𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahmatullah
Don Allah ina da tambaya. Wai haramun ne saurayi ya yi wa budurwarsa kayan sallah?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikis Salaam Wa Rahmatullahi Wa Barkatuhu:
Shi Ɗinkin Sallah, Haƙƙin Iyayen ki ne su Ɗinka miki kayan Sallarki da duk wasu hidimar da yakamata ace an yiwa Mace
toh haƙƙin iyayenki ne su yi
miki komai matukar suna da halin su yi, toh haƙƙin su ne suyi miki dolen su ne wannan.
Sabida haka Ɗinki Sallah ba haƙƙin Saurayin ki ba ne, ace ya Ɗinka miki kayan sallah ko ya yi miki Hidimar Sallah koda kuwa shi ne ya
kawo kuɗin Auren ki Sadakin sa na hannun ki, toh ba haƙƙin sa ba ne ya yi hidima
da duk wasu abubuwan da yakamata ayiwa Mace, wannan Haƙƙin Iyayen ki ne domin har yanzu ke ba za ki zama
Matar sa ba tukuna bai da iko a kanki kamar yadda iyayen ki suke da shi a
yanzu, don haka haƙƙin iyayen ki ne suyi miki komai na rayuwa wadda Mace ta ke Bukata a rayuwar
ta, amma bawai Saurayin ki ba.
Yi Miki Ɗinki, bayar da Kuɗin kitso, kuɗin kwalliya, kuɗin Lalle Gyaran
gashi da sauran su duk waɗannan Haƙƙoƙin iyayen ki ne suyi miki su idan suna da Halin
yi, amma bawai haƙƙin Saurayin ki ba ne.
Idan an Ɗaura Auren ki da shi kin zama Matar sa, misalin ace kin zo gidan ku hutu,
toh nan ne yake zama wajibi ne a kansa ya yi miki indai yana da shi, nan Kuma
babu Ruwan iyayen ki da ke, ko da kuwa suna da shi ba suyi ba sai sun ga dama
su yi miki, domin ba haƙƙin su ba ne a yanzu suyi miki, sabida kin zama Matar wani haƙƙin ya fita daga kansu haƙƙin sa ne ya yi miki.
Sabida a yanzu da kika zama Matar sa ke kin fita daga haƙƙin iyayenki Kin koma haƙƙin sa ne ya yi miki komai na rayuwar ki dole ne ya
yi idan yana da shi.
Don haka idan Saurayin da ya kawo kuɗin Auren ki, toh idan bai yi miki Hidimar Sallah, ya yi miki
Ɗinki, ya ba ki Kuɗin da za ki gyara jikin ki a gyara gashin Kai ayi kitso
kwalliya, ayi Lalle, da Kuɗin da za ki yi
girki ko wasu hidimar Sallah ba, toh kada kiyi fushi kar ki ɓata Rai akan wannan, ko kuma ki ce wai ah haka zai iya
rike ki? Ko kuɗin sabulu wannan Bai taɓa ba ki ba a Sallah balle kuɗin barka da Sallah, kiyi fushi ki tayar da jijiyar wuya
kina cewa ai ba zai iya rike ki ba ko ya Aure ki, wannan Kuskure ne domin har
yanzu ba ki zama Matar sa da zai iya miki Hidima irin wannan ba, Haƙƙin Iyayen ki ne suyi
miki komai bawai Saurayin ki ba.
Shi kyautatawa a rayuwa yana dakyau Kuma duk Mace
tana son Miji me kula da rayuwar ta gurin kyautatawa rayuwar ta komin kankantar
Abu ya siyo ya ba ta, ta hanya Siya mata abubuwan da ta ke so a irin wannan
lokacin, Amma ki Sani cewa fa bawai Haƙƙin sa ba ne haƙƙin iyayen ki ne suyi miki komai na rayuwar ki domin kina gaban su ne, ke ba
za ki zama Matar sa ba tukuna wadda haƙƙin ki zai rataya a kansa ace dolen sa sai ya yi miki.
Kin ga daga ranar da kika zama Matar sa an Ɗaura Auren ku ko ba ki
tare zuwa gidan sa ba, toh yanzu wajibi ne a kansa ya yi miki komai haƙƙin sa ne a yanzu ya yi miki
domin kin fita daga haƙƙin iyayen ki kin koma haƙƙin Mijin ki.
Amma idan shi ne ya yi Ra'ayin kansa ya Ɗinka ya kawo miki bawai
kene kika tambaye shi ba, sai ya Ɗinka Kayan Sallah da Kuɗin kwalliyar ki,
Gyaran jikin ki komai ya haɗa ya kawo
miki, shikenan sai ki sa hannunki ki karɓa ba Haramun ba ne, ki karɓa tare da sanyawa rayuwar sa Albarka sosai koda kuwa abun
da ya yi miki bai burge ki ba, wato misalin ya siyo irin masu araha ya kawo
miki kin Raina abun da ya miki, toh kada ki zage shi ko ki kuce kyautar da ya
yi miki ko rika gayawa ƙawayen ki wannan matsaya shi ne ku duba dan abun da ya yi min har yana
Alfahari ya miki abu, kawai kin Sanya Albarka tare da nuna Godiyar ki da
wadatuwar ki da jinjina masa.
Sa'annan a matsayin ki na Mace Budurwa wadda kike
son Namijin da idan ya Aure ki kina son ya kyautatawa rayuwar ki ya rike ki
tsakanin sa da Allah da gaskiya da Amana, wadda zai kula da rayuwar ki sosai
yadda kike so, toh abun da za ki duba anan shi ne, shin da ya yi miki kayan
Sallah ya kashe miki kuɗi sosai a
Sallah, don Allah ki tambaye shi yayiwa Mahaifiyar sa haka? Ki sani cewa idan
kin yarda saurayin ki yana miki Hidima a gidan ku, toh ko ya Aure ki ba zai iya
kula da rayuwar ki irin yadda yake miki a gidan ku ba.
Sa'annan ki Sani cewa fa kema Nan gaba Uwa ce shin
za ki yarda ace yau Ɗan ki bai yi miki komai ba a ranar Sallah, Amma ga shi kuɗin da zai kashewa Budurwar sa a kalla sai yafi dubu
hamsin (50k) don Allah idan kin ji haka cewa Ɗan ki yayiwa budurwarsa irin wannan ke bai yi miki
ba ya za ki ji a ranki? Sa'annan duk wadda zai yiwa Budurwar sa irin wannan
amma ga Mahaifiyar sa 2k tak ta tambaye shi zatayi siya Lalle ko Sabulu ko man
gashi ta gyara kanta ya ce mata babu, don Allah wadda yayiwa Mahaifiyar sa irin
wannan ke kuma ya faranta miki ya kashe miki kuɗi Sama da 50k ko 20k kina Jin daɗi ya yi miki abun da kike so, kina ganin idan ya Aure ki
zai iya rike ki ne? Wallahi karya ne idan ma ke kin ɗauka ai tunda yana Mutuwar son ki Yana kaunar ki, yana da
zuciyar ya yi miki komai duk abun da kike so a rayuwar ki ai idan ya Aure ki ma
hakane, wallahi kin Yaudari kanki kin cuci kanki kin Zalunci kanki. Yadda kika
ga bai yiwa Mahaifiyar sa ba ya zo yana miki, toh haka idan ya Aure ki ya samu
abun da yake so a jikin ki Bukatar sa ta biya, shikenan ba zai taɓa kyautatawa rayuwar ki sosai kamar irin yadda yake miki
a lokacin da kike gidan ku ba.
Saurayi yayiwa Budurwar sa kayan Sallah ba Haramun
ba ne abu ne me kyau kamar yadda nace a sama, Amma haƙƙin iyayen ki ne ki san da wannan, kin ga idan
misalin an ba shi ke zai Aure ki, sa'annan kuma kin tabbatar da cewa yayiwa
Mahaifiyar sa ɗinkin Sallah ɗin da wasu hidimar,
toh babu laifi idan ya yi miki kema ki sa Hannu ki karɓa kiyi masa fatan Alkhairi a rayuwar sa, duk da dai shi
ma bawai wajibi ne yayiwa Mahaifiyar sa ba domin itama haƙƙin Mahaifin sa ne ya yi mata, toh amma ai tunda
sun haihu, ai yakamata itama ta samu ace Ɗan ta ya yi mata.
Amma idan har ba'a ba shi ke ba, Ma'ana ba'a ma
San sa a gidan ku ba kawai kuna chatting ne da shi ko kuma Kuna Haɗuwa akan Hanya ne kuyi Hirar ku ba wadda ya sani,
sa'annan bai yiwa Mahaifiyar sa ɗinki ba, toh ke
kanki Budurwa idan kin San me kike yi Idan an kawo miki irin wannan kayan ba za
ki taɓa karɓa ba, matukar
kin san wacece ke a rayuwar ki.
Sa'annan Ko da ma ace shi zai Aure ki, ba zai miki
kayan Sallah ba domin har yanzu kina gaban iyayen ki ne haƙƙin iyayen ki suyi miki komai, toh idan ko ya yi ya
kawo miki kina iya tambayar sa ka yiwa Mahaifiyar ka? idan ya ce eh shikenan
kina iya karɓa idan ya ce a'a ki ce
ba ki so ko zai mutu ki bar sa da kayan sa ya Koma ya je ya fara yiwa
Mahaifiyar sa tukuna, domin sune suka fi Cancanta da ya yi su a yanzu bawai ke
ba.
Yayiwa Mace kayan Sallah ba shi yake nuna cewa
saurayin ki na matukar son ki yana kaunar ki yana ji da ke, damuwar ki ko
matsalolin ki kab yana kawar ki da su, ko hakan na nuna zai iya kula da ke a
rayuwar ki, hasalima wannan shi yake nuna cewa ya mayar da ke Mai kwaɗayi ce, kamata ya yi ace kin ƙi karɓa, amma ya je
yayiwa Mahaifiyar sa yafi akan ya yi Miki.
Idan shi Saurayin ya San me yake yi wallahi daga
lokacin da kika ce masa ba ki son abun hannun sa dalilin cewa kin ce dole sai
yayiwa iyayen sa idan ma yana son ya yi miki sai ya miki sai ya yi daga baya,
toh zai ji kin Kara shiga zuciyar sa ya gane cewa ai ke ɗin ta musamman ce kina son sa da Rahmar Allah tunda har
kina nuna masa hanyar da yafi dacewa tun yanzu, amma idan ke kawai matsalar ki
ayi miki ne babu Ruwan ki da sanin cewa yayiwa Mahaifiyar sa ne ko bai yi ba,
ke ba damuwar ki ba ne tunda Yana son ki yana kaunar ki yana kula da ke ai
shikenan, toh Wallahi kin yi asara, abu na farko Saurayi ba zai taɓa ganin Ƙimar ki ko Mutuncin ki ba, kullum a Yar kwaɗayi zai ɗauke ki,
sa'annan idan ya samu Labarin ba shi zai Aure ki ba kin ga ba zai kashe Kuɗin sa a banza su tafi a iska ba, me tausayin ki ne zai ce
ya bar ki da Allah ya domin kin Yaudare shi, Kuma ko kin yi Aure sai kin gagara
samun zaman lafiya a gidan Mijin ki dalilin wannan, wadda baya Tausayin ki
shine zai neme ki ta kowane hanyar ne dole sai ya yi Zina da ke domin ya fance
Kuɗin sa da yake kashe miki kullum ya ce ai ba zai yi aikin
Banza ba, shiyasa wasu Yan Mata idan za suyi Aure kafin a Kai su gidan Miji sai
sun je gurin tsohon saurayin su ya yi duk abun da yake so da su tukuna wai sun
sallami juna yanzu ayi Zina da ke.
Abu na biyu shi ne indai Namiji yana ba ki Abu
kina karɓa toh Mutuncin ki Ƙimar ki da Martaban ki kab suna zubewa a idon sa, sa'annan idan mutumin
Banza ne dalilin kayan sa da kike karɓa ya samu hanyar
da zai yi Zina da ke a sawwake kenan, domin duk lokacin da ya ce zai rabu da ke
idan ba ki ba shi kanki ba ke gani za ki yi duk irin nuna kulawar sa a kanki
duk wahalar da yake Sha a kanki ai idan kin yi masa haka ba kiyi masa Adalci
ba, sa'annan ya ce ai Auren ki zai yi mene ne a gurin don kin ba shi kanki?
shikenan kina sake jikin ki ya yi Zina da ke ya yi tafiyar sa kuɗin sa da ya kashe miki ya fitar da su domin ya lalata
Budurcin ki, ba zai Aure ki ba ya tafi ya bar ki har abada, idan ma ya dawo toh
sai dai idan zai ce ki sake cewa ki ba shi kanki ya yi Zina da ke.
Sabida haka Yan Mata a ji tsoron Allah ku Rika
cire kwaɗayin ku akan komai na hannun saurayin ki komai ma, idan
ya Aure ki wannan dole ne ya yi miki, haka iyayen Yan Mata ku dena cewa wai
idan Saurayin Yar ki bai yi mata Hidima ba, ku Rika Zagin Yar ku kuna Zagin
wadda yake neman ta ai bai da zuciya bai damu da ke ba a haka zai Aure ki ya
rike ki, ki Rika cewa Yar ke ba ki ga yadda Samarin ƙawayen ki suke kashewa ƙawayen ki kuɗi ba? amma
wannan matsaya shi ne bai da zuciyar yi, suyi ta Zagin sa ana kutse shi Iyaye
wannan Kuskure ne wallahi, yana ɗaya daga cikin
abun da ya sa ake yin Zina da Yar ki ke ba ki Sani ba, don haka ko Yar ki an
kawo mata irin wannan kamata ya yi ace kin hana ta karɓa, kin yi mata fada sosai ki nuna Ɓacin ran ki over, kada ta sake aikata irin wannan
Kuskuren na karɓan Abu a hannun
Namiji, amma bawai kene za ki ce wai ki ce ayi miki, ko kuma meyasa bai yi miki
ba ke ba za ki yi masa magana ba wannan Kuskure ne Iyaye. Dafatan Kin gane
ko???? Allah ya tsare mu ya kare mu.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.