haifa da babanmu nida ƙanena malam sati ɗaya kenan da mijinta yazomin cikin dare ya bani wasu ruwa nasha daganan na kasa ko magana sai kawai ya fara amfani dani (Zina) nakasa yadda zanyi in faɗawa mahaifiyana don bansan ta ina zan fara bayani ba toh malam abjn bai tsaya ba don ya sake dawo min, nidai bawai na yanke Shawarar komawa inda kakata amma mahaifiyata na nunamin ra'ayin zama damu kusa da ita, na mata uzurin saurarenta don batasan abunda ya faru dani ba, malam banason in kashe mata aure shin zan iya bijirewa ince sai inda kakata zan zauna koda rayuwarta za ta ɓaci karin tashin hankalin shine watan 12 zanyi aure narasa ya zanyi ko zan faɗawa wanda zan aura idan zai iya aurena ahaka? Shawara don Allah malam ina neman mafita.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam: Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi
Raji'uun Subhalallah toh Abin da ya Dace Za Kiyi Shine, Kada Ki Gayawa ita
Mahaifiyar Ki, Kuma Kada Ki Gayawa Shi Wadda Zai Aure Ki.
Dalilin Haka Shine, Ba Ki da Wani Shaida idan Kin
Gayawa ita Mahaifiyar Ki Wannan Labarin da ya Faru da ke a yanzu. Sa'annan Shi
ma Mijin Mahaifiyar ki ɗin ma Zai iya
Karyatawa Cewa Shi bai Aikata Hakan da ke ba. Ɗan Adam Sai Allah. Sabida haka Ke Ce Za Ki Ƙwana a Ciki kenan.
Sa'annan Idan Kin Gayawa Wanda Zai Aure Ki, Shi ma
dai ba Maslaha ba Ce Gaya Masa, Domin Zai iya Fasa Auren Ki Kuma Yake Yawo da
Sunan Ki Cewa ga Abun da Kika Aikata. Sabida haka Kawai Shawara Anan Shine Ki
Haɗa Yanaki-danaki Ki Koma Can Gidan Kakar Ki Ɗin, Koda Kuwa ita
Mahaifiyar Ki ta ce Wani Abu akan Komawar ki can Ɗin. Ki Nuna mata Cewar Hakan da Za Kiyi Shine Abun
da Zai Sa Ki Samu Natsuwa da ita kanta. Indai Kika Gaya mata Haka In sha Allahu
Na Sani za ta Ce da ke, Ko Akwai Wani Abu Ne?? Sai Ki Ce da ita babu Komai.
Idan Kika yi mata Haka, In sha Allahu za ta Bar Ki Ki Koma Can Gidan Kakar Ki.
Domin tunanin ta Zai bata Cewar Lallai Akwai Wani
Abun da yake Damun ki, Sai dai Kuma ba za ta Matsa Miki Akan Sai ta San Mene ne
ba. In sha Allahu za ta Barwa Allah ne Kawai. Duk da Cewar Na san itama tana
Son Zama da ke a Kusa da ita kema haka, Sabida Tarbiyyan ki da Sauran Su. Allah
ya tsare ki da Faɗawa Halaka da
Kuma Sauran Matan Musulmai Akan Mugayen Mutanen Banza.
Sai dai idan kina da Hujjojin ki toh ko domin
ceton rayuwar Mahaifiyar ki toh gara ki fito Fili ki sanar da ita ta hanyar
hujjojin ki da kike da su, domin za ta yiyu wannan aikin sa ne Yin Zina kin ga
kenan aje aje zai iya ɗauko Ciwo ya
sawa Mahaifiyar ki, kin ga kenan ga Auren su ya mutu akan ta ci gaba da zama da
Mazinaci ma ci yin Amana wadda bai San me yake yi ba a rayuwar sa.
Sa'annan yanzu kin ga kada Ciki ya shige ki
Mahaifiyar ki da mutane da wadda zai Aure ki su fara Zargin ke Yar Iska ce Zina
kike yi da Maza alhalin wannan banzan ne ya lalata rayuwar ki, kin ga koda ace
gayawa Mahaifiyar ki zai sa Auren ya mutu toh gara kin gaya mata in ya so Auren
ya mutu, wannan wacce irin rayuwa ce don Allah? sabida haka abun da za ki yi
kenan Mazinaci sai Yar uwar sa Mazinaciya, sa'annan babu wani zaman Aure ma ga
irin wannan Mijin da zai yi Zina da Yar Matar sa.
NASIHA Zuwa Gare Ku Maza Waɗanda Suke Tare da Agwalolin Matayen Su a Cikin Gidajen
Su, Wallahi Wallahi Wallahi Ku Ji Tsoron Allah, Ku Ji Tsoron Haɗuwa da Azabar Ubangijin Ku a Ranan Alkiyama ko Kuma daga
anan Duniyar, ranar da Allah zai bayyana duk wasu abubuwan da ka aikata
Al'umman duniya da Mala'ikun Allah da Jinnu duk suna ganin ka shi ne ranar Alƙimaya, Ku Dena Yin Zina
da Ɗiyar Matayen Ku Agwala,
Ka Sani Cewa Zina Kayi, Sa'annan Hukuncin Zina ne a Kanka ko ba ka so, Shi ne a
Jefa ka har Sai Ka Mutu. Shin Yanzu Idan Ɗiyar Ka Ce, sai Ka Saki Mahaifiyar ta Wani Namijin ya Aure ta, Sai ta Tafi
da ita Gidan Mijin ta, Sai Ɗiyar naka ta Girma ta Dawo Budurwa a gaban wannan Mijin, Sai Mijin Wannan tsohuwar
Matar naka ya Rika Yin Zina da ita, don Allah yaya Za ka Ji a Rayuwar ka?
Maza Mene ne Kuke nema a Duniyar nan ne da Babu
Kunya, babu Tsoron Allah, babu Tunawa da Mutuwa, wai Har za ka iya Saduwa da
Mahaifiyar Yarinya, Sa'annan ko kunya babu kuma Ka Juya Kayi Zina da Ɗiyar ta? Wannan Wacce
irin Rayuwar Ce haka na Zalunci da cin Amana? Wannan Wacce Irin Masifa Ce? Ka
Sani Cewa Kamar Yadda Ɗiyar Ka Mace Budurwa Wanda Ka Haifa na Jinin ka yadda ta ke a Wajen ka,
Wadda Kai Kana Ganin ba Za ka Iya Zina da Ɗiyar ka ba, haka nan itama Wannan agwalan naka ta
ke a Wajen ka, Domin ka Auri Mahaifiyar ta Kuma kana tare da ita Babu Aure ma a
tsakanin ku tunda ka Auri Mahaifiyar ta har kayi Jima'i da ita, kenan babu wani
alaka da zai shiga tsakanin ka da Yar ta domin Yar ka ce yanzu.
Allah ya haramta yin Aure tsakanin ka da ita amma
sai kuma ga shi Kai Zina ma kayi da ita Inna lillahi Wa inna Ilaihi Rajee'un
wannan wacce irin rayuwa ce ta dabbanci?, Shin ka Lalata Budurcin ta, ka Lalata
Rayuwar ta, Ka Watsar da duk Tunanin ta Farin cikin ki komai nata ka wargaza
shi, Shin kana Ganin Cewa Allah Zai bar Ka Ne? Shin kana Ganin Cewa kaima idan
Kana da Ɗiya Mace Allah ba Zai yi
Sakamako a Kanta ba ne?
Maza mene ne wanne daɗi za ka ji a zuciyar ka? ko min daɗin da za ka ji fa wallahi Azabar ƙabarin ka kaɗai masifa ce
wadda ba za ka iya ɗaukar sa ba, Yar
ka kayi Zina da ita sabida son zuciya da mugunta da Zalunci, wallahi Allah ba
zai bar ka ba. Wajibi ne gare ku Maza Masu Irin Waɗannan mummunar Ɗabi'ar Wallahi ku Ji Tsoron Allha, Ku Ji Tsoron Haɗuwa da Azabar Ubangijin ku, Ku yi Gaggawan tuba daga
Wannan Mummunar Aikin na Zina da Ɗiyar ku.
Annabi Muhammad Mai Tsira Da Amincin Allah Su
Tabbata Agare Shi yana Cewa, Shin Idan Kayi Zina da Matar Wani Kai Kana Son ayi
da Naka Matar ne? Ka Sani Cewa ita Wanda kayi Zina da ita, ai Matar Wani ne nan
Gaba, Ya ce Shin Za ka Iya Zina da Mahaifiyar Wani? ya ce Ka Sani Cewa ita
Wanda Kayi Zina da Ita fa, Nan gaba itama Mahaifiyar Wani ne, Ya ce Shin Za ka
Iya yin Zina da Ɗiyar Ka Yar ka Wadda ka Haifa kayi Zina da ita ta cire ma Tsiraicin Jikin
ta kayi Zina da ita shin za ka iya yin hakan? Ya ce Ka Sani Cewa ita Wanda Kake
yin Zina da ita Ɗiyar Wani ne, Shin idan Kaine akayiwa Haka za ka Ji Ɗaɗin Haka? idar
yar uwar ka ce zai ka za ka iya yin Zina da ita ta zauna a gaban ka ta Buɗe ma Tsiraicin ta kayi Zina da ita? haba maza Ina zamu sa
kan mu?
Ku ji Tsoron Allah, Ku tuɓa Ku ɗena Lalata
Rayuwar ƴan Mata idan Sun taso,
yin Haka Ba Karamin Zunubi ba ne da Azaba ba ne wadda kuke ɗaukar kanku, daga yin Shirka zuwa ga Allah, toh babu Wani
Bala'i da Masifa da ya kai na Yin Zina, Zinar ma wai da Yar ka haba don Allah,
duk Wani Abun da ba ka Son ayiwa Naka, toh wajibi ne ka Kiyaye yin sa ga wasu
Sai ka Zauna Lafiya. Allah muke roka ya Shiyi Masu Lalata Rayuwar ƴan Mata da Matan Aure da
Kananan Yara Ameen.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.