HUKUNCIN YANKA WA ƁARAWON HANNU
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum Malam, wani al'amari ne ya damemu a garinmu. Muna da ɓarayi sosai 'yan rainin hankali saboda goyon baya da suke samu daga wurin wasu mutane. Idan an kama ɓarawo an kaishi wurin hukuma wani lokacin ko kwana uku baza ayi ba, zaka ganshi sun sakeshi ya dawo gari yana cigaba da sha'aninsa. Shi yasa mu matasan unguwarmu muka yanke shawarar cewa duk ɓarawon da muka kama zamu yi masa tsinannen duka, ko kuma mu yanke masa hannu ko kafa, ko kunnuwansa ko wani waje a jikinsa. Shin idan munyi hakan babu laifi, tunda dukiyoyinmu suke sacewa kuma mukan kamasu da abun ahannunsu?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatulLahi wa barakatuhu.
Da farko dai ina yi maka nasiha tare da ni kaina
da dukkan Musulmai cewa Wajibinmu ne muji tsoron Allah afili da ɓoye, kuma mu kiyaye dokokinsa koda sunci karo da son
zuciyarmu.
Hakika Allah shi yayi umurni cewa ayanke hannun ɓarawo acikin Suratul Ma'idah (ayah ta 38). Allah yace :
وَالسَّارِقُ وَالسَّارِقَةُ فَاقْطَعُوا أَيْدِيَهُمَا جَزَاءً
بِمَا كَسَبَا نَكَالًا مِّنَ اللَّهِ وَاللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ
"DA ƁARAWO DA ƁARAUNIYA KU
YANKE HANNAYENSU. WANNAN SAKAMAKO NE BISA ABINDA SUKA AIKATA, (KUMA) AZABA CE
DAGA ALLAH. HAKIKA ALLAH MABUWAYI NE (CIKIN AYYUKANSA), MAI HIKIMA NE (CIKIN
HUKUNCINSA)".
To amma fa ba'a bada damar cewa kowanne mutum idan
ya kama kowanne ɓarawo ya zartar
masa da hukunci shi dashi ba. A'a hukumar Musulunci kaɗai keda wannan damar. Misali kamar Alqali ko Sarkin Yanka
(wanda keda matsayin Amirul Mu'uminina acikin mutanen dake karkashinsa).
Sannan kuma ba kowanne irin ɓarawo ake yanke wa hannu ba. Idan ɗan fashi ne (wato Armed robber) wannan hukuncinsa daban,
idan ɗan danfara ne ko mai yankan aljihu shima hukuncinsa
daban, idan kuma mai fasa gidan mutane ne ya shiga, shi ne wanda ake yanke wa
hannu ɗaya, amma idan abinda ya sata ɗin yakai nisabin da shari'a ta ajiye. Misali a mazhabin
Malikiyyah shi ne 'RUB'U DINAR' Wato kimar mafi karancin sadaqi kenan.
Addinin Musulunci bai bada damar mutum ya rika ɗaukar doka a hannunsa ba. Ya kamata a kula sosai kada
abiye wa son rai. Duk sanda kuka kama ɓarawo ku mikashi
wajen hukumar da tafi kusa daku, sannan ku tsaya akan maganar har sai kun
tabbatar da anyi masa hukuncin da ya dace dashi. Idan kun tabbatar ba'a yi muku
adalci ba, zaku iya ɗaukaka Qara zuwa
wata kotun ko kuma ku tuntubi hukumar sauraron koke-koke ko kungiyoyinku na
jama'ar gari zasu iya shiga cikin maganar domin tabbatar da adalci.
Lokaci ɗaya ne aka yarda
zaka iya ɗaukar mataki akan ɓarawo. Shi ne idan ya shigo gidanka da makami kuma yana
nufin kasheka ko yayi maka rauni, to zaka iya ɗaukar mataki kaima domin kare kanka ko iyalanka ko
dukiyarka, kuma koda ɓarawon ya
kasheka, to mutuwar shahada kayi. Idan kuma kaine ka kasheshi, to jininsa ya
zuba abanza.
Mutanen dake amfani da matsayinsu ko dukiyarsa
wajen goyon bayan miyagun dake aikata ɓarna acikin
al'ummar musulmai, wajibi ne suji tsoron Allah su dena domin yin hakan yana
Qara bunkasa ayyukan ɓarna da
ta'addanci atsakanin mutane, kuma hakan babbar hanyar lalacewar zamantakewa ne.
Allah yana cewa :
...وَتَعَاوَنُوا عَلَى الْبِرِّ وَالتَّقْوَىٰ وَلَا تَعَاوَنُوا
عَلَى الْإِثْمِ وَالْعُدْوَانِ وَاتَّقُوا اللَّهَ إِنَّ اللَّهَ شَدِيدُ الْعِقَابِ
...Kuma ku taimaki junã a kan aikin ƙwarai da taƙawa. Kuma kada ku
taimaki juna a kan zunubi da zãlunci, kuma ku
bi Allah da taƙawa. Lalle ne
Allah Mai tsananin uƙũba ne.
WALLAHU A'ALAM.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
HUKUNCIN
KASHE ƁARAWO:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum malan barka da safiya Wai malam
hukuncin kisa da ake yiwa ɓarawo idan an
kama shi, ya hallata ko kuwa bai hallatta a kashe ɓarawo ba? Allah ya karawa malan sani.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikum assalam. Bai halatta ba, saboda a
Shari'a hukuncin ɓarawo shi ne a
yanke masa hannu, idan ya saci nisabi daga inda ba shi da iznin shiga.
Sannan yanke hannun Ɓarawo yana hannun Hukuma, ita ce take da hakkin
zartar Masa da haddi, hakan sai ya nuna abin da mutane suke Yi kuskure ne.
Idan Ɓarawo ya yi kokarin yin ta’addanci aka
kashe shi wajan kai ɗauki babu
matsala in an kashe shi.
Allah ne Mafi sani
Dr. Jamilu Yusuf Zarewa
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.