𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum Don Allah malam ya matsayin mutumin da ya sha nonon matarsa, ya aurensu yake?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikum Salaam; Toh ɗan'uwa Allah Maɗaukakin sarki ya
halatta maka jin daɗi daga dukkkan ɓangarorin jikin Matar ka, in ban da dubura ko kuma saduwa
da ita lokacin da take cikin haila, don haka ya halatta ka tsotsi nonon ta
mutukar babu ruwa a ciki, amma idan akwai ruwa a ciki, toh malamai sun yi saɓani akan halaccin hakan zuwa maganganu guda biyu:
1. Ya Halatta; Saboda kasancewar nonon da yake
haramta aure shi ne wanda aka sha kafin yaro ya cika shakaru biyu, saboda faɗin Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wa Sallam
"Shayarwar da take haramtawa, ita ce wacce yaro ya sha saboda yunwa",
Bukhari lamba ta; 5102, ma'ana lokacin da ba zai iya wadatuwa ba daga nono,
saboda shi ne abincin sa, shi kuma wannan ya faru ne bayan mutum ya girma don
haka ba zai yi tasiri ba wajan haramta aure, wannan ita ce maganar mafi yawan
malamai.
2. Bai Halatta ya sha ba; Saboda ko da yaushe
mutum ya sha nonon mace tom ta haramta a gare shi, domin Annabi Muhammad
Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya umarci matar Abu-huzaifa da ta shayar da Salim,
don ta haramta a gare shi, kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta:
2636, tare da cewa a lokacin Salim ya riga ya girma, wannan sai yake nuna cewa
idan babba ya sha nono toh zai yi tasiri wajan haramcin aure. Gaskiyar magana
shi ne maganin abun kawai kada Sha.
Amma a Zancen da ya fi karfi shi ne ya halatta
miji ya sha nonon matar sa, sai dai fa kamar yadda na aka Faɗi a Sama rashin shan Nonon Matar ka shi ne ya fi dacewa
kawai, saboda fita daga saɓanin malamai, mu
Dena ɗaukar Fatawa don an samu wannan yace ayi amma Kuma wancan
yace kada ayi, toh abun da yafi dacewa ga Bawa mai imani da tsoron Allah shi ne
kawai kada Sha Nonon Matar ka a kiyaye dokokin Allah kawai.
Amma duk abun da kake son kayi mata na jin daɗi a lokacin Jima'i da matar ka kana iya yin sa ya halatta
yin hakan in ma Tsotsan Nonon zakayi ba tare da ka Sha ruwan Nonon ta ba,
wannan yayi, amma ka zauna kana shan Nonon ta wai don an ce ma ya halatta toh
akwai matsala fa, a kullum idan an ce ma ga Fatawa me Sauki da mai Zafi, toh ka
ɗauki mai zafin kawai ko Zuciyar ku tana son Wannan abun,
toh kawai ku hakura da aikata wannan abun kawai shi ne yafi dacewa ga mutanen
Kirki, akan ka rufe Ido ka biyewa son zuciya ka ce ai an ce ya halatta kayi,
shikenan kayi ta Shan Nonon Matar ka oga Kuskure ne wannan, Allah ya shirya
Allah ya sa a gane, yana da kyau a kiyaye dokokin Allah.
Don neman Karin bayani duba :
Bidayatul-mujtahid 2\67.
Allah ne mafi sani
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ƘARIN BAYANI
HUKUNCIN MIJI YA
SHA NONON MATARSA: SHIN AURENSU YA MUTU?
TAMBAYA:
Assalamu alaikum. Malam don Allah
mene ne matsayin auren miji da matarsa idan ya zamana mijin ya sha nonon matar
har ruwa ya shiga cikinsa? Shin ta zama mahaifiyarsa ta shayarwa ko kuwa
aurensu yana nan?
AMSA:
A musulunci, mace ta halatta ga
mijinta baki daya in ban da wurare kalilan da nassi ya haramta (kamar saduwa ta
dubura ko lokacin haila da biki). Game da batun shan nono kuwa, ga yadda
bayanin yake:
1. Aurenku Yana Nan (Bai Mutu
Ba): Magana mafi inganci wacce mafi yawan malamai (Jamhurul Ulama) suka tafi
akai ita ce: Shan nonon matar miji ba ya karya aure. Ko da mijin ya shanye
nonon duka, matarsa tana nan matarsa, ba ta zama mahaifiyarsa ta shayarwa ba.
2. Dalilin Da Ya Sa Ba Ya Haramta
Aure: Shari'a ta sanya ka'idoji guda biyu domin shayarwa ta haramta aure:
• Shekaru:
Dole ne shayarwar ta kasance lokacin da yaro yake jariri (kafin ya cika shekaru
biyu).
• Yawa:
Dole ne shayarwar ta kasance har sau biyar masu gamsarwa (a ra'ayin wasu
malaman). Tun da shi miji ya riga ya girma, to wannan nonon ba ya gina masa
jiki ko bargo yadda zai zama dan matar.
3. Shin Ya Halatta A Sha Da
Gangan? Duk da cewa auren bai mutuba, malamai sun rarraba:
• Idan
da nufin wasa ne: Babu laifi idan ya taba ko ya tsotsa yayin wasannin soyayya.
• Idan
ya shiga ciki: Wasu malaman suna ganin abin kyama ne (Makaruhi) miji ya rika
shan nonon matarsa da gangan kamar abinci, amma hakan ba zai taba karya aurensu
ba.
HUJJOJI DAGA HADISAN MANZON ALLAH
(SAW):
Malaman Musulunci sun gina wannan
hukunci ne akan kwararan hujjoji:
HADISI NA DAYA (KA'IDAR SHEKARU):
النَّصُّ النَّبَوِيُّ: عَنْ أُمِّ سَلَمَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهَا
قَالَتْ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: "لَا يُحَرِّمُ
مِنَ الرَّضَاعَةِ إِلَّا مَا فَتَقَ الْأَمْعَاءَ فِي الثَّدْيِ، وَكَانَ قَبْلَ الْفِطَامِ."
(رواه الترمذي وصححه)
FASSARAR HAUSA: An riwaya daga
Ummu Salama (RA) ta ce: Manzon Allah (SAW) ya ce: "Babu abin da yake
haramtawa na shayarwa face abin da ya ratsa hanji (ya zama abinci) daga nono,
kuma ya kasance kafin yaye (kafin shekaru biyu)."
Sharhi: Wannan hadisi ya nuna
cewa tun da miji ya riga ya girma (ya wuce shekaru biyu), duk nonon da ya sha
ba zai sanya shi ya zama dan matar ba.
HADISI NA BIYU (DALILIN YUNWA):
النَّصُّ النَّبَوِيُّ: عَنْ عَائِشَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهَا أَنَّ
النَّبِيَّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ: "انْظُرْنَ مَنْ إِخْوَانُكُنَّ،
فَإِنَّمَا الرَّضَاعَةُ مِنَ الْمَجَاعَةِ." (رواه البخاري ومسلم)
FASSARAR HAUSA: An riwaya daga
A'isha (RA) cewa Annabi (SAW) ya ce: "Ku lura da kyau wajen tantance su
wane ne 'yan uwanku (na shayarwa), domin kuwa shayarwa (da take haramta aure)
ita ce wacce ake yi saboda yunwa."
Sharhi: Wannan yana nufin nonon
da jariri yake sha domin ya rayu kuma jikinsa ya ginu da shi. Miji ba ya shan
nonon matarsa domin yunwa ko don ya rayu dashi.
BAYANI AKAN HADISIN SALIM
(SHAYARWAR BABBA):
Malaman da suka ce shayarwar
babba tana iya yin tasiri sun dogara ne da hadisin da Annabi (SAW) ya ba wa
matar Abu Huzaifa izinin shayar da Salim (wanda babbane). Amma mafi yawan
malamai sun ce wannan keɓantaccen
hukunci ne (Khususiyyah) ga Salim kawai saboda wata lalura, ba zai zama doka ga
sauran mutane ba.
Kammalawa:
• Aure: Aurenku yana nan daram, babu
abin da ya same shi.
• Nasiha: Ya halatta miji ya ji dadi da
nonon matarsa, amma idan ya kiyaye ba ya shan ruwan (madarar) da gangan hakan
ya fi dacewa domin fita daga sabanin malamai.
• Tsafta: Musulunci addini ne na tsafta,
don haka dukkan abin da zai karfafa soyayya tsakanin ma'aurata ba tare da an
keta alfarmar shari'a ba, abin so ne.
WALLAHU A'ALAM
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.