Citation: Garba S.A. (2024). Waƙoƙin Shata a Shirye-shiryen Rediyo. Ginshiƙin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa, 270-279. www.doi.org/10.36349/djhs.2024.v03i01.033.
WAƘOƘIN
SHATA A SHIRYE-SHIRYEN REDIYO
Sabi’u Alhaji
Garba
No. 47, Titin
Tafida, Ƙaramar Hukumar Mulkin Bukkuyum, Jahar Zamfara
Tsakure:
Danganataka a tsakanin gidajen
rediyo da waƙoƙin
baka abu ce da ta daɗe
a ƙasar
Hausa. A kan haka ne wannan takarda ta ƙudiri anniyar binciko matsayin Alhaji
Mamman Shata da waƙoƙinsa a wasu fitattun gidajen rediyo. An yi wannan binciken ne
ta hanya lura da shirye-shiryen gidajen rediyon inda aka taskace shiraruwa guda
ashirin da ake samun shata da waƙoƙinsa
a cikinsu. Haka kuma an nazarci ayyukan da suka shafi shata da rayuwarsa
ta waƙa.
A ƙarshe
takardar ta gano irin yadda aka samar da
rediyo a nahiyar Afirka da Najieriya da Arewacin Najeriya da yadda rediyon ya
tasirantu da waƙoƙin Hausa. Mun ga yadda aka tabbatar da kasantuwar waƙoƙin
Shata tun kafin kafuwar gidan rediyo a ƙasar Hausa da yadda rediyon ya ƙara yaɗa waƙoƙin Shata.Bugu da ƙari,
an fito da irin shirye-shiryen rediyo da ke gabatar da waƙoƙin
Shata kacokan da ma waɗanda
waƙoƙin
nasa kan fito tare da na wasu mawaƙan. Wani muhimmin abu da wannan takarda
ta fito da shi fili shi ne irin gudunmawar da rediyo ke bayarwa wajen adana da
taskace waƙoƙi.
Euba (1976:29) ya tantace rediyo a matsayin ɗaya
daga cikin hanyoyin taskace waƙoƙi.
Fitilun Kalmomi: Alhaji Mamman
Shata, Shirye-shirye, Gidajen rediyo
Gabatarwa
Tarihin
kafuwar rediyo a ƙasashen
Afirka na da tsawo ta yadda idan an ce a kawo shi a wannan gajerar takarda zai
ci fili da yawa, kuma ya zama maimai. Idan
an duba waɗannan ayyuka: Mytton (1996) da Mytton (ba shekara (b.s)
da Spitulnik (2004) da Larkin (2008) za a samu cikakken bayani. Dangane da
shigowar rediyo a Najeriya, a dubi aikin Ladele (1979). Idan kuma ana maganar
samuwar shirye-shiryen Hausa a rediyo, a dubi Garba (2013) da Garba (2014a) da
Garba (2016) domin sanin matsayin rediyo a al’ummar Hausawa da kuma Garba
(2018) domin sanin adadin gidajen rediyo da ke amfani da harshen Hausa a faɗin
duniya inda ya tabbatar da samuwar gidajen rediyo ɗari
huɗu da hamsin da biyar (455). Yanzu haka, adadin ya ƙaru. Daga lokacin da aka gudanar da wancan aiki zuwa yau,
a ƙiyasce, an samu ƙarin kimanin gidajen rediyo hamsin (50) ko ma fiye. A
Kano kaɗai, an samu ƙarin
gidajen rediyo kusan goma kamar: Aminci Rediyo, Gurantee Rediyo, Liberty
Rediyo, Muhasa Rediyo da Jalla Rediyo da Nasara Rediyo da Kanawa Rediyo da
sauransu. Rediyon TRT ya ƙara adadin
gidajen rediyon ƙasashen
waje da ke amfani da harshen Hausa.
Waƙa tsararriyar maganar hikima ce da ta ƙunshi saƙo cikin zaɓaɓɓun
kalmomin da aka auna domin maganar ta reru ba faɗuwa
kurum ba (Yahaya 1997). Ita kuma waƙa, sai da salo domin shi ne asirin waƙa (Yahaya 2001). Idan ba shi, sai ta zamo lami, miya ba
gishiri. Salo yana nufin duk wata dabara ko hanya a cikin waƙa wadda aka bi domin isar da saƙo. Ita wannan dabara ko hanya tana yi wa waƙa kwalliya ta yadda saƙon waƙar zai isa
ga mai sauraro (Yahaya 2001:3). Masana sun kasa waƙa zuwa gida biyu: ta baka da kuma rubutatta. A wannan
aiki, za a karkata ne a kan waƙar baka. Waƙar baka kamar yadda Gusau (2003:xiii) ya fada, “wani
zance ne shiryayye cikin hikima da azanci da yake zuwa gaba-gaba bisaƙa’idojin tsari da daidaitawa, a rere
cikin sautin murya da amsa-amo na kari da kida, sau da yawa kuma a tare da
amshi”.
Wannan
takarda ta mayar da hankali kacokan wajen nazarin waƙoƙin Mamman
Shata a shirye-shiryen rediyo. Gusau (2018:xv) ya ce, “Mamman Shata Katsina
mawaƙin baka ne, fasihi,masanin waƙa a jini da tsoka, mai hikima ta sarrafa kalmomi a
matsayin saƙonni cikin zubi da raujin na waƙa”. Domin Samun cikakken tarihi Mamman Shata a dubi
ayukan Abdulƙadir (1975) da Ƙanƙara (2015)
da Sheme (2018) da kuma CRNLT& F (2019)[1].
Abdulkadir (1975:266-8) ya nuna irin gudunmawar waƙoƙin Shata a
al’ummar Hausawa da irin yada gidajen rediyo da ma’aikatar yaɗa
labarai ke amfani da waƙoƙin Shata wajen wayar da kan al’umma a muhimman fannonin
rayuwa.
2.0 Rediyo da Waƙoƙin
Hausa
Dangantakar
waƙa da rediyo tamkar ta tagwayen juna ce.
Na'Allah (1994:503) ya bayyana Mawaƙan
bakan al’ummar Afirka tamkar rediyo da talabijin da jarida inda ya kira makaɗa a
matsayin ‘yanjaridar al’ummarsu. Na'Allah (1994:503) ya ruwaito Ruth Finnegan
(1970) tana da
irin wannan
ra’ayi inda ta ce, ‘mawaƙan baka, a
al’ummomin Afirka, sun kasance tamkar jaridu a
wajen waɗanda
ba su da ilimi’. Kodayake, Na'Allah (1994:503) ya yi wa Finnengan inkari inda
ya ce rawar da makaɗa ke takawa wajen faɗakarwa
da ilmantarwa da nishaɗantarwa ba su tsaya a kan waɗanda
ba su da ilimi ba, har masu ilimin na amfana da su. Domin kuwa irin waƙoƙin da
manomi ko wani mutumin karkara ko ƙaramin ɗan
kasuwa su ne dai malamin makaranta, ma’aikacin gwamnati ko jami’an tsaro ke
sauraro’. Haka kuma, Sullivan (2009:312) ta ruwaito Na’Allah (1994) na kwatanta
mawaƙan baka da kafafen sadarwa irin su:
rediyo da talabijin da jarida inda Na’Allan ke cewa, “Mawaƙan baka kan nishaɗantar
da al’umma tare da bayyana masu abin da ke faruwa a al’ummar da ma jan hankalin
al’ummar a kan abin da suke gannin bai kamata ba ko kuma wanda suke son a yi’.
Abin da wannan bayani ke son nuna mana shi ne irin kusanci da kamanci da ke
akwai tsakanin rediyo ko kafafen sadarwa da mawaƙa domin kusan manufarsu ɗaya
ce. Besmer (1970:20) da Euba (1976:29) sun tabbatar da samuwar waƙoƙin Hausa a
gidajen rediyo.
A ƙasar Hausa, matsayin waƙoƙi a rediyo
ya kai matuƙa gaya ta yadda ba yadda za a yi ba da
su ba. A hirar da na yi da wasu ma’aikatan rediyo da suka kwashe sama da
shekaru 30 suna gudanar da aiki, kuma a ɓangaren
shirye-shirye, sun tabbatar min da cewa: “Ba yadda za a yi a buɗe
rediyo, a ƙasar Hausa, ba tare da waƙoƙin Hausa
ba”. Abin da wannan bayani ke nuna mana shi ne waƙoƙin Hausa na
da muhimmin matsayi da ya kai a kamanta su da ‘ginshiƙan shirye-shiryen rediyo’ (Garba 2014b:56). Kodayake, ana
jin cewa da gangan aka bai wa waƙoƙi muhimmin gurbi a shirye-shiryen rediyo domin a shawo
kan mutanen Afirka wajen sauraren rediyo saboda
su fahimci irin farfagandar yaƙi
da ake son su ji, Turawan mulki suka sanya waƙoƙi da sauran
shirye-shirye a rediyo. Head (1979:45) ta ruwaito Wilson (1950: 46) na cewa,
daga cikin ma’aikatan rediyo na farko ‘yan Afirka da aka fara ɗauka
aikin rediyo a (Gold Cost Broadcasting),
wato Ghana ta yau, su ne malaman makaranta waɗanda
ke da zalaƙar magana da kuma mawaƙan gargajiya da ke sarrafa kayan kiɗan
gargajiya da iya yin waƙa nan take.
Waƙoƙin Hausa na
da matsayi a shirye-shirye rediyo,
Furniss da Fardon (2000:4) da Abdulƙadir (2000:131). Ba a shirye-shiryen Hausa na rediyo
kawai ba, har sauran al’ummu. A Afirka ta Kudu Hamm (1991:17) ya ruwaito wani
rahoto (AR Annual Report 1959, p4) na cewa, waƙoƙi na da babban gurbi kuma za su cigaba da riƙe wannan matsayi a shirye-shryen rediyo. Roscigno da
Danaher (2001) sun tabbatar da samuwar waƙoƙi a rediyoyin yankin na Amurika. Spitulnic (2004) ta nuna
tasirin hanyoyin bayar da labarun gargajiya na al’ummomin Afirka a rediyo.
Binciken da Garba (2012) ya gabatar ya tabbatar da maganar Spitulnic (2004) a
shirye-shiryen rediyo na Hausa. Waƙa ke da
babban kaso a shirye-shiryen rediyo fiye da duk wani nau’in adabin bakan
Hausa (Garba 2014b:58). Dangantakar waƙa da shirye-shiryen rediyo ta zamo tamkar ta jini da
tsoka (Garba 2014b:57-8).
Waƙoƙin Hausa na
daga cikin shirye-shiryen da suka fara
samun gindin zama a rediyo a al’ummar Hausawa tun kafin kafa gidan rediyo a ƙasar Hausa. Larkin (2008:48-9), ya tabbatar da cewa: “Tun
lokacin da ake watso labaran rediyo daga Landon ta hanyar amfani da
manya-manyan akwatunan rediyo da ake haɗawa da
waya, waƙoƙin
Hausa ne aka fara amfani da su a rediyo tun kafin a yanke shawarar fara amfani
da harshen Hausa a shirye-shiryen rediyo”. Waƙoƙin Hausa da
ake sanyawa a rediyo ne suka ƙara ƙwarzanta rediyo a idon Bahaushe, inji Maitama Sule, ɗaya
daga cikin ma’aikatan rediyo na farko wanda daga bisani ya zamo mashahurin ɗan
siyasa ya a cikin Lardin (2008:53). Wannan magana haka take domin Hamm (1991)
ya nuna irin yadda mahukunta suka yi amfani da waƙoƙi ta kafar
rediyo wajen assasa da shimfiɗa mulkin wariyar launin fata a Afirka ta Kudu a shekarun
1949 har zuwa shekarun 1990.
Shirye-shiryen
waƙoƙi
na rediyo, kamar yadda Garba (2014b:58) ya nuna, sun kasu kashi biyu. Kashi na ɗaya
shi ne wanda gidajen rediyon ke gabatarwa waɗanda suka ƙunshi
waƙoƙi
daban-daban. Kashi na biyu kuwa shi ne wanda
jam’iya ko ɗan takara ko zaɓaɓɓen
waƙili ko ‘yankasuwa kan saye fili domin
yaɗa waƙoƙinsu. Har wa yau, Garba (2014b:58) ya kassafa yadda
gidajen rediyo ke amfani da waƙoƙi a shirye-shiryensu a mabambantan wurare da lokuta inda
suke amfani da waƙoƙi a matsayin: ‘mabuɗin kunne’
da na cikon lokaci da maye gurbi da talla da kuma filayen waƙoƙi, irin waɗanda
ake keɓewa da yawanci akan yi wa suna da ‘rabin sa’ar mawaƙi wane’. Kodayake, akan yi wa irin wannan shiri sunaye
daban-daban kamar: Tuna baya, Mahadi mai dogon zamani, makaɗanmu
na mako da dai sauransu. Bugu da ƙari, Garba
(2014b:51) ya tabbatar da cewa, “Babu wani shirin rediyo da bai dogara ga waƙoƙi wajen
shirya shi ba. Waƙoƙi ne kawai ke taka muhimmiyar rawa a wasu shirye-shirye,
kuma tare da samun nasu shirye-shiryen masu zaman kansu a rediyo”. Wani
muhimmin lamari shi ne ba wai waƙoƙin baka kawai ake amfani da su a rediyo a Hausa ba. Waƙoƙin da ake
amfani da su a rediyo sun haɗa da na baka da rubutattu da ma na zamani da ake kira ‘waƙoƙin nanaye’
(Garba 2014b:51). Furniss (2003:2) ya nuna irin yadda ƙungiyar marubata waƙoƙin Hausa ta Hikima wato ‘Hikima Club’ wadda Mudi
Sipikin ke jagoranta ta sami fili a gidan rediyon Kano inda ake saka waƙoƙin ‘yan ƙungiyar a kowane mako. A wani aikin da Furniss (1991:21)
ya yi a kan rubutattun waƙoƙin yaƙin Basasan
Nijeriya inda ya tabbatar da samuwar ɗimbin waƙoƙin da aka
rubuta yayin gwabza yaƙin tsakanin
shekarar 1967 zuwa 1970 waɗanda aka wallafa a jaridar Gaskiya Ta Fi Kwabo ko aka
rera a taruruka ko dandali da ma gidajen rediyo.
3.0 Shata da Rediyo
Dangantakar
Shata da rediyo ta yi daidai da zancen nan na Hausawa da suke cewa, “Kafin a
haifi uwar baduku, borin turke yake da jakarsa,ko kuma iska ta tarar da kaba na
rawa. Domin kuwa, tun kafin zuwan rediyo ƙasar
Hausa Shata yake yin waƙoƙinsa. Sheme (2018:255) da Ƙanƙara
(2015:459) sun nuna cewa, “Kafin zuwan na’urorin ɗaukar
sauti da za a ɗauki mawaƙi a saurare
shi daga baya, wato garmaho ko rediyo, Shata ya yi ɗaruruwan
waƙoƙi
ko dubban waƙoƙi.
A farkon zamaninsa, (haka marubucin ya rubuta), kaf faɗin
Arewa babu gidan rediyo”. An fara ɗaukar waƙoƙin Shata a garmaho a wajajen shekarar 1950. Kamfanin ɗaukar
sauti na Badejo da ke Legos wanda ya ɗauki Shata
zuwa Legas a cikin shekarar 1951 don ya yi masa waƙa (Sheme 2018:257). Waɗannan
waƙoƙin
da aka naɗa a garmaho ne aka fara sanyawa a rediyo maras waya
(wireless) babba mai kama da akwatin talabijin, a yi ta sauraron waƙoƙinsa (Haka marubucin ya rubuta) (Sheme
2018:260).
Wasu sun ce
tun a shekarar 1944 wasu Kiristoci sun buɗe Rediyon
Muryar Bushara a unguwar Bompai a Kano a matsayin tashar rediyo ta farko a
Arewa… Sun riƙa ɗaukar
waƙoƙin
Shata su na (Haka marubucin ya rubuta) sawa; su kan (Haka marubucin ya rubuta)
bi shi ƙauyuka inda yake wasanni su na (Haka
marubucin ya rubuta) ɗaukar waƙoƙin…Rediyon Bushara da aka ambata a sama, daga bisani an
tabbatar da cewa tashar NBS ce”,
(Sheme 2018:264) da Ƙanƙara (2015:469). Sa’ilin da hukumar watsa labarai ta NBC
ta kafu a shekarar 1952 ta yi amfani da kade-kade da waƙoƙin
gargajiya da na maƙwabta da ma
na ƙetare wajen nishaɗantarwa
da wayar da kan masu saurare…Waƙoƙin Shata sun yi fice a shirye-shiryen yankin Arewa da
hukumar ta gabatar (Ladele da wasu 1979:36).
Jim kaɗan
da buɗe tashar Rediyo Talabijin Kaduna (RTK) a shekarar 1962, gidan rediyon ya aika ma’aikatansa garuruwa
domin su ɗauko waƙoƙi daga mawaƙan (Sheme
2018:271). Daga bisani mawaƙan kan zo
gidan rediyon RTK domin su yi waƙa a ɗauka.
A 1964 aka ɗauki waƙar “Ranar
Kilishi Jikar Dikko”, “Ta-Kunya Delun Kunya” da sauran su…A harabar gidan RTK a
ranar 5 ga Oktoba, 1965 Adamu Augie Argungu ya ɗauki
waƙoƙin
“Habu Na Habu”, “Alla Ba Ya Ba Ka Sai Ka Tama Shi Nema” ta Barira Musawa) da
Asauwara (waƙar Gulbin Karaɗuwa)…
(Sheme 2018:271), Ƙanƙara (2015:477). “Sanin da aka yi wa Shata ya
bambanta…amma dai yawa-yawan mutane waɗanda su ka
(Haka
marubucin ya rubuta) san Shata sun san shi a dalilin rediyo” in ji
Alhaji Halilu Ahmed Getso, fitaccen ma’aikacin rediyo ɗin
nan a cikin Sheme (2018:255). Ba shakka rediyo ne hanya mafi shahara wajen yaɗa
waƙoƙin
Shata…(Sheme 2018:255).
Wani
muhimmin abu da ya faru wanda ya ƙara kaurara
dangantakar Shata da rediyo, musamman
RNK, baya ga shaharar da Shata yake da ita, shi ne ƙaunar da ɗaya daga cikin shugabannin gidan rediyon, Alhaji Ɗahiru Modibbo, ke yi wa Shata da waƙoƙinsa (Sheme 2018). Alhaji Ɗahiru Modibbo ya taimaka gaya wajen ɗaga
Shata ta hanyar rediyo, ya fifita shi saman kowane mawaƙi… (Sheme 2018:276-277). In don ace (Haka marubucin ya rubuta) Shata ya canye duniya da yaƙin waƙa, ba wani
ne dalili ba Ɗahiru
Modibbo ne” (Ƙanƙara 2015:478).
Dangantaka
tsakanin Shata da rediyo, musamman RNK, ta zama tamkar ta ‘ba ni gishiri in ba
ka manda’, domin bayan irin gudunmawar da ake ganin RNK ya bai wa Shata, shi ma
Shatan ya bai wa gidan rediyon kamar yadda Sheme (2018:279) ya faɗa,
“Idan an waiwaya, za a ga cewa kamar yadda gidan Rediyo Najeriya na Kaduna ya
taimaka wajen yayata sunan Shata da waƙoƙin sa, (Haka
marubucin ya rubuta), haka shi ma Shata ya sa aka san gidan rediyon har
kowa ya koma ba shi da wani gidan rediyo da ya fi kamawa tamkar wannan”. Za a
iya gamsuwa da cewa, gidan Rediyo Najeriya na Kaduna ya taimaka wajen yayata
sunan Shata da waƙoƙinsa, idan aka yi la’akari da abin da wasu manazarta suka
ce. Finnegan (2012:289) tana ganin cewa, ‘Akwai yiyuwar cewa samuwar da bazuwar
rediyo a Afirka ya taimaka wajen fito da waƙoƙin siyasa
fili’. A nan, sai mu ce ba wai waƙoƙin siyasa ba kawai, akwai yiyuwar har da na Shata.
Dangantakar
Shata da rediyo ta kai har inda ake danganta Shata da rediyo ko rediyo da
Shata. Ƙololuwar dangantakar Shata da rediyo a ƙasar Hausa ita ce danganta rediyo da Shata wasu masu
sauraren rediyo ke yi. Za a fahimci
haka, idan aka yi la’akari da waɗannan layukan kirari da Garban Kora (2013), ɗaya
daga cikin manyan maroƙan Alhaji
Mamman Shata, ya yi wa Shatan:
“….Bahillacen
daji za ka ji yana cewa yaya da Shata?
In dai da
Shata kam ina sayen rediyo.
Amma ni ba
ni saye sai na ji Shata.
Buɗe
mani Shata.
Koway yi
rediyo da rikoda da garmaho saboda kai ya yi ɗan
Garba ɗan Ibrahim.
Don kai ake
sayensu…” Garban Kora (2013) a cikin Garba (2014b:55).
Babban abin
da za a lura da shi a nan kamar yadda wannan kirari ya nuna shi ne, tambayar
mai sayar da rediyo, ko rediyon na da Shata tun ma kafin a fara cinikin
rediyon. Idan ma mai sayar da rediyon ya ce akwai Shatan, to sai ya kamo an
tabbatar da Shatan, to zai saya, idan kuma babu, wataƙila ciniki ya fasu. Daga ƙarshe ma kirarin ya nuna cewa, ko wa ya mallaki rediyo da
rikoda da garmaho don ya ji waƙoƙin Shata ya saya.
4.0 Waƙoƙin Shata a Shirye-shiryen Rediyo
Irin
matsayin da waƙoƙin Hausa ke da su a shirye-shiryen rediyo na Hausa, Garba
(2014) ya bayar da rabe-raben yadda gidajen rediyo ke amfani da waƙoƙin Hausa
inda sukan yi amfani da waƙoƙi a matsayin “Mabuɗin kunne da
na cikon lokaci da maye gurbi da talla da kuma filayen waƙoƙi, irin waɗanda
ake keɓewa da yawanci akan yi wa suna da ‘rabin sa’ar mawaƙi wane’. Kodayake, akan yi wa irin wannan shiri sunaye
daban-daban kamar: Tuna baya.., makaɗanmu na
mako da dai sauransu”. Kasancewar Shata sha-kundum a fagen waƙa kamar yadda Ƙanƙara (2015) da Sheme (2018) da Nageda (Hira da shi a ranar
30/8/2023) suka nuna, waƙoƙinsa sun hau dukkan waɗannan
rabe-raben guraben da gidajen rediyo ke amfani da waƙoƙin Hausa.
Ga su kamar haka:
4.1 Mabuɗin Kunne
Waƙoƙin da kan
gabaci shiri kafin a gabatar da shi ko abin da ya ƙunsa ake kira mabuɗin kunne.
Kusan duk shirin da ake gabatarwa a rediyo na Hausa na da baiti ko ɗan
waƙa da ke yi wa shirin zagi. Irin waƙoƙin da Shata
ya yi a fannonin rayuwar Hausawa ta yau da kullum ne ya ba da wannan dama ta
amfani da waƙoƙinsa
da gidane rediyo ke yi a matsayin mabuɗin kunne.
Misali, mafi yawan shirye-shiryen noma na rediyo na amfani da waƙoƙin Shata na
‘Mai noma Habu Garba Ɗan’ammani’ da Garkuwan Bauchi Umarun Kari.
Shirye-shiryen da suka shafi tattalin arziki kan yi amfani da waƙar ‘Kuɗi a
kashe su ta hanya mai kyau’. Duk lokacin da gidan rediyon Freedom
na Kano 99.5 FM za su yi wani shiri mai magana kan harkokin lafiya sai sun sa
waƙar ‘Amadu
Gaya’. Haka kuma, rediyon Freedom Kano kan yi amfani da waƙar Shata ta ‘Yan Arewa ku bar bacci’ a shirin ‘In ka ji
wane…’
4.2 Cikon Lokaci da Maye Gurbi
Abin da ake
nufi da cikon lokaci a nan shi ne ƙarasa
lokacin da aka ware wa wani shiri. A al’adance, lokacin shirye-shiryen rediyo
kan kasance sa’a ɗaya ko kuma rabin sa’a, amma mafi yawan shirye-shirye sun
fi samun rabin sa’a. Yana da kyau a lura cewa, wannan lokaci na sa’a ko rabin
sa’a ba a kammala shi duka wato mintuna 55 a wasu lokuta ma 50 ne a matsayin
sa’a ɗaya a lokacin rediyo, a yayin da mintuna 25 ne matsayin
rabin sa’a. Saboda haka, akan yi amfani da sauran lokacin da ya yi saura wato
mintuna 5 ko 10 daga cikin sa’a ɗaya da mintuna 5 na rabin sa’a wajen sanya waƙoƙi ko
tallace-tallace ko sanarwa. A mafi yawan lokuta an fi sanya waƙoƙi (Garba
2014b:60).
A yayin da
maye gurbi, kamar yadda sunan ya nuna, na nufin maye gurbin wani shiri da wani
shirin. Alal misali, idan mai shirya wani shiri bai samu damar yin aikinsa ba
saboda wasu dalilai, akan maye shi da wani abu maimakon a bar shi haka nan ba
tare da wani abu ba. Mafi yawan lokuta, waƙoƙi ne ake
amfani da su wajen yin hakan. Abin da ya sa aka sanya cikon lokaci da maye
gurbi a matsayin wani kaso na yadda gidajen rediyo ke amfani da waƙoƙi shi ne,
cikon lokaci dai kamar wajibi ne a kodayaushe, kuma an fi yin amfani da waƙoƙi wajen
aiwatar da shi. A yayin da maye gurbi shi ma ya zamo ruwan dare saboda wasu
shirye-shirye na da wahalar shiryawa saboda bayanai da abubuwa daban-daban da
ake buƙatar samu kafin a haɗa
shi. Dalilin haka, akan yi amfani da waƙoƙin Shata daban-daban wajen cikon lokaci da maye gurbi
a-kai-a-kai.
4.3 Talla
Talla na ɗaya
daga cikin manyan hanyoyin da ke kawo wa gidajen rediyo kuɗin
shiga. Wannan ne ya sa talla ta zamo ruwan dare a gidajen rediyo. Mafi yawancin
tallace-tallacen da ake sa wa a rediyo na da waƙoƙi. Akan
shirya waƙoƙi
domin talla. Idan ana son a yi wa wani abu talla, akan sa a yi waƙa a kan wannan abun ko dai a ƙyale waƙar ita
kanta ta faɗi wannan saƙon ko kuma
bayan waƙar a gabatar da saƙon da baki (Garba 2014:61). An yi kuma ana amfani waƙoƙin Shata a
irin wannan bagire a gidajen rediyo da dama. Misali, Rediyo Najeriya na Kaduna:
Takin Sasisa da Jirgin Ɗankabo/Kabo
Air da waƙar Omo da Sabon Robb da kuma Kafinol.
4.4 Filayen Waƙoƙi
Wannan ɓangaren
zai yi magana ne a kan wasu daga cikin filayen waƙoƙi da
rediyoyi ke gabatarwa. Waɗannan su ne filayen da gidajen rediyo ke warewa domin
gabatar da waƙoƙi zalla ba tare da gauraya su da komai ba. Akan ware wa
waɗannan filaye mabambantan lokuta, wato wasu kan sami rabin
sa’a, wasu kuma sa’a ɗaya cur. Gidajen rediyo ne da kansu kan ware yawancin
filayen waƙoƙin,
a yayin da wasu kuma akan ɗauki nauyinsu ne domin tallata haja ko ɗantakarar
siyasa ko jam’iya ko ɗaiɗaikun mutane. Waƙoƙin Shata na da babban kaso a irin wannan bagire. Akan yi
wa irin waɗannan filaye sunaye daban-daban kamar: Rabin Sa’ar Alhaji
Mamman Shata da ake gabatarwa a Rediiyo Nijeriya na Kaduna a kowace ranar
Litinin da Alhamis da yamma da Mahadi mai dogon zamani da Ibrahim Nageda Bichi
ya gabatar a Rediyo Freedom da Dala FM Kano. Ga abin da Garba (2014:63) y ace
game dashirin ‘Mahadi Mai Dogon Zamani’, “Wannan shiri ne da gidan rediyon
Freedom da ke Kano ke gabatarwa wanda aka ware domin sanya waƙoƙin Alhaji
Mamman Shata. An ware sa’a ɗaya cur domin gabatar da shirin. Ana yin shirin ne a
ranakun Litinin da Talata da Laraba da Alhamis daga ƙarfe biyu na rana zuwa ƙarfe uku na ranakun da aka lissafo a sama. Shirin, wanda
Ibrahim Nageda Bichi ke gabatarwa, na gabatar da waƙoƙin Mamman
Shata zalla tare da sharhin wasu muhimman abubuwa da waƙoƙin na ƙunsa. Da yake kai-tsaye ake gabatar da shirin, masu
sauraro kan buga waya su yi tambayoyi ko sharhi da ƙarin bayani ko kuma su nemi ƙarin bayanin abin da ya shige masu duhu daga waƙoƙin. A
shekarar 2011 ce aka ƙirƙiro shirin, amma an tsayar da shi a shekarar 2013. Daga
bisani aka mayar da shirin a rediyon Dala FM, abokiyar tagwaicin rediyo
Freedom. Daga bisani nan ma an tsayar da shirin. Kodayake, ko a ranar da na
tattauna da mai gabatar da shirin, Ibrahim Nageda Bichi, a ranar 24 ga watan
Yuni, 2014, ana tattaunawa a kan yadda za a dawo da shirin”. Ya kuma gabatar da
shirin Nageda Baban Fati a Vision FM
Kano wanda kacocan shi ma ke magana a kan waƙoƙin Shata
daga 2019 zuwa 2002. Har wa yau, Ibrahim Nageda Bichi na gabatar da shirin Mahadi Mai Dogon Zamani a Primier Rediyo
Kano wanda ya fara daga 2022 zuwa yau, kuma ana cigaba da gabatar da shirin.
4.4 Zaɓen
Maigabatarwa
Wannan shirin mintuna 30 da ke bai wa mai
gabatar da shirye-shirye damar zaɓar duk waƙar da ya ga
dama ya sa a yayin da yake kan aiki. Maigabatarwar kan bayar da tarihin mawaƙin, kayan kiɗan mawaƙin da kuma
saƙon da waƙar ke ɗauke da shi. Ana gabatar da shirin a kusan dukkan gidajen
rediyoyin da ke amfani da harshen Hausa a shirye-shiryensu. Kaɗan
daga cikin su sun haɗa da: Rima Rediyo Sokoto da Rediyo Freedom Kano da Globe
FM Bauchi da Rediyo Kano (AM) da sauransu. Waƙoƙin Shata
kan fito a mafi yawan lokuta a irin wannan shirin.
4.5 Zaɓi da Kanka
Kamar yadda
sunan wannan shiri ya nuna, masu saurare ne ke buga waya su faɗi
waƙar da suke so, daga cikin waƙoƙin
tsofaffin mawaƙanmu na
gargajiya. Waƙoƙin Shata na ɗaya daga cikin su. Gidan rediyon Freedom da ke Kano ne ya
keɓe wannan shiri.
4.6 Kaɗe-Kaɗen
Gargajiya
Wannan
shiri ne da gidan rediyo Rahama da ke Kano ne ya keɓe
wa tsofaffin waƙoƙin Hausa. Shirin na da ɓangarori
biyu: ɓangaren gayyatar mawaƙan da ke raye ko kuma sanya waƙoƙin mawaƙan da suka kau da kuma masu fashin baƙin waƙoƙin. Daga cikin mawaƙan
da suka shiga ɗakin shirin, kamar yadda maigabatar da shirin, Malan
Salisu Adamu ya tabbatar, sun haɗa da: Audu Wazirin Ɗanduna,
Babangida Kakadawa, Nasiru Garba Sufa da sauransu. Cikin mawaƙan da ba su raye kuma, an yi nazarin waƙoƙin Narambaɗa
da Jankiɗi da Sa’idu Faru da Ɗanƙwairo da
Shata da Sani Sabulu da sauransu. Shirin kan gayyato Dr Ibrahim Garba Satatima
na Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero Kano don fashin baƙi tare da wasu waɗanda ake
jin cewa sun san mawaƙin da ake
magana a shirin.
4.7 Tuna Baya
Wannan
shiri ne da gidan rediyon Dala FM da ke Kano ya sadaukar domin gabatar da waƙoƙin
tsofaffin makaɗan Hausa. Waƙoƙin Shata na daga cikin waƙoƙin da ake
gabatarwa a shirin.
Rediyon
jahar Kano ne ya yi gabatar da wannan shiri a shekarun 1980. Shirin ya yi kula
da waƙoƙin
tsofaffin makaɗa irin su: Jan-kiɗI, Narambaɗa
da Aliyu Ɗandawo da Sa’idu Faru da Kurna da
Maidaji Sabon Birni da Ɗanƙwairo da Shata da Ɗanmaraya
Jos da Haruna Uje da Uwani Zakairai da Magajiya Ɗanbatta. Duk an yi hira da su a cikin shirin, kuma dukkan
hirarrakin da waƙoƙin na nan aje inji Kaigama (hira da shi :25/6/2014 ).
4.8 Inuwar Fasaha
Wannan
shiri ne da gidan rediyo Pyramid FM da ke Madobi, Kano ya ware domin gabatar da
waƙoƙin
Hausa, tsofaffi da sababbi.Ko ba a faɗa ba, waƙoƙin Shata na
daga cikin waƙoƙin da ake gabatarwa a shirin.
4.9 Ina Kwana?
Shiri ne da
ake gabatarwa tun da sassafe ake yin sa a gidan rediyon BRC da ke Bauchi. Da
zarar an gama gabatar da taƙaitattun
labarai da ƙarfe 6: 05 har zuwa ƙarfe 7:00 na safe. Akan sa kaɗe-kaɗe
da waƙoƙin
Hausa iri-iri. Kullun ake sa shirin ba Asabar ba Lahadi. Waƙoƙin Shata
suna cikin waɗanda suke ƙawata
shirin.
4.10 Makaɗanmu
na Mako
Akan zabi
mawaƙa
ciki har da Shata da a sanya a tsawon mintuna 30. Wani lokaci akan sa waƙoƙi
daban-daban na tsawon lokacin da aka ware wa shirin. Gidan rediyon gwamnatin
jihar Bauchi ne BRC ke gabatar da shirin.
4.11 Daga Taskarmu
Wannan
shiri na gidan rediyon jahar Kano na mayar da hankali ne a kan tsofaffin waƙoƙi na da.
Don kada mutane su manta da al’adunsu, mukan tsamo irin waɗannan
tsofaffin waƙoƙi
da suka haɗa da: kalangu da goge da garaya da dundufa da duman girke
dasauransu. Shirin kan gayyato makaɗa su zo har
ɗakin yaɗa labarai, wani lokaci a saka kai-tsaye wani lokaci kuma
a naɗa. Mukan tambayi tarihinsu da kayan kiɗansu
da ƙarin bayani a kan wasu fitattun waƙoƙinsu. Daga
cikin waƙoƙin
da shirin ke gabatarwa har da na Shata.
4.12 Kowane Allazi Da Nasa Amanu
Wannan
shirin na rediyon Kano wanda daga bisani ya koma ‘Allura da zare’ an yi gabatar
da shi ne a shekarar 1988. Marigayi Sharu Lawan Adamu ne ya fara gabatar da
shirin. Daga baya Abdullahi Sani Makarantar Lungu ya kama, bayan rasuwar sa
kuma Ali Ahmad Sharifai ya ci gaba da gabatar da shi. Shirin kan gayyato masana
waƙoƙin
Hausa domin su yi fashin baƙi. Daga
cikin waƙoƙin
da ake nazari har da na Shata.
4.13 Kiɗan Kalangu
Wannan
shirin gidan rediyon jihar Bauchi ne wato (Bauchi Radio Corporation) ne ke
gabatar da shi. Kamar yadda sunansa ya nuna, an sadaukar da shi ga mawaƙan da ke amfani da kalangu a waƙoƙinsu. Daga
cikin su har da Shata.
4.14 Kaɗe-Kaɗe
da Al’adu
Wannan
shiri ne da Gidan Rediyon Faransa (RFI) ke gabatarwa. Kamar yadda sunan shirin
ya nuna, kaɗe-kaɗe da al’adu, yana kula da kaɗe-kaɗe
da sauran abubuwan da suka shafi al’adun Hausawa da ma na maƙwabtansu. Shirin kan yi hira da mawaƙan Hausa da ma waɗanda ba
Hausawa ba tare da tattaunawa a kan waƙoƙinsu. Shata yana ɗaya daga
cikin waɗanda shirin kan gayyato a lokaci-lokaci.
4.15 Filin Zaɓi
Sonka
Wannan fili
ne da gidajen rediyo ke keɓewa domin miƙa saƙwannin gaisuwa da masu saurare ke yi. Akan ɗauki
nauyin shirin a wasu lokuta, a wasu lokutan kuma gidajen rediyon ne ke ɗaukar
nauyin gabatar da shi. Dangane da Rediyon Najeriya na Kaduna, ga abin da Sheme
(2018:282) ke cewa, “Ko bayan kwangilar da kamfanin PZ da ke gudanar da “Zaɓen
Robb” da “Zaɓen Drastin” su ka (Haka
marubucin ya rubuta) bayar ta ƙare,
Rediyon Najeriya na Kaduna bai watsar da Shata ba saboda irin son da masu
sauraro ke masa. Don haka sai aka ci gaba da keɓe
masa (Shata) fili na musamman a Zaɓen Rana Kashi na Farko” da Zaɓen
Rana Kashi na Biyu” a kowace rana a daidai lokacin sallar Azahar, lokacin
dayawancin Hausawa, musamman a yankin karkara, inda nan ne su ka (Haka marubucin ya rubuta) fi yawa, su na
(Haka marubucin ya rubuta) hutawa a
gida bayan komowa daga gun aiki. Waɗannan
filaye tun wajen 1973 aka fara gabatar da su... A kan (Haka marubucin ya rubuta) kuma sa waƙoƙin sa (Haka marubucin ya rubuta) a wasu
shirye-shiryen waɗanda su ka (Haka
marubucin ya rubuta) haɗa da “Zaɓen Almuru da “Zaɓen Safe”.
4.16 Kundin Makaɗan
Hausa
Ana gabatar
da wannan shiri ne a Rediyo Nijeriya na Kaduna. Shirin na yin bayani dangane da
waƙoƙin
makaɗan Hausa. Shirin ya tattauna da Malam Ibrahim Sheme,
marubucin littafin nan na Shata Ikon Allah, a kwanan nan inda ya yi fiɗar
waƙoƙin
Shata. A wani daga cikin shirin na kwanan nan, Sheme ya tattauna a kan
dangantakar Shata da jigon Arewa, Sardaunan Sakkwato, Alhaji Ahmadu Bello da
fashin baƙin ɗiyan
waƙoƙin
da Shata ya yi wa Sardauna. Akwai shirin da suka tattauna a kan Shata a
Masarautar Kano tare da Malam Ibrahim Sheme ɗin
da sauransu.
4.17 Daga Bakin Mai Ita
Wanan shiri
ne da gidan rediyon Companion FM, Katsina ke gabatarwa. Sanusi Anu Sabuwar Unguwa ne ke gabatar da
shi. Shiri ne da ke gayyatar mawaƙa domin a tattauna da su tare da nazarin waƙoƙin mawaƙan da suka ƙaura. Akan yi nazarin waƙoƙin Shata a
wannan shiri a mafi yawan lokuta. Shirin kan gayyato Dr Aliyu Ibrahim Ƙanƙara domin
yin fashin baƙin waƙoƙin Shata.
4.18 Zaɓen Rana
Shiri ne da
gidan rediyon Companion FM, Katsina ke gabatarwa. Kamar yadda sunan ya nuna,
shiri ne da ake aika gaishe-gaishen masu saurare. Dukkan waƙoƙin da ake
sanyawa a shirin waƙoƙin Shata ne zalla.
4.19 Makaɗanmu
Shiri ne da
ake gabatrwa a Rediyo Nijeriya na Kaduna wanda Muhammad Sayasaya ke gabatarwa.
Akan aika shirin agidan rediyon Companion FM, Katsina domin gabatarwa. Shirin
na gabatar da waƙoƙin Shata a-kai-a-kai.
4.20 Hanjin Jimina
Shiri ne da
gidan rediyon Vision FM, Katsina, ke gabatarwa. Ibrahim Yunusa Dutsin-Ma ne ke
gabatar da shirin. Kamar yadda sunan shirin ya nuna, shiri ne da ke magana a
kan waƙoƙin
Hausa, inda ake gabatar da waƙoƙin Shata da nazarin su.
Wasu
shirye-shiryen waƙoƙin Shata a Rediyo Nijeriya Kaduna kamar yadda Sheme
(2018:272) ya ruwaito sun haɗa da: “Kaɗe-Kaɗen Mu (Haka marubucin ya rubuta) wanda Mainasara Idris,
wanda ya zama Hakimin Funtuwa kuma Sarkin Maska, ya shugabanci gabatarwa daga
1975 zuwa 1990 inda ya yi ɗaukar makaɗin (wato Shata) duk sa’ilin da ya je Kaduna. Haka kuma
akwai shirin “Gidan Kashe Ahu’ inda Shata ke wasa”. Tuna baya shi ne roƙo shirin da ke sanya tsofaffin waƙoƙin Hausa
(Sheme 2018:290).
5.0 Kammalawa
Daga
bayanan da suka gabata, mun ga irin yadda aka samar da rediyo a nahiyar Afirka
da Najieriya da Arewacin Najeriya da yadda rediyon ya tasirantu da waƙoƙin Hausa.
Mun ga yadda aka tabbatar da kasantuwar waƙoƙin Shata
tun kafin kafuwar gidan rediyo a ƙasar Hausa
da yadda rediyon ya ƙara yaɗa
waƙoƙin
Shata. Za a iya tabbatar da haka, idan an yi la’akari da abin da Finnegan
(2012:290) ta ce, “Duk da cewa, da ma waƙoƙin yau da kullun da ma na siyasa sun samu gindin zama a
Afirka, samuwar rediyo ta ƙara
taimakawa wajen yaɗa su da fito da su fili”. Shi kuma Shata ya ƙara wa gidan rediyo Najeriya na Kaduna karɓuwa
ga masu saurare. Bugu da ƙari, an
fito da irin shirye-shiryen rediyo da ke gabatar da waƙoƙin Shata
kacokan da ma waɗanda waƙoƙin nasa kan fito tare da na wasu mawaƙan.
Wani
muhimmin abu da wannan takarda ta fito da shi fili shi ne irin gudunmawar da
rediyo ke bayarwa wajen adana da taskace waƙoƙi. Euba
(1976:29) ya tantace rediyo a matsayin ɗaya daga
cikin hanyoyin taskace waƙoƙi. Sauran kamar yadda ya lissafa su ne talabijin da
fayafayin garmaho da kuma finafinnai. Ita kuma Alou (2009:8) ta nuna rin
amfanin rediyo wajen taskace waƙoƙi inda ta ce waƙar
Mu’azu Ɗan’alalo ta Baudot wadda aka yi tun
shekarun mulkin mallaka kuma wadda gidan Rediyo da Talabijin na Zinder ya naɗa a
shekarun 1960, har yanzu tana tashe a tsakanin mutanen Nijar waɗanda
mafi yawa daga cikinsu ba a haife su ba lokacin da aka yi waƙar. Har wa yau, za mu iya cewa, kamar yadda rediyo ya
taskace waƙoƙin Ɗan’alalo, haka ya yi wa na Shata.
Samuwar
sababbin hanyoyin sadarwa (zauruka ko dandullan sada zumunta) sun bayar da
damar adana da sauraren irin waɗannan shirye-shiryen waƙoƙi na Shata
da ma na sauran mawaƙa. Akan
samu waɗannan shirye-shiryen waƙoƙi na Shata
fezbuk, da twuita da yutub da gugul+ da foskad da BBM da wazaf da sauransu.
Garba (2016:512) ya ce, “Gidajen rediyo na amfani da waɗannan
hanyoyin sadarwa da aka lissafa a sama wajen watsa shirye-shiryensu ga masu
sauraro da ma samun ra’ayoyin masu sauraro dangane da labarai da
shirye-shiryensu da suke watsawa. Mafi yawan rediyoyin da ke shirye-shirye da
Hausa na amfani da waɗannan hanyoyin sadarwa”.
Manazarta
Abdulƙadir, Ɗandatti (1975). The Role of Oral Singer in Hausa/Fulani
Society: The Case Study of Mamman Shata. Ph.D Thesis, USA. Indiana University.
Abdulkadir, M.
(2000). ‘Popular Culture in Advertising: Nigerian Hausa Radio’, in R. Fardon
and G. Furniss, eds., African
Broadcast Cultures: Radio inTransition, Westport, CT:
Praeger.
Alou, Antoinette Tidjani. (2009). ‘Performance and Power:
Cultural Strategies for Contesting Hierarchy and PoliticalAuthority in Maazou
Dan Alalo's Song 'Baudot'’, Africa Development / Afrique et Développement, Vol.
34, No. 2, Special Issue onThe Humanities / Numéro spécial sur les humanités
(2009), pp. 1-20, CODESRIA, https://www.jstor.org/stable/24484017
Accessed: 01-12-2018 21:41 UTC
Besmer, Fremont E. (1970). ‘An Hausa Song from Katsina’,
Ethnomusicology, Vol. 14, No. 3 (Sept., 1970), pp. 418-438, University of
Illinois Press on behalf of Society for Ethnomusicology, https://www.jstor.org/stable/850611
Accessed: 01-12-2018 21:29 UTC
Euba, Akin. (1976). ‘Aspects of the Preservation and
Presentation of Music in Nigeria’, The World of Music, Vol. 18, No. 4 (1976),
pp. 27-43, Schott Music GmbH & Co. KG, https://www.jstor.org/stable/43563579
Accessed: 01-12-2018 21:52 UTC
Finnegan, Ruth. (2012). ‘Topical and Political Songs’, Oral Literature in Africa. Open Book
Publishers, https://www.jstor.org/stable/j.ctt5vjsmr.20
Furniss, Graham. (1991). ‘Hausa Poetry on the Nigerian
Civil War’, African Languages and Cultures, Vol. 4, No. 1, The Literatures of
War (1991), pp.21-28, Taylor & Francis, Ltd. https://www.jstor.org/stable/1771678
Accessed: 09-09-2018 14:35 UTC
Furniss, G. da Fardon, R. 2000. ‘African Broadcast
Culture’, in R. Fardon and G. Furniss, eds., African Broadcast Cultures: Radio inTransition, Westport, CT:
Praeger.
Furniss, G. (2003) ‘Hausa Popular Literature and Video
Film: The Rapid Rise of Cultural Production in times of Economic Decline’,
in Bierschenk, T. (ed) The Working
Papers, Nr. 27, Department of Anthropology and African Studies, Johannes
Gutenberg-Universität, Forum 6, D-55099 Mainz, Germany.
http://www.uni-mainz.de/ɓifeas GeschäftsführenderHerausgeber
Garba, S. A. (2012). ‘Tasirin Zantukan Hikima da Hanyoyin
Bayar da Labaran Gargajiya a kan Labaran Hausa na Rediyo’, in Amfani, A. H. et al (eds.) Champion of Hausa Cikin Hausa: A Festschrift in Honour of Dalhatu
Muhammad. Zaria: Ahmadu Bello University Press
Garba, S. A. (2013). “Hausa in the Media” in Malumfashi,
I. A. (ed) Dundaye Journal of Hausa
Studies Vol.1; Number 5: June, 2013, Department of Nigerian Languages, Sokoto.
Usmanu Danfodiyo University.
Garba, S. A. (2014a). ‘A Survey of Radio Stations
Broadcasting in Hausa in Nigeria’, in Azare, Y.M. (ed) Harsunan Nijeriya: Journal of Nigerian Languages and Folklore, vol
XXIV
Garba, S. A. (2014b). ‘Waƙoƙin Hausa:
Ginshiƙan Shirye-shiryen Rediyo’, in Yahaya, A. B. (ed.) Zauren Waka: Journal of Hausa Poetry Studies,
vol.1 No. 2, September 2014, Sokoto Usmanu Ɗanfodiyo University.
Garba, S. A. (2016). ‘Rediyo: Limamin Hanyoyin Sadarwar
Hausawa’ in Malumfashi, I. A. M., Yakasai, S. A. and Abdullahi, I. S. S. (eds) The Hausa People, Language and History:
Past, Present and Future. Kaduna: Garkuwa Publishing Ltd
Garba, S. A. (2018). ‘Language Use in Hausa Radio: The
Case Study of Programmes of Some International Hausa Radio Stations’, PhD
thesis, Sokoto. Usmanu Danfodiyo University.
Gusau, S. M. (2003). Jagoran
Nazarin Waƙar Baka.
Kano: Benchmark Publishers Limited
Gusau, S.M. (2018). Diwanin
Waƙoƙin Baka (littafi na uku).
Kano: Century Research and Publishing Ltd.
Hamm, Charles. (1991). 'The Constant Companion of Man':
Separate Development, Radio Bantu and Music’, Popular Music, Vol. 10, No. 2
(May, 1991), pp. 147-173, Cambridge University Press, https://www.jstor.org/stable/853058,
Accessed: 16-11-2018 20:58 UTC
Head, Sydney W. (1979). British Colonial Broadcasting
Policies: The Case of the Gold Coast’, African Studies Review, Vol. 22, No. 2
(Sep., 1979), pp. 39-47, Cambridge University Press, http://www.jstor.org/stable/523811,
Accessed: 29-11-2017 01:24 UTC
Ƙanƙara, Aliyu Ibrahim (2015). Shata: Mahadi Mai Dogon Zamani. Zaria: Hope Printers and Publishers
Ladale, O. da wasu (1979). History of the Nigerian Broadcasting Corporation. Ibadan:
University of Ibadan Press
Larkin, B. (2008) Signal
and Noise: Media, Infrastructure and Urban Culture in Nigeria. Durham: Duke
University Press
Mytton, G. (1996) ’40 Years of Broadcasting from London
in African Languages’, in Allen, C. H. (ed) Africa
Bibliography 1996: Works on Africa Published During 1996. Edinburgh:
Edinburgh University Press
Mytton, Graham. (nd) A Brief History of Radio
Broadcasting in Africa, http://www.traculturalwriting.com/radiophonics/continents/usr/downloads/radiophonics/A-Brief-History.pdf
Na'Allah, Abdul Rasheed. (1994). ‘Oral Tradition, Islamic
Culture, and Topicality in the Songs of Mamman Shata Katsina and Omoekee Amao
Ilorin’, Canadian Journal of African Studies / Revue Canadienne des Études
Africaines,Vol. 28, No. 3 (1994), pp. 500-515, https://www.jstor.org/stable/485343
Accessed: 01-12-2018 21:14 UTC
Roscigno, Vincent J. and Danaher, W illiam F. (2001).
Media and Mobilization: The Case of Radio and Southern Textile Worker
Insurgency, 1929to 1934’, American Sociological Review, Vol. 66, No. 1 (Feb.,
2001), pp. 21-48, American Sociological Association, https://www.jstor.org/stable/2657392,
Accessed: 16-11-2018 21:26 UTC
Sheme, Ibrahim (2018).
Shata Ikon Allah: Rayuwar Mamman Shata Katsina. Kaduna: Informart
Publishers Ltd
Spitulnik, D. (2004). ‘Electronic Media and Oral
Tradition’ in Philip M.Peek and Kwesi Yankah (eds.) African Folklore An Encyclopedia: Routledge New York London
Sullivan, Joanna. (2009). ‘From Poetry to Prose: The
Modern Hausa Novel’, Comparative
Literature Studies, Vol. 46, No. 2, Literatures and Theories of
Africa(2009), pp. 311-337, Penn State University Press, https://www.jstor.org/stable/25659718
Accessed: 09-09-2018 14:01 UTC
Yahya, A. B. (1997). Jigon
Nazarin Waƙa.
Kaduna: Fisbas Media Service.
Yahya, A. B. (2001). Salo Asirin Waƙa. Kaduna: Fisbas Media Service.
Hira
Ibrahim Nageda Bichi, Mai gabatar da shirin ‘Mahadi Mai
Dogon Zamani’ a Rediyo Premier Kano a ranar 30/8/2023, a gidan Rediyo Freedom,
Kano
Muhammad Umar Kaigama, Mai gabatar da
shirin Taskarmu na Rediyo Kano a ranar 25/6/2014, a ofishinsa a gidan Rediyon
Kano.
[1]An gabatar da wannan ma}ala a
taron duniya a kan Alhaji (Dr.) Mamman Shata Katsina wanda Cibiyar Nazarin
Harsunan Nijeriya da Fassara da kuma Fasahar Al’umma (CRNLT&F), Jami’ar
Bayero, Kano ta shirya daga ranakun 3 zuwa 5 Satumba, 2018. Kuma ba a buga ta a
ko’ina ba.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.