𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, Malam Barka da yau dafatan kana cikin koshin lafiya, Allah ya sakawa malam da Alkhairi, dan Allah malam tambaya na zo da ita ina neman Amsa, ga tambayar kamar haka; Mace ce yaranta huɗu amman kafin aurensu ita da mijinta suna Zina so batayi istibra'i ba ankayi auren har Yara huɗu to yanzu auren nasu valid ne ko invalid?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu;
Wannan auren nata bai yiwu ba dole a warwareshi ta
je tayi Istibra'i sa'annan a sake daura shi.
MA'ANAR ISTIBRA'I: Istibra'i shine neman sanin
kububtar mahaifa daga ɗaukar ciki. ko
kuma zaman jiran a haife cikin da mace ke ɗauke da shi bayan tabbatar da samuwar sa.
Idan namiji ya sadu da mace wadda bata hanyar aure
ba, ta hanyar zina ne ko kuma fyaɗe toh wajibi ne
sai ta yi itibra'i kafin mijin ta ya kusance ta in tana da aure ko kuma kafin
ta yi auren Akwai fuskoki biyu da suka nuna rashin halaccin auren:
1. FUSKA TA FARKO: A karkashin Addinin Musulunci
bai halatta a Ɗaura ma mace
aure da wani sabon Miji ba, har sai ta tabbatar da cewar babu komai a cikin
mahaifarta. a Bisa wannan dalilin shi ya sa Mata suke yin iddah bayan sun fita
daga hannun Mijin su kafin su sake aurar wani Mijin daban.
Hakanan duk Matar da ta yi Zina, ko budurwa ce ko
bazawara, toh bai halatta a Ɗaura Mata aure ba har sai tayi Istibra'i. Wato tayi Jini uku, ko kuma a Ƙalla jini guda (a fa'dar
wasu Maluman).
Toh idan har Mace ta yi Aure ba tare da yin
Istibra'in nan ba, Malamai sun ce auren bai yiwu ba. Ba za'a kira irin wannan
zaman da sunan "AURE" ba. Har sai an warwareshi ta je ta yi Istibra'i
sannan a sake ɗaura sabon aure da sabon
sadaki Allah ya shirya Zina masifa ce da Bala'i Yan Mata ku Ji tsoron Allah
wallahi.
2. FUSKA TA BIYU: Duk Matar da ta zamanto ita
Mazinaciya ce, toh bai halatta a Ɗaura mata aure da cikakken Mumini wanda ba ya Zina ba.
Hakanan duk Namijin da ya zamanto shi ba Mazinaci ba
ne, bai halatta ya auri Matar da bata yin Zina ba. Sai dai idan sun tuba
Sahihin tuba irin tubar da ba za'a sake koma Ruwa ba, Ita Mazinaciyar sai ta yi
istibra'i. Sannan zai halatta Mumini ya aure ta. Allah ne ya fada a cikin ayah
ta Uku a cikin Suratun Nuur.
الزَّانِي لَا يَنكِحُ إِلَّا زَانِيَةً أَوْ مُشْرِكَةً وَالزَّانِيَةُ
لَا يَنكِحُهَا إِلَّا زَانٍ أَوْ مُشْرِكٌ وَحُرِّمَ ذَٰلِكَ عَلَى الْمُؤْمِنِينَ
Mazinãci bã ya aure fãce da mazinãciya kõ
mushirika, kuma mazinãciya bãbu mai aurenta fãce mazinãci kõ mushiriki. Kuma an
haramta wannan a kan mũminai. (Suratul Nur Ayata 3).
Al Imam Ahmad bn Hanbal ya ruwaito hadisi daga
Sayyiduna Abdullahi bn Amru bn Al-Aas (R.A) ya ce, "Wani Mutum Mumini ya
nemi izinin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) akan yana so zai auri
wata Mata mai suna UMMU MAHZOUL wacce ta kasance kowa ya san tana yin Zina. Sai
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya karanto masa wannan ayar ta cikin
Suratun Nuur cewa; "MAZINACI BA ZAI AURA BA SAI DAI MAZINACIYA KO
MUSHRIKA. KUMA MAZINACIYA BABU MAI AURENTA SAI MAZINACI KO MUSHRIKI. KUMA AN
HARAMTA WANNAN BISA MUMINAI". (A duba Hadisi na 11359 a cikin Sunanul
Kubrah ta Imamun Nisa'iy).
Hakanan akwai wani Sahabi mai Suna MARTHAD IBNU
ABI MARTHAD (R.A) ya taɓa neman izini a
wajen Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) cewa yana so zai auri wata Mata mai
suna 'UNAAƘ" ta
kasance Mazinaciya ce a garin Makkah. Sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa
Sallam) ya yi shuru bai ba shi amsa ba, har sai da wannan ayar ta cikin Suratun
Nuur ta sauka. (A duba Sunanu Abi Dawud hadisi na 2051. Da kuma Sunanun Nisa'iy
juzu'i na 6 shafi na 66 a cikin kitabun Nikahi).
Duk da cewa akwai Malaman da suke ganin cewa
wannan ayar Mansukhiyah ce, toh amma Bisa waɗannan hujjojin ne Malamai irin su Imamu Ahmad suka
dogara. Sun ce bai halatta a auri duk Matar da tayi zina ba, har sai bayan ta
tuba. Don Haka auren nata bai ɗauru ba.
Matsayin shi Saurayin shine sunan sa Mazinaci Kuma
lallai laifin zinar yana nan a kansa. Idan bai tuba ba, yadda ya yi haka shima
za'ayi masa. Kafin kuma ya koma ga Allah ya karɓi sakamakon abin da ya aikata.
Yan Mata Zina Bala'i ce, Zina masifa ce, wallahi
akan ki Yarda da saurayin ki ya yi Zina da ke gara kin Mutu yafi miki, Saurayin
ki ko ya kawo a kanki Indai ya ce miki toh me ya rage ai kin zama nashi ki ba
shi kanki, wallahi ki ja masa layi ya hakura har sai an ɗaura Auren ku tukuna kin zama nashi kafin ya yi duk abun
da yake so da ke.
Amma a yanzu wai ke kin sake bakin cewa wai
Saurayin ki Yana Mutuwar Son ki ai kuna son junan ku kamar yaya ai Auren ki zai
yi, don haka ya yi ta bin ki ya ce ki ba shi kanki tunda shi zai Aure ki,
wallahi idan kin yarda kin ba shi kanki kin yi Asara mafi girman asara a
rayuwar ki, sa'annan ke ba ki San waye yake son ki ba, Kai wallahi ba ki San mene
ne ake kira Soyayya ba, da ace kin san me ake kira Soyayya toh ba za ki taɓa Kiran wadda zai yi Zina da ke ya bata rayuwar ki gaba ɗayan sa ki ce wai shi ne yake matukar son ki ba.
Duk wadda yake son ki tsakanin sa da Allah, yake
son ki zama Matar sa wallahi Hannun ki wannan tsoron tabawa zai ji, duk wadda
zai ce ki ba shi kanki ya yi Zina da ke ai shi ne zai gane cewa lallai kina son
sa, ko kuma ai Auren ki zai yi toh idan kina neman Makiyin ki Wadda zai iya
kashe ki, sa'annan dãman jikin ki yake so bawai ke yake so ba, kuma yana samun
jikin naki shikenan ko ya kawo duniya ne a kanki haka zai bar ki da su tunda ke
mai kwaɗayin ce ku ji tsoron Allah Yan Mata da Matan Aure.
Zina masifa ce da Bala'i, ba za ki gane hakan sai
ranar da kika aikata shi ki dawo kina yin nadamar da ba zai amfane ki ba,
rayuwar ki gaba ɗayan sa ya tashi
a iska an miki tabon da har ki koma ga Allah ba za ki taɓa mantawa, an miki illar da ke kanki kin tuba amma kullum
zargin kanki da kanki kike yi, an miki tabon da ke kanki za ki dawo tamkar
mahaukaci duk wannan illar Zina ce Wallahi ku ji tsoron Allah duk Karfin
Sha'awar ki indai Saurayi da Zina ya zo miki ki rabuwa da shi ko da kuwa Karfin
Sha'awar ki zai sa ki mutu gara ki mutu ba ki aikata Zina ba akan ki biyewa
zuciyar ki da na saurayin ki kiyi Zina. Allah ya tsare.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku
kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.