Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Matar Aure Da Take Soyayya Da Tsohon Saurayinta

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Dama Ina da tambayane shin mene ne hukuncin wadda take da aure Kuma take cewa tana son wani daban awaje misali ace shi ɗin tsohon saurayintane Kuma Allah baiyi auren nasu yayuwuba har takaima ayanzu tana da mijin amma Kuma har yanzu bata daina Kiran wance tsohon saurayinnata da masoyiba, mene hukuncinta shin auran  zai'tabuwa adalilin Hakan? Allah ya Karawa malam sani.

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Hukuncinta shine mai cin amanace. Domin kuwa anan taci amanar mijinnata saboda kula tsohon saurayinta da takeyi a can waje batareda sanin mijinba. Wannan duk yana ɗaya daga cikin planning da shaiɗan yake don ya raba aure tsakanin mata da miji. Kuma hakan ya nuna ita ɗin ba mumina bace ba, don haka bazata yi nasara a rayuwarta ba indai har bata tuba ta daina ba, meyasa akace ba mumina bace ba ? Mu duba me Allah ya ce a cikin Suratul Mu'uminun ayata 8:

وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ

(Kuma waɗanda suke, sũ ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarwa ne).

Rashin tsare alƙawari da kuma rashin riƙon amanar auratayya shine zaisa a kirata da mai cin amana kuma hakan yana nufin bazatayi nasara ba idan bata tuba ba, domin kuwa Allah SWT ya zayyano wasu daga cikin masu nasara a rayuwar duniya da ta lahira a cikin ayar farkon Suratul Muminun:

قَدْ أَفْلَحَ الْمُؤْمِنُونَ

(Lalle ne, Mũminai sun sãmi babban rabõ)

Wanda su waɗannan muminan sune masu gadon Aljannatil Firdous kamar yanda Allah SWT ya fada a cikin ayata 10 zuwa ta 11 a Suratul Muminun:

أُولَٰئِكَ هُمُ الْوَارِثُونَ ۝ الَّذِينَ يَرِثُونَ الْفِرْدَوْسَ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ

(Waɗannan, sũ ne magãda. Waɗanda suke gãdõn (Aljannar) Firdausi, su a cikinta madawwama ne)

Sannan kuma akwai hadisai sahihai da suka tabbata daga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam akan illar cin amana, ɗaya daga hadisan shine hadisin da Bukhari ya kawoshi a cikin littafinsa Al-Adabul Mufrad littafi na 8, volume na 73, mai lambata 117 wanda aka rawaito daga Abu Hurairah RA wanda ya ce Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce alamomin munafuki guda 3 ne, na 1 idan yayi zance sai yayi ƙarya, na 2 idan aka amince masa sai yayi ha'inci na 3 idan yayi alƙawari sai ya saɓa.

Anyiwa Shaikh Umar Sani Fagge tambaya akan cin amana, ya ce: A ranar lahira za'a kawo amana a ɗora akan siradi, duk wanda yaci wannan amanar to sai ta dinga zabtare naman jikinsa gwargwadon yawan amanar nan da yaci anan duniyar.

To kinga anan mijin ya amince mata da manufar idan ya aureta bazata kula wasu a waje ba ballantana kuma tsohon saurayinta, anan ta zamo munafuka saboda cin amanar da tayi. Don haka Idan har tana son nasara a rayuwar nan da ta can sai ta tuba ta koma ga Allah domin samun rabo fiddunya wal akhira

Muna roƙon Allah yasa ta gane tayi taubatun nasuha.

Wallahu ta'ala a'alam

Amsawa:

Usman Danliti Mato, Usmannoor_Assalafy_

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments