𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Dama Ina da tambayane shin mene ne hukuncin wadda take da aure Kuma take cewa tana son wani daban awaje misali ace shi ɗin tsohon saurayintane Kuma Allah baiyi auren nasu yayuwuba har takaima ayanzu tana da mijin amma Kuma har yanzu bata daina Kiran wance tsohon saurayinnata da masoyiba, mene hukuncinta shin auran zai'tabuwa adalilin Hakan? Allah ya Karawa malam sani.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Hukuncinta shine mai cin amanace. Domin kuwa anan
taci amanar mijinnata saboda kula tsohon saurayinta da takeyi a can waje
batareda sanin mijinba. Wannan duk yana ɗaya daga cikin
planning da shaiɗan yake don ya
raba aure tsakanin mata da miji. Kuma hakan ya nuna ita ɗin ba mumina bace ba, don haka bazata yi nasara a
rayuwarta ba indai har bata tuba ta daina ba, meyasa akace ba mumina bace ba ?
Mu duba me Allah ya ce a cikin Suratul Mu'uminun ayata 8:
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ
(Kuma waɗanda suke, sũ ga
amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne).
Rashin tsare alƙawari da kuma rashin riƙon amanar auratayya shine zaisa a kirata da mai
cin amana kuma hakan yana nufin bazatayi nasara ba idan bata tuba ba, domin
kuwa Allah SWT ya zayyano wasu daga cikin masu nasara a rayuwar duniya da ta
lahira a cikin ayar farkon Suratul Muminun:
قَدْ أَفْلَحَ الْمُؤْمِنُونَ
(Lalle ne, Mũminai sun sãmi babban rabõ)
Wanda su waɗannan muminan
sune masu gadon Aljannatil Firdous kamar yanda Allah SWT ya fada a cikin ayata
10 zuwa ta 11 a Suratul Muminun:
أُولَٰئِكَ هُمُ الْوَارِثُونَ الَّذِينَ يَرِثُونَ الْفِرْدَوْسَ
هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ
(Waɗannan, sũ ne
magãda. Waɗanda suke gãdõn
(Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne)
Sannan kuma akwai hadisai sahihai da suka tabbata
daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam akan illar cin amana, ɗaya daga hadisan shine hadisin da Bukhari ya kawoshi a
cikin littafinsa Al-Adabul Mufrad littafi na 8, volume na 73, mai lambata 117
wanda aka rawaito daga Abu Hurairah RA wanda ya ce Annabi Sallallahu Alaihi
Wasallam ya ce alamomin munafuki guda 3 ne, na 1 idan yayi zance sai yayi ƙarya, na 2 idan aka
amince masa sai yayi ha'inci na 3 idan yayi alƙawari sai ya saɓa.
Anyiwa Shaikh Umar Sani Fagge tambaya akan cin
amana, ya ce: A ranar lahira za'a kawo amana a ɗora akan siradi, duk wanda yaci wannan amanar to sai ta
dinga zabtare naman jikinsa gwargwadon yawan amanar nan da yaci anan duniyar.
To kinga anan mijin ya amince mata da manufar idan
ya aureta bazata kula wasu a waje ba ballantana kuma tsohon saurayinta, anan ta
zamo munafuka saboda cin amanar da tayi. Don haka Idan har tana son nasara a
rayuwar nan da ta can sai ta tuba ta koma ga Allah domin samun rabo fiddunya
wal akhira
Muna roƙon Allah yasa ta gane tayi taubatun nasuha.
Wallahu ta'ala a'alam
Amsawa:
✍Usman Danliti Mato, Usmannoor_Assalafy_
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.