𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Malam Wallahi ni ne ranan muna tare da iyali na, sai ta ce min nasha maganin da zai kara min girman azzakari na da kuma tsayin ta, hakan yasa ni na washe ta kuma har nace mata wannan zai iya saka na zargeta, amma ta yaya tasan wannan maganan? sai ta ce wai taji ana fada akwai maganin ne a radio. Gaskiya yanzu Malam na rasa yaya zanyi shiyasa nace don Allah indai akwai yadda za'ayi azzakari na ta kara tsayi da girma ka taimaka min, domin ni bani da matsalan rashin karfin azzakari sai dai gaskiya azzakari na bai wuce 9 centimeter ko kuma ince tsayin ruler karami na cikin math-set. Saboda haka don Allah Malam akwai hanyan da zanyi azzakarina ta karu? Malam kuma wanne shawara za ka bani akan wannan maganan da ta gaya min domin har yanzu banajin sha'awanta kaman da, thank you very much for your contribution. Malam don Allah ina bukatan amsar ka, domin nafi jin aminci tattare da maganganun ka da hujjoji da kake bujirowa da su. Nagode. Allah ya kara maka Imani.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Gaskiya ɗan'uwa Ya kamata
ka godewa Allah tunda ya baka cikakkiyar lafiya da ikon yin aure, sannan ya
baka matar da ka aura, harma kuka samu daman biyan bukatunku na sha'awa.
Idan ka duba za ka ga wasu da dama suna da lafiyar
jiki, amma kuma mazakutarsu batta da
cikakkiyar lafiya. Wasu kuma suna da cikakkiyar
lafiyar amma Allah bai basu ikon yin auren ba, har ranar mutuwarsu. Bai kamata
ka ji haushin matarka saboda ta baka wannan shawarar ba. Watakila akwai dalilin
da yasa ta baka shawarar. Watakila kana da WUƘA MAI KAIFI ne, amma baka san yadda za ka yi aiki
da ita ba. Don haka ya kamata kayi tunani akan wasu halattattun hanyoyin da za
ka bi domin gamsar da ita ayayin da kuke Jima'i. MISALI: Kamar gabatar da
wasanni, da kalamai na soyayya, da chanja position alokacin Jima'i. Duk waɗannan suna sanya Ma'aurata su samu Gamsuwa da Junansu.
Kabi waɗannan shawarwarin. Kar ka wahalar da kanka wajen neman
maganin Ƙarin Girman Mazakuta.
Tsawon da kake dashi ayanzu ma ya isheka.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.